< Psalmen 44 >

1 Voor muziekbegeleiding. Van de zonen van Kore; een leerdicht. O God, wij hebben het met eigen oren gehoord, Onze vaderen hebben het ons verteld, Wat Gij gedaan hebt in hun dagen, Met eigen hand in vroeger tijd.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
2 Naties hebt Gij uitgeroeid om hèn te planten, Volkeren geveld, om hèn te doen groeien.
Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
3 Neen, niet met hun zwaard namen zij bezit van het Land, Niet hun arm bracht hun zege: Maar het was uw rechterhand en uw arm En het licht van uw aanschijn, omdat Gij ze lief hadt.
Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
4 Gij waart het, mijn Koning en God, Die Jakob de zege verleende;
Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
5 Met úw hulp sloegen wij onze vijanden neer, Door úw Naam trapten wij onze haters tegen de grond;
Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
6 Neen, ik heb niet vertrouwd op mijn boog, En mijn zwaard kon de zege niet schenken.
Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
7 Maar Gij hebt ons van onze verdrukkers verlost, En onze haters te schande gemaakt;
amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
8 In God mochten we steeds blijven roemen, En uw Naam in eeuwigheid prijzen!
A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
9 Maar nú hebt Gij ons verstoten, ons te schande gemaakt, En trekt niet meer met onze heirscharen op;
Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
10 Gij laat ons vluchten voor onze verdrukkers, En onze haters roven ons leeg!
Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
11 Gij levert ons als slachtvee uit, En verstrooit ons onder de naties;
Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
12 Verkoopt uw volk voor een spotprijs, En geeft het bijna voor niet!
Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
13 Gij maakt ons tot smaad onzer buren, Tot spot en hoon voor die ons omringen;
Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
14 Gij laat de heidenen over ons schimpen, De volkeren meewarig het hoofd over ons schudden.
Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
15 Mijn schande staat mij altijd voor ogen, En de schaamte bedekt mijn gelaat,
Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
16 Om de praatjes van schimper en spotter, Om de blik van vijand en hater.
saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
17 En dit alles trof ons, ofschoon wij U niet hebben vergeten, En uw Verbond niet hebben verbroken.
Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
18 Ons hart is niet afvallig geworden, Onze schreden dwaalden niet af van uw pad;
Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
19 Toch hebt Gij ons naar het oord der jakhalzen verwezen, En ons met de schaduw des doods overdekt.
Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
20 Of, hadden wij de Naam van onzen God soms vergeten, Onze handen naar vreemde goden geheven:
Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
21 Zou God het misschien niet hebben geweten, Hij, die de hartsgeheimen doorgrondt?
da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
22 Neen, om Uwentwil blijft men ons wurgen, En worden wij als slachtvee behandeld!
Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
23 Sta op dan; waarom zoudt Gij slapen, o Heer! Ontwaak; blijf ons niet altijd verstoten!
Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
24 Waarom zoudt Gij uw aanschijn verbergen, Onze nood en ellende vergeten?
Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
25 Want onze ziel ligt gebukt in het stof, En ons lichaam kleeft vast aan de grond.
An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
26 Sta op, ons te hulp! Red ons om wille van uw genade!
Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.

< Psalmen 44 >