< Romerne 15 >

1 Men vi, som ere stærke, bør bære de svages Skrøbeligheder og ikke være os selv til Behag.
Yanzu mu da muke da karfi ya kamata mu dau nauyi raunana, kuma bai dace mu nuna son kai ba.
2 Enhver af os være sin Næste til Behag til det gode, til Opbyggelse.
Bari kowannenmu ya faranta wa makwabcinsa rai, domin wannan yana da kyau, don a gina shi.
3 Thi også Kristus var ikke sig selv til Behag; men, som der er skrevet: "Deres Forhånelser, som håne dig, ere faldne på mig."
Domin Almasihu bai faranta wa kansa rai ba. Kamar yadda aka rubuta, “zagin da wadansu suka yi masa ya sauka a kaina.”
4 Thi alt, hvad der er skrevet tilforn, det er skrevet til vor Belæring, for at vi skulle have Håbet ved Udholdenheden og Skrifternes Trøst.
Don abin da aka rubuta a baya an rubuta ne domin a gargade mu, domin ta hakuri da karfafawar litattafai mu sami karfi.
5 Men Udholdenhedensog Trøstens Gud give eder at være enige indbyrdes, som Kristus Jesus vil det,
Yanzu Allah mai hakuri da karfafawa ya baku zuciya daya ta zaman tare da juna bisa ga halin Yesu Almasihu.
6 for at I endrægtigt med een Mund kunne prise Gud og vor Herres Jesu Kristi Fader.
Domin ya yi haka ne da zuciya daya domin ku yi yabo da bakinku daya.
7 Derfor tager eder af hverandre, ligesom også Kristus har taget sig af os, til Guds Ære.
Domin ku karbi juna, kamar yadda Yesu ma ya karbe ku domin a daukaka Allah.
8 Jeg siger nemlig, at Kristus er bleven Tjener for omskårne for Guds Sanddruheds Skyld for at stadfæste Forjættelserne til Fædrene;
Saboda na ce an mai da Almasihu bawan kaciya a madadin gaskiyar Allah. Ya yi wannan ne don a tabbatar da alkawarai da aka ba kakanin kakaninmu.
9 men at Hedningerne skulle prise Gud for hans Barmhjertigheds Skyld, som der er skrevet: "Derfor vil jeg bekende dig iblandt Hedninger og lovsynge dit Navn,"
Domin Al'umai su daukaka Allah saboda jinkansa, kamar yadda ya ke a arubuce, “Domin ta haka zan yabe ka cikin Al'umai in yi wakar yabon sunanka.”
10 Og atter siges der: "Fryder eder, I Hedninger, med hans Folk!"
Kuma an ce. “Ku yi faranciki, ku Al'ummai tare da mutanensa.”
11 Og atter: "Lover Herren, alle Hedninger, og alle Folkene skulle prise ham."
Kuma.” Ku yabi Ubangiji, ku dukan Al'ummai; bari dukan mutane su yabe shi.”
12 Og atter siger Esajas: "Komme skal Isajs Rodskud og han, der rejser sig for at herske over Hedninger; på ham skulle Hedninger håbe."
Kuma, Ishaya ya ce “Za a sami tsatson Yessi, wanda zai tashi ya yi mulki a kan Al'umai, Al'umai za su sami karfin hali a cikinsa.”
13 Men Håbets Gud fylde eder med al Glæde og Fred, idet I tro, for at I må blive rige i Håbet ved den Helligånds Kraft!
Yanzu Allah mai karfafawa ya cika ku da dukkan farin ciki salama, saboda da bangaskiyarku, domin ku sami cikkakiyar karafafawa, ta wurin ikon Ruhu Mai Tsarki.
14 Men også jeg, mine Brødre! har selv den Forvisning om eder, at I også selv ere fulde af Godhed, fyldte med al Kundskab, i Stand til også at påminde hverandre.
Ni kaina na amince da ku, yan'uwa. Kuma na amince cewa ku da kanku kuna cike da alheri, cike da dukkan sani. Na amince cewa za ku sami zarafi ku gargadi juna.
15 Dog har jeg for en Del tilskrevet eder noget dristigere for at påminde eder på Grund af den Nåde, som er given mig fra Gud
Amma ina rubuta maku da gabagadi kan wadansu abubuwa, domin in tunasheku, saboda baiwar da aka bani daga wurin Allah.
16 til iblandt Hedningerne at være en Kristi Jesu Offertjener, der som Præst betjener Guds Evangelium, for at Hedningerne må blive et velbehageligt Offer, helliget ved den Helligånd.
Cewa baiwar ta sa na zama bawan Almasihu Yesu da aka aika ga Al'ummai, limami na bisharar Allah. Zan yi wannan saboda baikon Al'ummai ya zama karbabbe, kuma kebbabe ga Allah ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
17 Således har jeg min Ros i Kristus Jesus af min Tjeneste for Gud.
Don haka ina jin dadi cikin Yesu Almasihu da abubuwa na Allah.
18 Thi jeg vil ikke driste mig til at tale om noget af det, som Kristus ikke har udført ved mig til at virke Hedningers Lydighed, ved Ord og Handling,
Domin ba ni da abin da zan ce, sai abin da Yesu ya aikata ta wurina, domin Al'ummai su yi biyayya ta magana da aiki.
19 ved Tegns og Undergerningers Kraft, ved Guds Ånds Kraft, så at jeg fra Jerusalem og trindt omkring indtil Illyrien har til fulde forkyndt Kristi Evangelium;
Ta wurin alamu, da al'jibai, da ikon Ruhu Mai Tsarki. Daga Urushalima, da kewaye har zuwa Ilirikum, an kai bisharar Almasihu ko'ina dukka.
20 dog således, at jeg sætter min Ære i at forkynde Evangeliet ikke der, hvor Kristus er nævnet, for at jeg, ikke skal bygge på en andens Grundvold,
A cikin hanyar nan, burina in sanar da bishara, amma a inda ba a san Yesu ta wurin sunansa ba, don kada in sa gini akan harshashi wani.
21 men, som der er skrevet: "De, for hvem der ikke blev kundgjort om ham, skulle se, og de, som ikke have hørt, skulle forstå."
Kamar yadda yake a rubuce.”Wadanda ba a taba fada wa labarinsa ba, su gane. Wadanda ba su taba jin labarinsa ba su fahimta.”
22 Derfor er jeg også de mange Gange bleven forhindret i at komme til eder.
Saboda an hana ni zuwa wurin ku a lokatai da dama.
23 Men nu, da jeg ikke mere har Rum i disse Egne og i mange År har haft Længsel efter at komme til eder,
Amma yanzu bani da sauran wani wuri a lardin nan, kuma cikin shekaru masu yawa ina da marmarin in zo wurin ku.
24 vil jeg, når jeg rejser til Spanien, komme til eder; thi jeg håber at se eder på Gennemrejsen og af eder at blive befordret derhen, når jeg først i nogen Måde er bleven tilfredsstillet hos eder.
Duk lokacin da zan tafi Asbaniya ina begen ganin ku yayin wucewa, don ku raka ni bayan na ji dadin zama da ku na dan lokaci.
25 Men nu rejser jeg til Jerusalem i Tjeneste for de hellige.
Amma yanzu ina tafiya Urushalima don in yi wa tsarkaka hidima.
26 Thi Makedonien og Akaja have fundet Glæde i at gøre et Sammenskud til de fattige iblandt de hellige i Jerusalem.
Domin abin farinciki ne ga mutanen Makidoniya da Akaya su yi bayarwa domin gajiyayyu masu bada gaskiya wadanda suke a Urushalima.
27 De have nemlig fundet Glæde deri, og de ere deres Skyldnere. Thi ere Hedningerne blevne delagtige i hines åndelige Goder, da ere de også skyldige at tjene dem med de timelige.
Suna jin dadi domin hakika kamar bashi ne a kansu. Domin Al'ummai sun yi tarayya da su cikin ayyukan ruhaniya, ya zama hakki a kansu su ma su taimake su da abubuwa.
28 Når jeg da har fuldbragt dette og beseglet denne Frugt for dem, vil jeg derfra drage om ad eder til Spanien.
Domin lokacin da na gama basu kudin, zan zo gareku a hanyata ta zuwa Asbaniya.
29 Men jeg ved, at når jeg kommer til eder, skal jeg komme med Kristi Velsignelses Fylde.
Na san cewa lokacin da na zo gareku, zan zo da cikakkun albarku na Almasihu.
30 Men jeg formaner eder, Brødre! ved vor Herre Jesus Kristus og ved Åndens Kærlighed til med mig at stride i eders Bønner for mig til Gud,
Yanzu ina rokonku, yan'uwa, ta wurin Ubangiji Yesu Almasihu, da kaunar Ruhu Mai Tsarki, ku yi ta fama tare da ni a cikin yin addu'o, inku ga Allah saboda ni.
31 for at jeg må udfries fra de genstridige i Judæa, og mit Ærinde til Jerusalem må blive de hellige kærkomment,
Kuyi haka saboda in tsira daga wadanda suke masu biyayya ga Yahudiya, domin kuma hidimata saboda Urushalima ta zama karbabbiya.
32 for at jeg kan komme til eder med Glæde, ved Guds Villie, og vederkvæges med eder.
Ku yi addu'a cewa in zo wurinku da farinciki ta wurin nufin Allah, cewa tare da ni da ku, mu sami hutu.
33 Men Fredens Gud være med eder alle! Amen.
Allah na salama ya kasance tare da ku duka. Amin.

< Romerne 15 >