< Salme 83 >

1 (En Sang. En Salme af Asaf.) Und dig, o Gud, ikke Ro, vær ej tavs, vær ej stille, o Gud!
Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
2 Thi se, dine Fjender larmer, dine Avindsmænd løfter Hovedet,
Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
3 oplægger lumske Råd mod dit Folk, holder Råd imod dem, du værner:
Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
4 "Kom, lad os slette dem ud af Folkenes Tal, ej mer skal man ihukomme Israels Navn!"
Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
5 Ja, de rådslår i Fællig og slutter Pagt imod dig,
Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
6 Edoms Telte og Ismaeliterne, Moab sammen med Hagriterne,
tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
7 Gebal, Ammon, Amalek, Filister land med Tyrus's Borgere;
Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
8 også Assur har sluttet sig til dem, Lots Sønner blev de en Arm. (Sela)
Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
9 Gør med dem som med Midjan, som med Sisera og Jabin ved Kisjons Bæk,
Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
10 der gik til Grunde ved En-Dor og blev til Gødning på Marken!
waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
11 Deres Høvdinger gå det som Oreb og Ze'eb, alle deres Fyrster som Zeba og Zalmunna,
Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
12 fordi de siger: "Guds Vange tager vi til os som Eje."
waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
13 Min Gud, lad dem blive som hvirvlende Løv som Strå, der flyver for Vinden.
Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
14 Ligesom Ild fortærer Krat og Luen afsvider Bjerge,
kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
15 så forfølge du dem med din Storm, forfærde du dem med din Hvirvelvind;
haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
16 fyld deres Åsyn med Skam, så de søger dit Navn, o HERRE;
Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
17 lad dem blues, forfærdes for stedse, beskæmmes og gå til Grunde
Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
18 Og kende, at du, hvis Navn er HERREN, er ene den Højeste over al Jorden!
Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.

< Salme 83 >