< Salme 44 >

1 (Til sangmesteren. Af Koras sønner. En maskil.) Gud, vi har hørt det med egne ører, vore Fædre har fortalt os derom; du øved en Dåd i deres Dage, i Fortids Dage med din Hånd;
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
2 Folk drev du bort, men plantede hine, Folkeslag knuste du, men dem lod du brede sig;
Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
3 thi de fik ej Landet i Eje med Sværdet, det var ej deres Arm, der gav dem Sejr, men det var din højre, din Arm og dit Ansigts Lys, thi du havde dem kær.
Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
4 Du, du er min Konge, min Gud, som sender Jakob Sejr.
Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
5 Ved dig nedstøder vi Fjenden, Modstanderne træder vi ned i dit Navn;
Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
6 thi ej på min Bue stoler jeg, mit Sværd kan ikke give mig Sejr;
Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
7 men du gav os Sejr over Fjenden, du lod vore Avindsmænd blive til Skamme.
amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
8 Vi roser os altid af Gud, dit Navn vil vi love for evigt. (Sela)
A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
9 Dog har du forstødt os, gjort os til Spot, du drager ej med vore Hære;
Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
10 du lader os vige for Fjenden, vore Avindsmænd tager sig Bytte;
Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
11 du har givet os hen som Slagtekvæg, og strøet os ud mellem Folkene,
Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
12 dit Folk har du solgt til Spotpris, vandt ikke Rigdom ved Salget.
Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
13 Til Hån for Naboer gør du os, til Spot og Spe for Grander,
Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
14 du gør os til Mundheld blandt Folkene, lader Folkeslagene ryste på Hovedet ad os.
Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
15 Min Skændsel er mig altid i Tanke, og Skam bedækker mit Åsyn
Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
16 for spottende, hånende Tale, for Fjendens og den hævngerriges Blikke.
saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
17 Alt det kom over os, skønt vi glemte dig ikke, sveg ikke heller din Pagt!
Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
18 Vort Hjerte veg ikke fra dig, vore Skridt forlod ej din Vej.
Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
19 Dog knuste du os, hvor Sjakalerne bor, og indhylled os i Mørke.
Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
20 Havde vi glemt vor Guds Navn, bredt Hænderne ud mod en fremmed Gud,
Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
21 vilde Gud ej opspore det? Han kender jo Hjerternes Løn dom
da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
22 nej, for din Skyld dræbes vi Dagen lang og regnes som Slagtekvæg!
Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
23 Vågn op, hvi sover du, Herre? Bliv vågen, forstød ej for stedse!
Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
24 Hvorfor vil du skjule dit Åsyn, glemme vor Nød og Trængsel?
Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
25 Thi vor Sjæl ligger bøjet i Støvet, vort Legeme klæber ved Jorden.
An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
26 Stå op og kom os til Hjælp, forløs os for din Miskundheds Skyld!
Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.

< Salme 44 >