< Aabenbaringen 13 >

1 Og jeg stod på Sandet ved Havet. Og jeg så et Dyr stige op af Havet, som havde ti Horn og syv Hoveder, og på sine Horn ti Kroner, og på sine Hoveder Bespottelsens Navne.
Macijin kuwa ya tsaya a bakin teku. Sai na ga wata dabba tana fitowa daga teku. Tana da ƙahoni goma da kawuna bakwai, da kuma rawani goma a ƙahoninta, a kowane kai kuwa akwai sunan saɓo.
2 Og Dyret, som jeg så, var ligt en Panter, og dets Fødder som en Bjørns, og dets Mund som en Løves Mund; og Dragen gav det sin Kraft og sin Trone og stor Magt.
Dabbar da na gani ta yi kamar damisa, amma tana da ƙafafu kamar na beyar, bakinta kuma ya yi kamar na zaki. Macijin nan ya ba wa dabbar ƙarfinsa da gadon sarautarsa da kuma ikonsa mai girma.
3 Og jeg så et af dets Hoveder ligesom såret til Døden, og dets dødelige Sår blev lægt, og al Jorden fulgte undrende efter Dyret.
Ɗaya daga cikin kawunan dabbar ya yi kamar yana da raunin da zai iya kashe shi, amma raunin nan da zai iya kashe shi ya riga ya warke. Dukan duniya ta yi mamaki ta kuma bi dabbar.
4 Og de tilbade Dragen, fordi den havde givet Dyret Magten; og de tilbade Dyret og sagde: Hvem er Dyret lig? hvem mægter at kæmpe imod det?
Mutane suka yi wa macijin sujada domin ya ba wa dabbar ikonsa, suka yi wa dabbar sujada, suka kuma yi tambaya cewa, “Wane ne yake kama da dabban nan? Wa zai iya yaƙe ta?”
5 Og der blev givet det en Mund til at tale store Ord og Bespottelser, og der blev givet det Magt til at virke i to og fyrretyve Måneder.
Aka ba wa dabbar baki don ta faɗi kalmomin girman kai da na saɓo ta kuma yi amfani da ikonta har watanni arba’in da biyu.
6 Og det åbnede sin Mund til Bespottelser imod Gud, til at bespotte hans Navn og hans Telt, dem, som bo i Himmelen.
Ta buɗe bakinta don tă yi wa Allah saɓo, ta kuma ɓata sunansa da kuma mazauninsa da na waɗanda suke zama a sama.
7 Og der blev givet det at føre Krig imod de hellige og at overvinde dem; og der blev givet det Magt over hver Stamme og Folk og Tungemål og Folkeslag.
Aka ba ta iko tă yaƙi tsarkaka tă kuma ci nasara a kansu. Aka kuma ba ta iko bisa kowace kabila, jama’a, harshe da kuma al’umma.
8 Og alle, som bo på Jorden, skulle tilbede ham, enhver, hvis Navn ikke fra Verdens Grundlæggelse er skrevet i Lammets, det slagtedes, Livets Bog.
Dukan mazaunan duniya za su yi wa dabbar sujada, dukan waɗanda ba a rubuta sunayensu a cikin littafin ran da yake na Ɗan Ragon da aka yanka tun kafin halittar duniya ba.
9 Dersom nogen har Øre, han høre!
Duk mai kunne ji, bari yă ji.
10 Dersom nogen fører andre i Fængsel, han kommer selv i Fængsel; dersom nogen dræber med Sværd, han skal dræbes med Sværd. Her gælder det de helliges Udholdenhed og Tro.
Duk wanda aka ƙaddara ga bauta, ga bauta zai tafi. Duk wanda aka ƙaddara za a kashe da takobi, da takobin za a kashe shi. Wannan yana bukata haƙuri da aminci a gefen tsarkaka.
11 Og jeg så et andet Dyr stige op af Jorden, og det havde to Horn ligesom et Lam og talte som en Drage.
Sai na ga wata dabba tana fitowa daga ƙasa. Tana da ƙahoni biyu kamar ɗan rago, amma ta yi magana kamar maciji.
12 Og det udøver hele det første Dyrs Magt for dets Åsyn og får Jorden og dem, som bo derpå, til at tilbede det første dyr, hvis dødelige Sår blev lægt.
Ta mori dukan ikon dabban nan ta fari a madadinta, ta sa duniya da mazaunanta su yi wa dabba ta farin nan sujada, wadda aka warkar mata da raunin nan da zai iya kashe ta.
13 Og det gør store Tegn, så at det endog får Ild til. at falde ned fra Himmelen på Jorden for Menneskenes Åsyn.
Ta kuma yi manyan ayyuka da kuma alamu masu banmamaki, har ta sa wuta ta sauko daga sama zuwa ƙasa a gaban idon mutane.
14 Og det forfører dem, som bo på Jorden, for de Tegns Skyld, som det blev givet det at gøre for Dyrets Åsyn, og siger til dem, som bo på Jorden, at de skulle gøre et Billede af Dyret, ham, som har Sværdhugget og kom til Live.
Saboda alamun nan da aka ba ta iko tă yi a madadin dabban nan ta fari, sai ta ruɗi mazaunan duniya. Ta umarce su su kafa siffa don girmama dabbar da aka ji mata rauni da takobi duk da haka ta rayu.
15 Og det fik Magt til at give Dyrets Billede Ånd, så at Dyrets Billede endog kunde tale og gøre, at alle de, der ikke vilde tilbede Dyrets Billede, skulde ihjelslås.
Aka ba ta iko tă ba da numfashi ga siffar dabban nan ta fari, don tă yi magana tă kuma sa a kashe duk waɗanda suka ƙi yi wa siffar sujada.
16 Og det får alle, både små og støre, både rige og fattige, både frie og Trælle, til at sætte sig et Mærke på deres højre Hånd eller på deres Pande,
Ta kuma tilasta wa kowa, manya da yara, mawadata da matalauta,’yantattu da bayi, don a yi musu alama a hannun dama ko a goshi,
17 for at ingen skal kunne købe eller sælge uden den, som har Mærket, Dyrets Navn eller dets Navns Tal.
don kada kowa yă saya ko yă sayar, sai dai yana da alamar, wadda take sunan dabbar ko kuma lambar sunanta.
18 Her gælder det Visdom! Den, som har Forstand, udregne Dyrets Tal; thi det er et Menneskes Tal, og dets Tal er 666.
Wannan yana bukata hikima. Duk mai hankali, sai yă lissafta lambar dabbar, gama lamban nan ta mutum ne. Lambarta kuwa ita ce 666.

< Aabenbaringen 13 >