< Genesis 37 >

1 And Jacob dwelt in the land of his father's sojourning, in the land of Canaan.
Yaƙub ya zauna a ƙasar da mahaifinsa ya zauna, wato, ƙasar Kan’ana.
2 These are the generations of Jacob. Joseph, being seventeen years old, was feeding the flock with his brothers. And he was a lad with the sons of Bilhah, and with the sons of Zilpah, his father's wives, and Joseph brought the evil report of them to their father.
Wannan shi ne labarin zuriyar Yaƙub. Yusuf, saurayi ne mai shekara goma sha bakwai. Shi da’yan’uwansa, wato,’ya’yan Bilha maza da kuma’ya’yan Zilfa maza, matan mahaifinsa suna kiwon garkuna tare. Sai Yusuf ya kawo wa mahaifinsu rahoto marar kyau game da’yan’uwansa.
3 Now Israel loved Joseph more than all his sons, because he was the son of his old age. And he made for him a coat of many colors.
Isra’ila dai ya fi ƙaunar Yusuf fiye da kowanne a cikin sauran’ya’yansa maza, gama an haifa masa shi a cikin tsufansa. Sai ya yi masa riga mai gwanin kyau.
4 And his brothers saw that their father loved him more than all his brothers. And they hated him, and could not speak peaceably to him.
Sa’ad da’yan’uwansa suka ga cewa mahaifinsu ya fi ƙaunarsa fiye da kowanne daga cikinsu, sai suka ƙi jininsa, ba sa kuma maganar alheri da shi.
5 And Joseph dreamed a dream, and he told it to his brothers, and they hated him yet the more.
Sai Yusuf ya yi mafarki, sa’ad da ya faɗa wa’yan’uwansa, suka ƙara ƙin jininsa.
6 And he said to them, Hear, I pray you, this dream which I have dreamed.
Ya ce musu, “Ku saurari wannan mafarkin da na yi.
7 For, behold, we were binding sheaves in the field, and, lo, my sheaf arose, and also stood upright. And, behold, your sheaves came round about, and made obeisance to my sheaf.
Muna daurin dammunan hatsi a gona, sai nan da nan damina ya tashi ya tsaya, yayinda dammunanku suka taru kewaye da nawa suka rusuna masa.”
8 And his brothers said to him, Shall thou indeed reign over us? Or shall thou indeed have dominion over us? And they hated him yet the more for his dreams, and for his words.
Sai’yan’uwansa suka ce masa, “Kana nufin za ka yi mulki a kanmu ke nan? Ko kuwa za ka zama sarki, a bisanmu?” Suka ƙara ƙin jininsa saboda mafarkinsa da kuma abin da ya faɗa.
9 And he dreamed yet another dream, and told it to his brothers. And said, Behold, I have dreamed a dream again. And, behold, the sun and the moon and eleven stars made obeisance to me.
Sai Yusuf ya sāke yin wani mafarki, ya faɗa wa’yan’uwansa. Ya ce, “Ku saurara, na sāke yin wani mafarki, a wannan lokaci, na ga rana da wata da taurari goma sha ɗaya suna rusuna mini.”
10 And he told it to his father, and to his brothers. And his father rebuked him, and said to him, What is this dream that thou have dreamed? Shall I and thy mother and thy brothers indeed come to bow down ourselves to thee to the earth?
Sa’ad da ya faɗa wa mahaifinsa da kuma’yan’uwansa, sai mahaifinsa ya kwaɓe shi ya ce, “Wanne irin mafarki ne haka da ka yi? Kana nufin ni da mahaifiyarka da’yan’uwanka za mu zo gabanka mu rusuna maka?”
11 And his brothers envied him, but his father kept the saying in mind.
’Yan’uwansa suka yi kishinsa, amma mahaifinsa ya riƙe batun nan a zuciya.
12 And his brothers went to feed their father's flock in Shechem.
To,’yan’uwansa suka tafi kiwon garkunan mahaifinsu kusa da Shekem.
13 And Israel said to Joseph, Are not thy brothers feeding the flock in Shechem? Come, and I will send thee to them. And he said to him, Here I am.
Sai Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Kamar yadda ka sani,’yan’uwanka suna kiwon garkuna kusa da Shekem. Zo, in aike ka gare su.” Ya ce, “To.”
14 And he said to him, Go now, see whether it is well with thy brothers, and well with the flock, and bring me word again. So he sent him out of the valley of Hebron, and he came to Shechem.
Saboda haka Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Jeka ka ga ko kome lafiya yake da’yan’uwanka da kuma garkunan, ka kawo mini labari.” Sa’an nan ya sallame shi daga Kwarin Hebron. Sa’ad da Yusuf ya kai Shekem,
15 And a certain man found him, and, behold, he was wandering in the field. And the man asked him, saying, What do thou seek?
sai wani mutum ya same shi yana yawo a cikin jeji, sai mutumin ya tambaye shi ya ce, “Me kake nema?”
16 And he said, I am seeking my brothers. Tell me, I pray thee, where they are feeding.
Yusuf ya amsa ya ce, “Ina neman’yan’uwana ne. Za ka iya faɗa mini inda suke kiwon garkunansu?”
17 And the man said, They are departed from here, for I heard them say, Let us go to Dothan. And Joseph went after his brothers, and found them in Dothan.
Mutumin ya amsa, “Sun yi gaba daga nan. Na ji su suna cewa, ‘Bari mu je Dotan.’” Saboda haka Yusuf ya bi bayan’yan’uwansa, ya kuwa same su kusa da Dotan.
18 And they saw him afar off. And before he came near to them, they conspired against him to kill him.
Amma da suka gan shi daga nesa, kafin yă kai wurinsu, sai suka ƙulla su kashe shi.
19 And they said one to another, Behold, this dreamer comes.
Suka ce wa juna, “Ga mai mafarkin nan can zuwa!
20 Come now therefore, and let us kill him, and cast him into one of the pits. And we will say, An evil beast has devoured him. And we shall see what will become of his dreams.
Ku zo mu kashe shi mu kuma jefa shi a ɗaya daga cikin rijiyoyin nan, mu ce mugun naman jeji ya cinye shi. Mu ga yadda mafarkinsa zai cika.”
21 And Reuben heard it, and delivered him out of their hand, and said, Let us not take his life.
Sa’ad da Ruben ya ji wannan, sai ya yi ƙoƙari yă cece shi daga hannuwansu. Ya ce, “Kada mu ɗauki ransa.
22 And Reuben said to them, Shed no blood. Cast him into this pit that is in the wilderness, but lay no hand upon him, that he might deliver him out of their hand, to restore him to his father.
Kada mu zub da wani jini. Mu dai jefa shi cikin wannan rijiya a nan cikin hamada, amma kada mu sa hannu a kansa.” Ruben ya faɗa wannan ne don yă cece shi daga gare su, yă kuma mai da shi ga mahaifinsa.
23 And it came to pass, when Joseph came to his brothers, that they stripped Joseph of his coat, the coat of many colors that was on him,
Saboda haka sa’ad da Yusuf ya zo wurin’yan’uwansa, sai suka tuɓe masa rigarsa, rigan nan mai gwanin kyau da ya sa,
24 and they took him, and cast him into the pit. And the pit was empty; there was no water in it.
suka kuma ɗauke shi suka jefa a cikin rijiya. To, rijiyar wofi ce, babu ruwa a ciki.
25 And they sat down to eat bread. And they lifted up their eyes and looked, and, behold, a caravan of Ishmaelites was coming from Gilead, with their camels bearing spicery and balm and myrrh, going to carry it down to Egypt.
Da suka zauna don cin abinci, sai suka tā da idanu, suka ga ayarin mutanen Ishmayel suna zuwa daga Gileyad. An yi wa raƙumansu labtu da kayan yaji da na ƙanshi, suna kan hanyarsu za su Masar.
26 And Judah said to his brothers, What profit is it if we kill our brother and conceal his blood?
Yahuda ya ce wa’yan’uwansa, “Me zai amfane mu in muka kashe ɗan’uwanmu muka ɓoye jininsa?
27 Come, and let us sell him to the Ishmaelites, and let not our hand be upon him, for he is our brother, our flesh. And his brothers hearkened to him.
Ku zo, mu sayar da shi wa mutanen Ishmayelawan nan, kada mu sa hannuwanmu a kansa; ban da haka ma, shi ɗan’uwanmu ne, jiki da jininmu.” Sai’yan’uwansa suka yarda.
28 And there passed by Midianites, merchantmen, and they drew and lifted Joseph up out of the pit, and sold Joseph to the Ishmaelites for twenty pieces of silver. And they brought Joseph into Egypt.
Saboda haka sa’ad da Fataken Midiyawa suka iso, sai’yan’uwansa suka ja Yusuf daga rijiyar, suka sayar da shi a bakin shekel ashirin na azurfa wa mutanen Ishmayel, waɗanda suka ɗauke shi zuwa Masar.
29 And Reuben returned to the pit, and, behold, Joseph was not in the pit. And he tore his clothes,
Sa’ad da Ruben ya dawo wurin rijiyar, sai ya tarar cewa Yusuf ba ya can, sai ya kyakkece tufafinsa.
30 and he returned to his brothers, and said, The child is not, and I, where shall I go?
Ya koma wurin’yan’uwansa ya ce, “Yaron ba ya can! Ina zan bi yanzu?”
31 And they took Joseph's coat, and killed a he-goat, and dipped the coat in the blood.
Sai suka ɗauki rigar Yusuf, suka yanka akuya suka tsoma rigar a cikin jinin.
32 And they sent the coat of many colors, and they brought it to their father, and said, We have found this. Know now whether it is thy son's coat or not.
Suka ɗauki rigan nan mai gwanin kyau, suka kawo wa mahaifinsu suka ce, “Mun sami wannan. Ka bincika shi ka gani ko rigar ɗanka ne.”
33 And he knew it, and said, It is my son's coat. An evil beast has devoured him; Joseph is without doubt torn in pieces.
Ya gane shi, sai ya ce, “Rigar ɗana ne! Waɗansu mugayen namun jeji sun cinye shi. Tabbatacce an yayyaga Yusuf.”
34 And Jacob tore his garments, and put sackcloth upon his loins, and mourned for his son many days.
Sa’an nan Yaƙub ya kyakkece tufafinsa, ya sa tufafin makoki, ya kuma yi makoki domin ɗansa kwanaki masu yawa.
35 And all his sons and all his daughters rose up to comfort him, but he refused to be comforted, and he said, For I will go down to Sheol to my son mourning. And his father wept for him. (Sheol h7585)
Dukan’ya’yansa maza da mata, suka zo don su ta’azantar da shi, amma ya ƙi yă ta’azantu. Ya ce, “A’a, cikin makoki zan gangara zuwa kabari wurin ɗana.” Saboda haka, mahaifin Yusuf ya yi kuka saboda shi. (Sheol h7585)
36 And the Midianites sold him into Egypt to Potiphar, an officer of Pharaoh's, the captain of the guard.
Ana cikin haka, Midiyawa suka sayar da Yusuf a Masar wa Fotifar, ɗaya daga cikin shugabannin’yan gadin fadar Fir’auna.

< Genesis 37 >