< Luke 1 >

1 Inasmuch as many have taken in hand to arrange in order a narration about the deeds that have been brought to fullness among us,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 just as they delivered them to us, who became from the beginning eyewitnesses and servants of the word,
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 it occurred to me also, having followed closely from the beginning all things accurately, to write to thee in order, eminent Theophilus,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 so that thou might know the certainty of the declarations about which thou were instructed.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 It came to pass in the days of Herod, king of Judea, there was a certain priest, named Zacharias, from the division of Abijah, and his wife was from the daughters of Aaron, and her name was Elizabeth.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 And they were both righteous before God, going in all the commandments and righteous things of the Lord blameless.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 And there was no child to them because Elizabeth was barren, and they were both advanced in their days.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 But it came to pass during his service as a priest in the course of his division in the presence of God,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 that, according to the custom of the priesthood, he was chosen by lot to burn incense after entering into the temple of the Lord.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 And the whole multitude of the people were praying outside at the hour of incense.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 And an agent of the Lord became visible to him, standing on the right side of the altar of incense.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 And Zacharias having seen, was shaken, and fear fell upon him.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 But the agent said to him, Fear not, Zacharias, because thy plea was heard, and thy wife Elizabeth will bear a son for thee. And thou shall call his name John.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 And there will be joy and exultation for thee, and many will rejoice at his birth.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 For he will be great in the sight of the Lord, and he should, no, not drink wine and strong drink. And he will be filled of the Holy Spirit, even from his mother's belly.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 And he will turn back many of the sons of Israel to the Lord their God.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 And he will go ahead, in front of him, in the spirit and power of Elijah, to turn back the hearts of fathers toward children, and the disobedient in a mentality of the righteous, to make ready for the Lord a people prepared.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 And Zacharias said to the agent, How will I know this? For I am aged, and my wife is advanced in her days.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 And having answered, the agent said to him, I am Gabriel who stand in the presence of God. And I was sent to speak to thee, and to announce these good news to thee.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 And behold, thou will be mute, and not able to speak until that day these things will come to pass, because thou did not believe my words, which will be fulfilled in their time.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 And the people were waiting for Zacharias, and they wondered during his delay in the temple.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 And when he came out, he could not speak to them, and they recognized that he had seen a vision in the temple. And he was beckoning to them, and remained speechless.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 And it came to pass, when the days of his service were fulfilled, he departed to his house.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 And after these days his wife Elizabeth conceived, and she concealed herself five months, saying,
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 Thus the Lord has done to me during the days in which he looked, to take away my shame among men.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Now in the sixth month the agent Gabriel was sent by God to a city of Galilee, named Nazareth,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 to a virgin betrothed to a man whose name was Joseph, of the house of David. And the virgin's name was Mary.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 And the agent having come in near her, he said, Hail, thou who are highly favored. The Lord is with thee, thou who are blessed among women.
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 But having seen, she was perplexed at his saying, and was pondering what kind of greeting this might be.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 And the agent said to her, Fear not, Mary, for thou have found favor with God.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 And behold, thou will conceive in thy womb, and bring forth a son. And thou shall call his name JESUS.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 This man will be great, and will be called the Son of the Most High. And the Lord God will give to him the throne of his father David.
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 And he will reign over the house of Jacob into the ages. And of his kingdom there will be no end. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 And Mary said to the agent, How will this be, since I know not a man?
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 And having answered, the agent said to her, The Holy Spirit will come upon thee, and the power of the Most High will overshadow thee. Therefore also the holy thing that is begotten will be called the Son of God.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 And behold, Elizabeth thy kinswoman, she also has conceived a son in her old age, and this is the sixth month with her who was called barren.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 For no word from God will be impossible.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 And Mary said, Behold the maid-servant of the Lord. May it happen to me according to thy word. And the agent departed from her.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 And having risen in these days, Mary went with haste into the hill country, into a city of Judah,
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 and entered into the house of Zacharias and greeted Elizabeth.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 And it came to pass, when Elizabeth heard the greeting of Mary, the babe leaped in her belly. And Elizabeth was filled of the Holy Spirit,
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 and she exclaimed in a great voice, and said, Blessed are thou among women, and blessed is the fruit of thy belly.
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 And why is this to me, that the mother of my Lord would come to me?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 For lo, when the voice of thy greeting happened in my ears, the babe leaped with joy in my belly.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 And blessed is she who believed, because there will be a fulfillment of the things that were spoken to her from the Lord.
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 And Mary said, My soul magnifies the Lord,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 and my spirit rejoices in God my Savior,
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 because he has looked upon the lowliness of his bondmaid. For behold, from henceforth all generations will regard me blessed,
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 because the Mighty has done great things to me. And his name is holy.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 And his mercy is for generations of generations to those who fear him.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 He did a mighty work by his arm. He scattered the proud in the mentality of their heart.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 He brought down potentates from thrones, and raised up lowly men.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 He filled those who are hungry with good things, and those who are rich he sent away empty.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 He helped his boy Israel to be reminded of mercy,
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 just as he spoke to our fathers: to Abraham and his seed into the age. (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 And Mary dwelt with her about three months, and returned to her house.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Now the time for Elizabeth was fulfilled for her to give birth, and she brought forth a son.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 And her neighbors and her kinfolk heard that the Lord magnified his mercy toward her, and they rejoiced with her.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 And it came to pass on the eighth day, that they came to circumcise the child, and they were calling it by the name of his father Zacharias.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 And his mother having answered, said, No, but he will be called John.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 And they said to her, There is no man among thy relatives who is called by this name.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 And they made signs to his father, whatever he wanted to call him.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 And having asked for a writing tablet, he wrote, saying, His name is John. And they all marveled.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 And immediately his mouth was opened, and his tongue, and he spoke, praising God.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 And fear developed in all who dwell around them. And all these sayings were talked about in the entire hill country of Judea.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 And all who heard stored up in their heart, saying, What then will this child be? For the hand of the Lord was with him.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 And his father Zacharias was filled of the Holy Spirit, and prophesied, saying,
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 Blessed is the Lord, the God of Israel, because he came to help, and made ransom for his people.
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 And he raised up a horn of salvation for us in the house of his boy David,
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 just as he spoke by the mouth of his holy prophets from of old, (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 salvation from our enemies, and from the hand of all who hate us,
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 to do mercy with our fathers, and his holy covenant to be remembered,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 the oath that he swore to Abraham our father, to give to us,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 without fear from the hand of our enemies, having been saved to serve him
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 in piety and righteousness before him all the days of our life.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 And thou, child, will be called a prophet of the Most High. For thou will go ahead, before the face of the Lord, to prepare his ways,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 to give knowledge of salvation to his people in the remission of their sins,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 because of the bowels of mercy of our God, by which the dayspring from on high came to help us,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 to give light to those who dwell in darkness and the shadow of death, to guide our feet into a way of peace.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 And the child grew, and became strong in spirit. And he was in the desolate regions until the day of his manifestation to Israel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luke 1 >