< Job 34 >

1 Elihoe vervolgde en sprak:
Sa’an nan Elihu ya ce,
2 Gij wijzen, hoort naar mijn rede; Verstandigen, luistert naar mij:
“Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
3 Want het oor toetst de woorden, Zoals het gehemelte spijzen keurt.
Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
4 We moeten zelf onderzoeken, wat recht is, Onder elkander beslissen wat goed is.
Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
5 Want Job heeft gezegd: Ik ben rechtschapen, Maar God onthoudt mij mijn recht;
“Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
6 Ondanks mijn recht moet ik lijden, Mijn wonde is ongeneeslijk, al ben ik niet schuldig!
Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
7 Is er wel iemand als Job, Die godslastering als water drinkt,
Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
8 Die het gezelschap van boosdoeners opzoekt En met slechte lieden omgang heeft?
Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
9 Want hij zegt: Wat baat het den mens, In God zijn behagen te stellen!
Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
10 Verstandige lieden, hoort dus naar mij: Onmogelijk; God doet geen kwaad, de Almachtige geen onrecht;
“Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
11 Want Hij vergeldt de mensen hun daden, Behandelt iedereen naar zijn gedrag!
Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
12 Waarachtig, God kan geen onrecht begaan, De Almachtige het recht niet verkrachten!
Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
13 Wie heeft de aarde onder zijn leiding gesteld Wie Hem met de hele wereld belast?
Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
14 Trekt Hij hun geest tot Zich terug, Neemt Hij tot Zich hun levensadem,
In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
15 Dan sterft onmiddellijk alle vlees, Keert de mens terug tot stof!
’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
16 Zijt ge verstandig, luister hiernaar, En leen het oor aan mijn rede:
“In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
17 Kan Hij, die het recht zou haten, besturen; Kan de Alrechtvaardige onrecht bedrijven?
Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
18 Hij, die tot den koning zegt: Belial Tot de edelen: Booswicht;
Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
19 Die vorsten niet voortrekt, Den arme niet achterstelt bij den rijke. Neen, ze zijn allen het werk zijner handen,
wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
20 En sterven plotseling, midden in de nacht; Rijken worden opgeschrikt, en gaan heen, Machtigen verdwijnen, al steekt men er de hand niet naar uit.
Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
21 Want zijn ogen zijn op de wegen der mensen gericht, En Hij ziet al hun schreden;
“Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
22 Er bestaat geen duister of donker, Waarin de boosdoeners zich kunnen verbergen.
Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
23 Neen, geen vaste tijd voor den mens, Om voor God ten gericht te verschijnen;
Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
24 Hij verplettert den machtige zonder verhoor, En stelt anderen voor hem in de plaats.
Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
25 Hij geeft dus acht op hun daden, Hij stort ze omver in de nacht;
Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
26 Ze worden verbrijzeld tot straf voor hun boosheid, Hij tuchtigt ze op de plaats, waar allen het zien.
Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
27 Want van Hem zijn ze afgeweken, En hebben op geen van zijn paden gelet;
domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
28 Ze hebben het kermen der armen tot Hem doen komen, Zodat Hij het klagen der ellendigen hoort.
Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
29 Hield Hij Zich stil, wie zou ze beschuldigen Bedekte Hij zijn gelaat, wie wees hen terecht? Neen, Hij houdt volk en eenling in het oog,
Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
30 Opdat geen boze regeert, het volk niet zondigt.
yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
31 Maar als de boze tot God zegt: Ik heb gedwaald, Doch ik wil niet meer zondigen;
“A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
32 Onderricht mij, totdat ik tot inzicht kom; Heb ik misdaan, ik doe het niet meer!
Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
33 Moet Hij, volgens u, het dan toch maar vergelden, Omdat gij zijn gerechtigheid anders misprijst? Gij hebt te beslissen, niet ik; Spreek dus uit, wat ge meent!
Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
34 Verstandige mensen zullen mij zeggen, Met den wijzen man, die mij hoort:
“Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
35 Job heeft niet verstandig gesproken, Zijn rede getuigt niet van inzicht.
‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
36 Waarachtig, Job zal ten einde toe worden beproefd, Om zijn antwoorden, boosdoeners waardig;
Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
37 Want hij heeft bij zijn zonde de misdaad gevoegd, Ons te honen, en tegen God een grote mond op te zetten!
Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”

< Job 34 >