< Salme 1 >

1 Salig den Mand, som ikke går efter gudløses Råd, står på Synderes Vej eller sidder i Spotteres Lag,
Mai farin ciki ne mutumin da ba ya aiki da shawarar mugaye ko yă yi abin da masu zunubi suke yi ko yă zauna tare da masu yin ba’a.
2 men har Lyst til HERRENs Lov, og som grunder på hans Lov både Dag og Nat.
Amma yana jin daɗin bin dokar Ubangiji, kuma yana ta nazarinta dare da rana.
3 Han er som et Træ, der, plantet ved Bække, bærer sin Frugt til rette Tid, og Bladene visner ikke: Alt, hvad han gør, får han Lykke til.
Yana kama da itacen da aka shuka kusa da maɓulɓulan ruwa, wanda yake ba da amfani a daidai lokaci wanda kuma ganyensa ba sa bushewa. Duk abin da yake yi, yakan yi nasara.
4 De gudløse derimod er som Avner, Vinden bortvejrer.
Ba haka yake da mugaye ba! Su kamar yayi ne da iska take kwashewa.
5 Derfor består de gudløse ikke i Dommen og Syndere ej i retfærdiges Menighed.
Saboda haka mugaye ba za su iya tsayawa a shari’a ba, balle a sami masu zunubi a taron adalai.
6 Thi HERREN kender retfærdiges Vej, men gudløses Vej brydes af.
Gama Ubangiji yana lura da yadda adalai suke yin abubuwa, amma ayyukan mugaye za su kai su ga hallaka.

< Salme 1 >