< Matthæus 7 >

1 Dømmer ikke, for at I ikke skulle dømmes; thi med hvad Dom I dømme, skulle I dømmes,
“Kada ku ba wa kowa laifi, don kada a ba ku laifi ku ma.
2 og med hvad Mål I måle, skal der tilmåles eder.
Gama da irin shari’ar da kuka yi wa waɗansu, da ita za a shari’anta ku. Mudun da kuka yi awo da shi, da shi za a yi muku.
3 Men hvorfor ser du Skæven, som er i din Broders Øje, men Bjælken i dit eget Øje bliver du ikke var?
“Don me kake duban ɗan tsinken da yake idon ɗan’uwanka, alhali kuwa ga gungume a naka ido?
4 Eller hvorledes kan du sige til din Broder: Lad mig drage Skæven ud af dit Øje; og se, Bjælken er i dit eget Øje.
Yaya za ka ce wa ɗan’uwanka, ‘Bari in cire maka ɗan tsinken nan daga idonka,’ alhali kuwa a kowane lokaci akwai gungume a naka ido?
5 Du Hykler! drag først Bjælken ud af dit Øje, og da kan du se klart til at tage Skæven ud af din Broders Øje.
Kai munafuki, fara cire gungumen da yake idonka, a sa’an nan ne za ka iya gani sosai yadda za ka cire ɗan tsinken da yake a idon ɗan’uwanka.
6 Giver ikke Hunde det hellige, kaster ikke heller eders Perler for Svin, for at de ikke skulle nedtræde dem med deres Fødder og vende sig og sønderrive eder.
“Kada ku ba karnuka abin da yake mai tsarki; kada kuma ku jefa wa aladu lu’ulu’anku. In kuka yi haka za su tattake su, sa’an nan su juyo su jijji muku ciwo.
7 Beder, så skal eder gives; søger, så skulle I finde; banker på, så skal der lukkes op for eder.
“Ku roƙa za a ba ku; ku nema za ku samu; ku ƙwanƙwasa za a kuwa buɗe muku ƙofa.
8 Thi hver den, som beder, han får, og den, som søger, han finder, og den, som banker på, for ham skal der lukkes op.
Gama duk wanda ya roƙa, akan ba shi; wanda ya nema kuwa, yakan samu, wanda kuma ya ƙwanƙwasa, za a buɗe masa ƙofa.
9 Eller hvilket Menneske er der iblandt eder, som, når hans Søn beder ham om Brød, vil give ham en Sten?
“Wane ne a cikinku in ɗansa ya roƙe shi burodi, sai yă ba shi dutse?
10 Eller når han beder ham om en Fisk, mon han da vil give ham en Slange?
Ko kuwa in ya roƙe shi kifi, sai yă ba shi maciji?
11 Dersom da I, som ere onde, vide at give eders Børn gode Gaver, hvor meget mere skal eders Fader, som er i Himlene, give dem gode Gaver, som bede ham!
In ku da kuke mugaye kun san yadda za ku ba da kyautai masu kyau ga’ya’yanku, balle Ubanku na sama, ba zai fi ku iya ba da abubuwa masu kyau, ga su waɗanda suka roƙe shi ba!
12 Altså, alt hvad I ville, at Menneskene skulle gøre imod eder, det skulle også I gøre imod dem; thi dette er Loven og Profeterne.
Saboda haka, duk abin da kuke so mutane su yi muku, ku ma sai ku yi musu, domin wannan shi ne Doka da koyarwar Annabawa sun ƙunsa.
13 Går ind ad den snævre Port; thi den Port er vid, og den Vej er bred, som fører til Fortabelsen, og de ere mange, som gå ind ad den;
“Ku shiga ta matsattsiyar ƙofa. Gama ƙofar zuwa hallaka faɗaɗɗiya ce mai sauƙin bi kuma, masu shiga ta cikinta kuwa suna da yawa.
14 thi den Port er snæver, og den Vej er trang, som fører til Livet og de er få, som finde den
Amma ƙofar zuwa rai, ƙarama ce matsattsiya kuma, masu samunta kuwa kaɗan ne.
15 Men vogter eder for de falske Profeter, som komme til eder i Fåreklæder, men indvortes ere glubende Ulve.
“Ku yi hankali da annabawan ƙarya. Sukan zo muku da kamannin tumaki, amma daga ciki mugayen kyarketai ne.
16 Af deres Frugter skulle I kende dem. Sanker man vel Vindruer af Torne eller Figener af Tidsler?
Ta wurin aikinsu za ku gane su. Mutane suna iya tsinkan inabi a jikin ƙaya, ko kuwa ɓaure a jikin sarƙaƙƙiya?
17 Således bærer hvert godt Træ gode Frugter, men det rådne Træ bærer slette Frugter.
Haka ma kowane itace mai kyau yakan ba da’ya’ya masu kyau, kuma mummunan itace ba ya ba da’ya’ya masu kyau.
18 Et godt Træ kan ikke bære slette Frugter, og et råddent Træ kan ikke bære gode Frugter.
Itace mai kyau ba ya ba da munanan’ya’ya, haka kuma mummunan itace ba ya ba da’ya’ya masu kyau.
19 Hvert Træ, som ikke bærer god Frugt, omhugges og kastes i Ilden.
Duk itacen da ba ya ba da’ya’ya masu kyau sai a sare shi a jefa cikin wuta.
20 Altså skulle I kende dem af deres Frugter.
Ta haka, ta wurin aikinsu za ku gane su.”
21 Ikke enhver, som siger til mig: Herre, Herre! skal komme ind i Himmeriges Rige, men den, der gør min Faders Villie, som er i Himlene.
“Ba duk mai ce mini, ‘Ubangiji, Ubangiji,’ ne zai shiga mulkin sama ba, sai dai wanda yake aikata nufin Ubana da yake sama.
22 Mange skulle sige til mig på hin Dag: Herre, Herre! have vi ikke profeteret ved dit Navn, og have vi ikke uddrevet onde Ånder ved dit Navn, og have vi ikke gjort mange kraftige Gerninger ved dit Navn?
Da yawa za su ce mini a wannan rana, ‘Ubangiji, Ubangiji, ashe, ba mu yi annabci a cikin sunanka ba, ba kuma a cikin sunanka ne muka fitar da aljanu, muka yi abubuwan banmamaki da yawa ba?’
23 Og da vil jeg bekende for dem Jeg kendte eder aldrig; viger bort fra mig, I, som øve Uret!
Sa’an nan zan ce musu a fili, ‘Ban taɓa saninku ba. Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta!’
24 Derfor, hver den, som hører disse mine Ord og gør efter dem, ham vil jeg ligne ved en forstandig Mand, som byggede sit Hus på Klippen,
“Saboda haka duk wanda yake jin kalmomin nan nawa yake kuma aikata su, yana kama da mutum mai hikima wanda ya gina gidansa a kan dutse.
25 og Skylregnen faldt, og Floderne kom, og Vindene blæste og sloge imod dette Hus, og det faldt ikke; thi det var grundfæstet på Klippen.
Ruwan sama ya sauko, rafuffuka suka cika, iska kuma ta hura ta bugi gidan; duk da haka bai fāɗi ba, gama yana da harsashinsa a kan dutse.
26 Og hver den, som hører disse mine Ord og ikke gør efter dem, skal lignes ved en Dåre, som byggede sit Hus på Sandet,
Amma duk wanda yake jin kalmomin nan nawa bai kuwa aikata su ba, yana kama da wani wawa wanda ya gina gidansa a kan yashi.
27 og Skylregnen faldt, og Floderne kom, og Vindene blæste og stødte imod dette Hus, og det faldt, og dets Fald var stort."
Ruwan sama ya sauko, rafuffuka suka cika, iska kuwa ta hura ta bugi gidan, sai ya fāɗi da mummunar ragargajewa kuwa.”
28 Og det skete, da Jesus havde fuldendt disse Ord, vare Skarerne slagne af Forundring over hans Lære;
Sa’ad da Yesu ya gama faɗin waɗannan abubuwa, sai taron mutanen suka yi mamakin koyarwarsa,
29 thi han lærte dem som en, der havde Myndighed, og ikke som deres skriftkloge.
domin ya koyar kamar wani wanda yake da iko, ba kamar malamansu na dokoki ba.

< Matthæus 7 >