< 4 Mosebog 10 >

1 HERREN talede fremdeles til Moses og sagde:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Du skal lave dig to Sølvtrompeter; i drevet Arbejde skal du lave dem. Dem skal du bruge, når Menigheden skal kaldes sammen, og når Lejrene skal bryde op.
“Ka ƙera kakaki guda biyu na azurfa, ka kuma yi amfani da su don kira taron jama’a wuri ɗaya, don kuma ka riƙa sanar da su lokacin tashi daga sansani.
3 Når der blæses i dem begge to, skal hele Menigheden samle sig hos dig ved Indgangen til Åbenbaringsteltet.
Sa’ad da aka busa su biyu, dukan jama’a za su taru a gabanka a ƙofar Tentin Sujada.
4 Blæses der kun i den ene, skal Øversterne, Overhovederne for Israels Stammer, samle sig hos dig.
In ɗaya ne kaɗai aka busa, sai shugabannin kabilan Isra’ila, su taru a gabanka.
5 Når I blæser Alarm med dem, skal Lejrene på Østsiden bryde op;
Sa’ad da aka ji karar busar kakaki, sai sansanin da yake a gabashi, su kama hanya.
6 blæser Alarm anden Gang, skal Lejrene på Sydsiden bryde op: tredje Gang skal Lejrene mod Vest bryde op, fjerde Gang Lejrene mod Nord; der skal blæses Alarm, når de skal bryde op.
A kara ta biyu, sansanin da yake a kudanci, su kama hanya. Busan kakaki zai zama alama ta kama hanya.
7 Men når Forsamlingen skal sammenkaldes skal I blæse på almindelig Vis, ikke Alarm.
In don a tara jama’a ne, sai a busa kakaki, amma ba da irin alama ɗaya ba.
8 Arons Sønner, Præsterne, skal blæse i Trompeterne; det skal være eder en evig gyldig Anordning fra Slægt til Slægt.
“’Ya’yan Haruna, firistoci ne, za su busa kakaki. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla gare ku da kuma tsararraki masu zuwa.
9 Når I drager i Krig i eders Land mod en Fjende, der angriber eder, og blæser Alarm med Trompeterne, skal I ihukommes for HERREN eders Guds Åsyn og frelses fra eders Fjender.
Duk lokacin da za ku tafi yaƙi a ƙasarku, in akwai waɗansu da suke matsa muku, za ku yi amfani da waɗannan kakaki ta wurin hura su, alama ce, cewa za a je yaƙi. Sa’an nan Ubangiji Allahnku zai tuna da ku, yă cece ku daga maƙiyanku.
10 Og på eders Glædesdage, eders Højtider og Nymånedage, skal I blæse i Trompeterne ved eders Brændofre og Takofre; så skal de tjene eder til Ihukommelse for eders Guds Åsyn. Jeg er HERREN eders Gud!
Haka ma in kuna cikin jin daɗinku, musamman lokacin da kuke bukukkuwanku, kamar Bikin Sabon Wata da dai kowane Bikinku, za ku hura waɗannan kakaki lokacin da kuke miƙa hadayunku na ƙonawa, da hadayunku na salama, za su kuma zama muku abin tunawa a gaban Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
11 Den tyvende Dag i den anden Måned af det andet År løftede Skyen sig fra Vidnesbyrdets Bolig.
A rana ta ashirin ga wata na biyu, a shekara ta biyu, sai girgijen ya tashi daga tabanakul na Shaida.
12 Da brød Israeliterne op fra Sinaj Ørken, i den Orden de skulde bryde op i, og Skyen stod stille i Parans Ørken.
Sai Isra’ilawa suka tashi daki-daki daga Hamadar Sinai, suna tafiya daga wuri zuwa wuri, har sai da girgijen ya tsaya a Hamadar Faran.
13 Da de nu første Gang brød op efter Guds Bud ved Moses,
Suka kama hanya, a wannan lokaci, bisa umarnin Ubangiji, ta wurin Musa.
14 var Judæernes Lejr den første, der brød op under sit Felttegn, Hærafdeling for Hærafdeling; deres Hær førtes af Nahasjon, Amminadabs Søn.
Ɓangarorin sansanin Yahuda suka fara tashi, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Nashon ɗan Amminadab ne shugaba.
15 Issakariternes Stammes Hær førtes af Netanel, Zuars Søn,
Netanel ɗan Zuwar ne shugaban ɓangaren kabilar Issakar,
16 og Zebuloniternes Stammes Hær af Eliab, Helons Søn.
Eliyab ɗan Helon kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Zebulun.
17 Da derpå Boligen var taget ned, brød Gersoniterne og Merariterne op og bar Boligen.
Sa’an nan aka saukar da tabanakul ƙasa, Gershonawa da mutanen Merari da suke ɗauke da shi suka kama hanya.
18 Så brød Rubens Lejr op under sit Felttegn, Hærafdeling for Hærafdeling; deres Hær førtes af Elizur, Sjedeurs Søn.
Sai ɓangarori sansanin Ruben suka biyo, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Elizur ɗan Shedeyur ne shugaba.
19 Simeoniternes Stammes Hær førtes af Sjelumiel, Zurisjaddajs Søn,
Shelumiyel ɗan Zurishaddai ne shugaban ɓangaren kabilar Simeyon,
20 og Gaditernes Stammes Hær af Eljasaf, Deuels Søn.
Eliyasaf ɗan Deyuwel kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Gad.
21 Så brød Kehatiterne, der bar de hellige Ting, op; og før deres Komme havde man rejst Boligen.
Sai Kohatawa suka kama hanya, ɗauke da kayayyaki masu tsarki, domin kafin su kai wurin da za a kafa sansani, a riga an kafa tabanakul.
22 Så brød Efraimiternes Lejr op under sit Felttegn, Hærafdeling for Hærafdeling; deres Hær førtes af Elisjema, Ammihuds Søn.
Biye da waɗannan kuma sai ɓangaren sansanin kabilar Efraim suka biyo bisa ga ƙa’ida da aka yi, aka kuma umarta. Elishama ɗan Ammihud ne shugaba.
23 Manassiternes Stammes Hær førtes af Gamliel, Pedazurs Søn,
Gamaliyel ɗan Fedazur ne shugaban ɓangaren kabilar Manasse,
24 og Benjaminiternes Stammes Hær af Abidan, Gidonis Søn.
Abidan ɗan Gideyoni kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Benyamin.
25 Så brød Daniternes Lejr op under sit Felttegn som Bagtrop i hele Lejrtoget, Hærafdeling for Hærafdeling; deres Hær førtes af Ahiezer, Ammisjaddajs Søn.
A ƙarshe, a matsayi masu gadin bayan dukan ɓangarori, sai ɓangaren sansanin Dan suka tashi bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Ahiyezer ɗan Ammishaddai ne shugaba.
26 Aseriternes Stammes Hær førtes af Pagiel, Okrans Søn,
Fagiyel ɗan Okran ne shugaban ɓangaren kabilan Asher,
27 og Naftalitemes Stammes Hær af Ahira, Enans Søn.
Ahira ɗan Enan kuma shi ne shugaban kabilar Naftali.
28 Således foregik Israelitternes Opbrud, Hærafdeling for Hærafdeling. Så brød de da op.
Wannan shi ne tsarin tafiyar ɓangarorin Isra’ilawa, sa’ad da sukan kama hanya.
29 Men Moses sagde til Midjaniten Hobab, Reuels Søn, Moses's Svigerfader: "Vi bryder nu op for at drage til det Sted, HERREN har lovet at give os; drag med os! Vi skal lønne dig godt, thi HERREN har stillet Israel gode Ting i Udsigt."
Sai Musa ya ce wa Hobab ɗan Reyuwel Bamidiyane surukinsa, “Yanzu fa, muna shirin tashi ne daga nan, domin mu tafi inda Ubangiji ya ce, ‘Zan ba ku.’ Ka zo tare da mu, za mu kuwa yi maka alheri, gama Ubangiji ya yi wa Isra’ilawa alkawari abubuwa masu kyau.”
30 Men han svarede ham: "Jeg vil ikke drage med; nej, jeg drager til mit Land og min Slægt."
Ya amsa, ya ce “A’a, ba zan tafi ba; zan koma ƙasata da kuma wurin mutanena.”
31 Da sagde han: "Forlad os ikke! Du kender jo de Steder, hvor vi kan slå Lejr i Ørkenen; vær Øje for os!
Amma Musa ya ce, “Ina roƙonka kada ka rabu da mu. Ka san inda ya kamata mu kafa sansani a hamada, za ka kuma zama idanunmu.
32 Drager du med os, skal vi give dig Del i alt det gode, HERREN vil give os."
In ka zo tare da mu, za mu raba duk abin alherin Ubangiji ya ba mu tare da kai.”
33 Derpå brød de op fra HERRENs Bjerg og vandrede tre Dagsrejser frem, idet HERRENs Pagts Ark drog i Forvejen for at søge dem et Sted, hvor de kunde holde Hvil.
Saboda haka suka kama hanya daga dutsen Ubangiji, suka yi tafiya kwana uku. Akwatin alkawarin Ubangiji ya ja gabansu a waɗannan kwanaki uku, don yă samo musu masauƙi.
34 Og HERRENs Sky svævede over dem om Dagen, når de brød op fra Lejren.
A duk lokacin da suka tashi daga sansani, girgijen Ubangiji ya inuwantar da su da rana.
35 Og hver Gang Arken brød op, sagde Moses: "Stå op, HERRE, at dine Fjender må splittes og dine Avindsmænd fly for dit Åsyn!"
Duk kuma sa’ad da akwatin ya kama hanya, sai Musa ya ce, “Ka tashi, ya Ubangiji! Ka sa maƙiyanka su warwatse; masu ƙinka kuma su gudu a gabanka.”
36 Og hver Gang den standsede, sagde han: "Vend tilbage, HERRE, til Israels Stammers Titusinder!"
Duk sa’ad da akwatin ya sauka kuma, sai Musa ya ce, “Ka komo, ya Ubangiji, a wurin dubban da ba a iya ƙidayawa na iyalan Isra’ila.”

< 4 Mosebog 10 >