< Spreuken 2 >

1 Mijn zoon, als ge mijn woorden aanvaardt, En mijn wenken ter harte neemt,
Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
2 Uw oren te luisteren legt naar de wijsheid, Uw aandacht richt op ervaring;
kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
3 Ja, als ge om wijsheid roept, En om inzicht uw stem verheft;
in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
4 Als ge er naar streeft als naar geld, En er naar zoekt als naar schatten:
in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
5 Dan zult ge de vreze voor Jahweh begrijpen, Zult ge vinden de kennis van God.
to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
6 Want Jahweh schenkt wijsheid, Van zijn lippen komen kennis en inzicht;
Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
7 Hij houdt hulp bereid voor de braven, Is een schild voor mensen van onberispelijke wandel;
Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
8 Hij beschermt de paden des rechts, En beveiligt de weg van zijn dienaars!
gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
9 Dan zult ge verstaan wat recht is en plicht, Recht vooruit gaan op elk goed pad.
Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
10 Want de wijsheid zal haar intrede doen in uw hart, De kennis zoet zijn voor uw ziel;
Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
11 Het overleg zal over u waken, Het verstand de wacht bij u houden.
Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
12 Zij zullen u behoeden voor de weg van het kwaad, Voor den man, die leugentaal spreekt;
Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
13 Voor hen, die het rechte pad hebben verlaten, En wandelen op duistere wegen;
waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
14 Voor hen, wie de misdaad een vreugde is, En die om boze plannen juichen,
waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
15 Die kronkelwegen gaan, En afdwalen op hun paden.
waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
16 Zij zullen u behoeden voor een vreemde vrouw, Voor een onbekende met haar gladde taal,
Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
17 Die den vriend van haar jeugd heeft verlaten, Het verbond van haar God heeft vergeten.
wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
18 Want haar pad helt naar de dood, Naar de schimmen leiden haar wegen.
Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
19 Wie zich met haar inlaat, keert nooit weerom, Bereikt nimmer de paden des levens!
Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
20 Zo zult ge het pad der braven bewandelen, En de weg der rechtvaardigen houden.
Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
21 Want de vromen zullen de aarde bewonen, Alleen de onberispelijken blijven er op;
Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
22 Maar de bozen worden van de aarde verdelgd, De afvalligen eruit weggevaagd!
amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.

< Spreuken 2 >