< Luke 8 >

1 And it came to pass that he traveled through, by city and village in succession, announcing and preaching the good news of the kingdom of God, and the twelve men with him,
Bayan wannan sai Yesu ya zazzaga gari da ƙauye, yana wa’azin bisharar mulkin Allah. Sha Biyun nan kuwa suna tare da shi,
2 and certain women who were healed from evil spirits and infirmities: Mary who was called Magdalene, from whom seven demons had gone out,
da kuma waɗansu mata waɗanda aka warkar da su daga cututtukansu, da kuma mugayen ruhohi. Cikinsu akwai Maryamu (wadda ake kira Magdalin) wadda aljanu bakwai suka fito daga cikinta.
3 and Joanna the wife of Chuza, Herod's steward, and Susanna, and many other women who served them from the things they possessed.
Da Yowanna matar Kuza, manajan iyalin Hiridus; da Suzana; da waɗansu mata da yawa. Waɗannan mata suna taimaka musu cikin hidima, daga cikin abin da suke da shi na zaman gari.
4 And when a large multitude gathered together, and those coming to him from each city, he spoke by a parable.
Yayinda taron mai girma na taruwa, mutane kuma daga garuruwa dabam-dabam suna zuwa wurin Yesu, sai ya ba da wannan misali ya ce,
5 The man who sows went forth to sow his seed. And during his sowing, some fell by the way, and it was trampled, and the birds of the sky devoured it.
“Wani manomi ya fita domin ya shuka irinsa. Da yana watsa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, aka tattaka su, tsuntsayen sararin sama kuma suka cinye su.
6 And another fell on the rock, and having grown, it withered away because of not having moisture.
Waɗansu suka fāɗi a kan dutse, da suka tsira sai suka yanƙwane don babu ruwa a wurin.
7 And another fell amidst the thorns, and having grown together, the thorns choked it.
Waɗansu kuma suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma tare, sai ƙayan suka shaƙe su.
8 And another fell on the good ground, and having grown it produced fruit a hundredfold. As he said these things, he called out, He who has ears to hear, let him hear.
Waɗansu kuma har yanzu, suka fāɗi a ƙasa mai kyau, suka yi girma, suka ba da amfani riɓi ɗari-ɗari, fiye da abin da aka shuka.” Da faɗin haka sai ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
9 And his disciples questioned him, saying, What is this parable?
Almajiransa suka tambaye shi ma’anar wannan misali.
10 And he said, To you it is given to know the mysteries of the kingdom of God, but to the others in parables, so that seeing they would not see, and hearing they would not understand.
Sai ya ce, “Ku ne aka ba sanin asirin mulkin Allah, amma ga sauran mutane kam, ina magana da misalai, saboda, “‘ko da yake suna kallo, ba za su gani ba, ko da yake suna ji, ba za su gane ba.’
11 Now the parable is this. The seed is the word of God.
“Ga ma’anar misalin, irin, shi ne maganar Allah.
12 And those by the way are those who hear, then the devil comes, and takes away the word from their heart, lest having believed, they would be saved.
Waɗanda suka fāɗi a kan hanya su ne mutanen da suka ji, amma Iblis, yakan zo ya ɗauke maganar daga zuciyarsu, don kada su gaskata, su sami ceto.
13 And those on the rock are those who, when they hear, receive the word with joy. And these have no root, who believe for a time, and withdraw in time of trial.
Na kan dutse kuwa, su ne da jin maganar, sukan karɓa da murna, amma ba su da saiwa. Sukan gaskata na ɗan lokaci, amma lokacin gwaji, sai su ja da baya.
14 And that which fell in the thorns, these are those who heard, and as they go they are choked by cares and wealth and pleasures of life, and do not bring to maturity.
Irin da suka fāɗi a cikin ƙaya kuwa, su ne mutanen da suka ji, amma a kwana a tashi, tunanin kayan duniya, da neman arziki, da son jin daɗi, sukan hana su ba da’ya’ya.
15 But those in the good ground, these are those who in an good and right heart, having heard the word, hold it firm, and bring forth fruit in perseverance.
Amma irin da suka fāɗi a ƙasa mai kyau kuwa, su ne mutane masu kyakkyawar zuciya, mai kyau, da suka ji, suka riƙe, suka kuma jimre har suka ba da’ya’ya.”
16 And no man, having lit a lamp, covers it with a container, or places it under a bed, but places it on a lampstand, so that those who enter in may see the light.
“Ba mai ƙuna fitila sa’an nan ya ɓoye ta a cikin tulu, ko kuma ya sa ta a ƙarƙashin gado ba. A maimakon haka, yakan sa ta a kan wurin ajiye fitila, saboda mutane masu shigowa su ga haske.
17 For there is no secret that will not become visible, nor hid, that will not be known and come to be visible.
Ba abin da yake ɓoye da ba za a fallasa ba. Kuma ba abin da yake rufe, da ba za a sani ba, ko a fitar da shi a fili ba.
18 Notice therefore how ye hear. For whoever has, to him will be given, and whoever has not, even what he seems to have will be taken from him.
Saboda haka, ku yi tunani da kyau yadda kuke saurara. Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda ba shi da shi kuma, abin da yake tsammani yana da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
19 And his mother and brothers came to him, and they could not come near him because of the crowd.
Sai uwar Yesu da’yan’uwansa suka zo, domin su gan shi, amma ba su iya zuwa kusa da shi ba, saboda taron.
20 And it was reported to him, saying, Thy mother and thy brothers stand outside, desiring to see thee.
Sai wani ya faɗa masa cewa, “Ga uwarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje suna so su gan ka.”
21 But having answered, he said to them, My mother and my brothers are these who hear the word of God and do it.
Ya amsa ya ce, “Mahaifiyata da’yan’uwana, su ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma aikata ta.”
22 Now it came to pass on one of those days, that he entered into a boat, also his disciples. And he said to them, Let us pass through to the other side of the lake. And they launched forth,
Wata rana Yesu ya ce wa almajiransa, “Mu haye zuwa wancan gefen tafkin.” Sai suka shiga jirgin ruwa suka fara tafiya.
23 but as they sailed he began to asleep. And a storm of wind came down on the lake, and they were filling up, and were in peril.
Da suna cikin tafiya, sai barci ya kwashe shi. Sai wata babban iska ta taso kan tafkin, har ruwa ya fara shiga cikin jirgin. Suka shiga babban hatsari.
24 And having approached, they awoke him, saying, Master, master, we are perishing. And having risen, he rebuked the wind and the raging of the water, and they ceased, and it became calm.
Almajiran suka je suka tashe shi daga barci, suka ce, “Ubangiji, Ubangiji, za mu nutse!” Ya tashi ya kwaɓe iskar da kuma haukar ruwan. Sai ruwan da iskar suka natsu. Kome ya yi tsit.
25 And he said to them, Where is your faith? And having feared, they wondered, saying to each other, Who then is this man, that he commands even the winds and the water, and they obey him?
Sai ya tambayi almajiransa, “Ina bangaskiyarku?” A cikin tsoro da mamaki, suka ce wa junansu, “Wane ne wannan? Yana ba da umarni ga iska da ruwa ma, kuma suna biyayya da shi?”
26 And they sailed toward the country of the Gadarenes, which is opposite Galilee.
Suka shiga jirgin ruwa zuwa yankin Gerasenawa da yake a hayin tafkin, daga wajen Galili.
27 And when he came forth upon the land, a certain man met him out of the city, who had demons of a considerable time. And he wore no clothing, and did not dwell in a house, but in the sepulchers.
Da Yesu ya sauka daga jirgin, sai ga wani mutum mai aljanu daga garin. Mutumin ya daɗe bai sa tufafi ba, kuma ba ya zama a gida. Yana zama a cikin kaburbura.
28 And when he saw Jesus, having cried out, he fell down before him. And in a great voice he said, What is with me and with thee, Jesus, thou Son of the Most High God? I beseech thee, do not torment me.
Da ya ga Yesu, sai mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi, ya fāɗi a gabansa, yana ihu cewa, “Ina ruwanka da ni, Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ina roƙonka, kada ka ba ni wahala!”
29 For he commanded the unclean spirit to come out from the man, for many times it had seized him. And he was bound with chains and shackles, and guarded. And breaking the bonds apart, he was driven by the demon into the desolate regions.
Gama Yesu ya riga ya umarci mugun ruhun ya fita daga mutumin. Sau da yawa mugun ruhun ya sha kamunsa. Ko da yake akan daure shi hannu da ƙafa, da sarƙa, a kuma yi gadinsa, amma yakan tsinke sarƙoƙinsa, aljanun kuma su kore shi zuwa wuraren kaɗaici, inda ba kowa.
30 And Jesus demanded him, saying, What is thy name? And he said, Legion, because many demons were entered into him.
Yesu ya tambaye shi, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa, “Tuli,” gama aljanu masu ɗumbun yawa ne suna cikinsa.
31 And they entreated him that he would not command them to go out into the abyss. (Abyssos g12)
Suka yi ta roƙonsa kada yă umarce su su shiga ramin Abis. (Abyssos g12)
32 Now a herd of considerable swine was there feeding on the mountain, and they implored him that he would allow them to enter into those. And he allowed them.
A wurin kuwa, akwai babban garken aladu da suke kiwo a gefen tudu. Aljanun suka roƙi Yesu ya bar su, su shiga cikin aladun, ya kuwa yardar musu.
33 And the demons having come out from the man, they entered into the swine. And the herd stampeded down the slope into the lake, and were drowned.
Da aljanun suka fita daga cikin mutumin, sai suka shiga cikin aladun. Garken kuma ya gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, kuma suka nutse.
34 And when those who tended them saw what happened, they fled and reported it in the city and in the fields.
Da masu kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka ruga da gudu zuwa garin da kewaye suka kai labari.
35 And they came out to see what happened. And they came to Jesus, and found the man, from whom the demons had gone out, sitting near the feet of Jesus, clothed and in his right mind. And they were afraid.
Mutanen kuma suka fito don su ga abin da ya faru. Da suka iso wurin Yesu, sai suka tarar da mutumin da aljanun suka fita daga cikinsa, yana zaune kusa da Yesu sanye da tufafi, kuma cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
36 And also those who saw it informed them how the man who was demon-possessed was saved.
Waɗanda suka ga abin da faru, suka gaya wa mutanen yadda aka warkar da mai aljanun.
37 And the whole multitude of the region around the Gadarenes besought him to depart from them, because they were gripped by great fear. And he, having embarked into the boat, returned.
Sai dukan mutanen yankin Gerasenawa suka roƙi Yesu ya bar su, don sun tsorata sosai. Sai Yesu ya shiga jirgin ruwa ya tafi.
38 But the man from whom the demons had gone out begged him to be with him. But Jesus sent him away, saying,
Mutumin da aka fitar da aljanun daga cikinsa, ya roƙi Yesu don yă tafi tare da shi, amma Yesu ya sallame shi ya ce,
39 Return to thy house, and relate everything God did for thee. And he departed, proclaiming throughout the whole city how many things Jesus did for him.
“Koma gida, ka shaida babban alherin da Allah ya yi maka.” Sai mutumin ya tafi yana faɗin abin da Yesu ya yi masa a duk garin.
40 And it came to pass during Jesus returning, the multitude welcomed him, for they were all waiting for him.
Da Yesu ya koma, taron suka marabce shi, don dā ma duk suna jiransa.
41 And behold, there came a man whose name was Jairus, and he was a ruler of the synagogue. And having fallen down near Jesus' feet, he besought him to come into his house,
Sai wani mutum mai suna Yayirus, wani mai mulkin majami’a, ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, yana roƙonsa ya zo gidansa,
42 because there was with him an only begotten daughter, about twelve years old, and she was dying. But during his going the multitudes thronged him.
domin diyarsa ɗaya tak, wadda ta kai shekara goma sha biyu, tana bakin mutuwa. Da Yesu yake kan hanyarsa, taron mutane masu yawa suka yi ta matsa shi a kowane gefe.
43 And a woman being with an issue of blood for twelve years, who, although she spent her entire living on physicians, was unable to be healed by any,
A wurin kuwa, akwai wata mace wadda tana da ciwon zubar da jini, har na shekara goma sha biyu, amma babu wanda ya iya warkar da ita.
44 having come from behind, she touched the border of his garment. And immediately the issue of her blood stayed.
Sai ta zo ta bayansa, ta taɓa bakin rigarsa. Nan da nan, zubar da jininta ya tsaya.
45 And Jesus said, Who is he who touched me? But when they all denied, Peter and those with him, said, Master, the multitudes come together and crowd thee, and thou say, Who is he who touched me?
Yesu ya yi tambaya, “Wa ya taɓa ni?” Bayan kowa ya yi musu, sai Bitrus ya ce, “Ubangiji, ai, mutane da yawa suna matsinka ta kowane gefe.”
46 But Jesus said, Who touched me? For I perceived power having gone forth from me.
Amma Yesu ya ce, “Wani ya taɓa ni, na san cewa iko ya fita daga wurina.”
47 And when the woman saw that she was not hid, she came trembling. And having fallen down before him, she declared to him in the presence of all the people for what reason she touched him, and how she was healed immediately.
Sai macen, da ta ga ba halin ɓoyewa, sai ta fita, jikinta na rawa, ta fāɗi a gabansa. A gaban dukan mutanen, ta faɗi dalilin da ya sa ta taɓa shi, da yadda ta warke nan take.
48 And he said to her, Cheer up, Daughter. Thy faith has healed thee. Go in peace.
Sai Yesu ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya.”
49 While he still spoke, some man comes from the synagogue ruler, saying to him, Thy daughter has died. Do not trouble the teacher.
Yayinda Yesu na cikin magana har yanzu, sai ga wani daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’ar ya ce, “Kada ka ƙara damun malam, diyarka ta rasu.”
50 But having heard it, Jesus answered him, saying, Fear not, only believe and she will be saved.
Da Yesu ya ji wannan, sai ya ce wa Yayirus, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata, za a kuma warkar da ita.”
51 And when he came to the house, he did not allow any man to enter in except Peter and John and James, and the father of the girl and the mother.
Da ya iso gidan Yayirus, sai ya hana kowa yă bi shi cikin ɗakin, sai dai Bitrus, da Yohanna, da Yaƙub, da kuma mahaifin da mahaifiyar.
52 And all were weeping and bewailing her. But he said, Weep not. She did not die, but sleeps.
Ana cikin haka, dukan mutanen kuma sai kuka da makoki suke ta yi, domin yarinyar. Sai Yesu ya ce, “Ka daina yin kuka, ba tă mutu ba, tana barci ne.”
53 And they ridiculed him, knowing that she died.
Sai suka yi masa dariya, da yake sun san cewa, ta mutu.
54 But having sent them all away outside, having taken her by the hand, he called out, saying, Girl, awake.
Amma Yesu ya kama ta a hannu ya ce, “Diyata, tashi.”
55 And her spirit returned, and she rose up immediately. And he commanded to give her to eat.
Ruhunta ya dawo, kuma ta tashi, nan take. Yesu ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.
56 And her parents were amazed, but he ordered them to tell no man that which happened.
Iyayenta suka yi mamaki, amma ya ba su umarni kada su faɗa wa kowa abin da ya faru.

< Luke 8 >