< Job 22 >

1 Weer nam Elifaz van Teman het woord, en sprak:
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
2 Handelt de mens soms ten bate van God? Neen, ten eigen bate is men wijs.
“Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
3 Heeft de Almachtige er voordeel van, als ge vroom zijt, Of profijt, zo ge onberispelijk leeft?
Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
4 Bestraft Hij u soms om uw godsvrucht, Daagt Hij u daarom voor het gerecht?
“Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
5 Is het niet om uw grote boosheid, Om uw fouten, zonder eind?
Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
6 Ja, zonder noodzaak neemt ge pand van uw broeders, En trekt de berooiden de kleren uit;
Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
7 Den dorstige geeft ge geen water, Den hongerige onthoudt ge zijn brood.
Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
8 Den man met de vuist moet het land toebehoren, En de gunsteling moet het bewonen;
Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
9 Maar de weduwen zendt ge zonder iets heen, De armen der wezen slaat ge stuk!
Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
10 En daarom zijt ge van strikken omringd, Plotseling verbijsterd van schrik;
Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
11 Is uw licht verduisterd, zodat ge niet ziet, Slaat de stortvloed over u heen!
An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
12 Woont God niet hoog in de hemel? Zie eens, hoe hoog de sterren staan!
“Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
13 Maar gij besluit er uit: Wat kan God weten, Of richten door de wolken heen?
Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
14 Het zwerk is een sluier voor Hem, zodat Hij niet ziet, Hij wandelt rond op het hemelgewelf.
Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
15 Wilt ge de weg van vroeger bewandelen Die de boosdoeners hebben betreden:
Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
16 Die vóór hun tijd zijn weggesleurd, Toen de vloed hun grondvesten wegspoelde?
An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
17 Die tot God durfden zeggen: Weg van ons! Wat kan de Almachtige ons doen?
Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
18 Hij had hun huizen met voorspoed gevuld, En Zich niet met de plannen der bozen bemoeid.
Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
19 De vromen zien het met vreugde, De onschuldige drijft de spot met hen:
“Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
20 "Waarachtig, hun have vernield, Hun overvloed door het vuur verteerd!"
‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
21 Verzoen u met Hem, dan leeft ge in vrede, Dan wordt uw rijkdom weer groot;
“Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
22 Neem de onderrichting aan uit zijn mond, En bewaar zijn woord in uw hart.
Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
23 Wanneer ge vol ootmoed u tot den Almachtige bekeert, De ongerechtigheid uit uw tent verwijdert:
In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
24 Dan zult ge het goud als stof gaan schatten, Het Ofirgoud als kiezel der beken.
Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
25 Want de Almachtige zal het fijnste goud voor u zijn, En stapels van zilver;
sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
26 Dan zult ge u in den Almachtige verlustigen, En uw aanschijn verheffen tot God.
Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
27 Dan zult ge Hem roepen: Hij zal u verhoren, En ge zult Hem dankoffers brengen;
Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
28 Onderneemt ge iets, het komt tot stand, En het licht zal uw wegen bestralen!
Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
29 Want Hij vernedert de trots, Maar redt, wie de ogen neerslaat;
Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
30 Hij verlost den onschuldige: Door de reinheid uwer handen wordt ook gij dus verlost!
Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”

< Job 22 >