< Matthæus 23 >

1 Da talte Jesus til Skarerne og til sine Disciple og sagde:
Sa’an nan Yesu ya ce wa taron mutane da kuma almajiransa,
2 På Mose Stol sidde de skriftkloge og Farisæerne.
“Malaman dokoki da Farisiyawa suke zama a kujerar Musa.
3 Gører og holder derfor alt, hvad de sige eder; men gører ikke efter deres Gerninger; thi de sige det vel, men gøre det ikke.
Saboda haka dole ku yi musu biyayya, ku kuma yi duk abin da suka faɗa muku. Sai dai kada ku yi abin da suke yi, gama ba sa yin abin da suke wa’azi.
4 Men de binde svare Byrder, vanskelige at bære, og lægge dem på Menneskenes Skuldre; men selv ville de ikke bevæge dem med en Finger.
Sukan ɗaura kaya masu nauyi, su sa wa mutane a kafaɗa. Amma su kansu, ba sa ko sa yatsa su taimaka.
5 Men de gøre alle deres Gerninger for at beskues af Menneskene; thi de gøre deres Bederemme brede og Kvasterne på deres Klæder store.
“Kome suke yi, suna yi ne don mutane su gani. Sukan yi layunsufantam-fantam bakin rigunarsu kuma sukan kai har ƙasa;
6 Og de ville gerne sidde øverst til Bords ved Måltiderne og på de fornemste Pladser i Synagogerne
suna son wurin zaman manya a wurin biki, da kuma wuraren zama gaba-gaba a majami’u;
7 og lade sig hilse på Torvene og kaldes Rabbi af Menneskene.
suna so a yi ta gaisuwarsu a kasuwa, ana kuma riƙa ce musu, ‘Rabbi.’
8 Men I skulle ikke lade eder kalde Rabbi; thi een er eders Mester, men I ere alle Brødre.
“Amma kada a kira ku ‘Rabbi,’ gama kuna da Maigida ɗaya ne, ku duka kuwa,’yan’uwa ne.
9 Og I skulle ikke kalde nogen på Jorden eders Fader; thi een er eders Fader, han, som er i Himlene.
Kada kuma ku kira wani a duniya ‘uba,’ gama kuna da Uba ɗaya ne, yana kuwa a sama.
10 Ej heller skulle I lade eder kalde Vejledere; thi een er eders Vejleder, Kristus.
Ba kuwa za a kira ku ‘malam’ ba, gama kuna da Malami ɗaya ne, Kiristi.
11 Men den største iblandt eder skal være eders Tjener.
Mafi girma a cikinku, zai zama bawanku.
12 Men den, som ophøjer sig selv, skal fornedres, og den, som fornedrer sig selv, skal ophøjes.
Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi, duk kuma wanda ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.
13 Men ve eder, I skriftkloge og Farisæere, I Hyklere! thi I tillukke Himmeriges Rige for Menneskene; thi I gå ikke derind, og dem, som ville gå ind, tillade I det ikke.
“Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, ku munafukai! Kun rufe ƙofar mulkin sama a gaban mutane. Ku kanku ba ku shiga ba, ba kuwa bar waɗanda suke ƙoƙarin shiga su shiga ba.
14 Ve eder, I skriftkloge og Farisæere, I Hyklere! thi I opæde Enkers Huse og bede på Skrømt længe; derfor skulle I få des hårdere Dom.
15 Ve eder, I skriftkloge og Farisæere, I Hyklere! thi I drage om til Vands og til Lands for at vinde en eneste Tilhænger; og når han er bleven det, gøre I ham til et Helvedes Barn, dobbelt så slemt, som I selv ere. (Geenna g1067)
“Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan yi tafiye-tafiye zuwa ƙasashe, ku ƙetare teku don ku sami mai tuba ɗaya, sa’ad da ya tuba kuwa, sai ku mai da shi ɗan wuta fiye da ku, har sau biyu. (Geenna g1067)
16 Ve eder, I blinde Vejledere! I, som sige: Den, som sværger ved Templet, det er intet; men den, som sværger ved Guldet i Templet, han er forpligtet.
“Kaitonku, makafi jagora! Kukan ce, ‘In wani ya rantse da haikali, ba damuwa; amma in ya rantse da zinariyar haikali, sai rantsuwar ta kama shi.’
17 I Dårer og blinde! hvilket er da størst? Guldet eller Templet, som helliger Guldet?
Wawaye makafi! Wanne ya fi girma, zinariyar, ko haikalin da yake tsarkake zinariyar?
18 Fremdeles: Den, som sværger ved Alteret, det er intet; men den, som sværger ved Gaven derpå, han er forpligtet.
Kukan kuma ce, ‘In wani ya rantse da bagade, ba damuwa; amma in ya rantse da bayarwar da take bisansa, sai rantsuwar ta kama shi.’
19 I Dårer og blinde! hvilket er da størst? Gaven eller Alteret, som helliger Gaven?
Makafi kawai! Wanne ya fi girma, bayarwar, ko kuwa bagaden da yake tsarkake bayarwar?
20 Derfor, den, som sværger ved Alteret, sværger ved det og ved alt det, som er derpå.
Saboda haka, duk wanda ya rantse da bagade, ya rantse ne da bagaden tare da abin da yake bisansa.
21 Og den, som sværger ved Templet, sværger ved det og ved ham, som bor deri.
Kuma duk wanda ya rantse da haikali, ya rantse ne da shi da kuma wanda yake zaune a cikinsa.
22 Og den, som sværger ved Himmelen, sværger ved Guds Trone og ved ham, som sidder på den.
Duk kuma wanda ya rantse da sama, ya rantse ne da kursiyin Allah da kuma wanda yake zaune a kansa.
23 Ve eder, I skriftkloge og Farisæere, I Hyklere! thi I give Tiende af Mynte og Dild og Kommen og have forsømt de Ting i Loven, der have større Vægt, Retten og Barmhjertigheden og Troskaben. Disse Ting burde man gøre og ikke forsømme hine.
“Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan ba da kashi ɗaya bisa goma na kayan yajinku, na’ana’a, anise, da lafsur. Amma kun ƙyale abubuwan da suka fi girma na dokoki, adalci, jinƙai da aminci. Waɗannan ne ya kamata da kun kiyaye ba tare da kun ƙyale sauran ba.
24 I blinde Vejledere, I, som si Myggen af, men nedsluge Kamelen!
Makafi jagora! Kukan tace ƙwaro ɗan mitsil amma sai ku haɗiye raƙumi.
25 Ve eder, I skriftkloge og Farisæere, I Hyklere! thi I rense det udvendige af Bægeret og Fadet; men indvendigt ere de fulde af Rov og Umættelighed.
“Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan wanke bayan kwaf da kwano, amma a ciki, cike suke da zalunci da sonkai.
26 Du blinde Farisæer! rens først det indvendige af Bægeret og Fadet, for at også det udvendige af dem kan blive rent.
Kai makaho Bafarisiye! Ka fara wanke cikin kwaf da kwano, sa’an nan bayan ma zai zama da tsabta.
27 Ve eder, I skriftkloge og Farisæere, I Hyklere! thi I ere ligesom kalkede Grave, der jo synes dejlige udvendigt, men indvendigt ere fulde af døde Ben og al Urenhed.
“Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kuna kama da kaburburan da aka shafa musu farin fenti, waɗanda suna da kyan gani a waje, amma a ciki, cike suke da ƙasusuwan matattu da kuma kowane irin abu mai ƙazanta.
28 Således synes også I vel udvortes retfærdige for Menneskene; men indvortes ere I fulde af Hykleri og Lovløshed.
Haka ku ma, a waje, a idon mutane, ku masu adalci ne, amma a ciki, cike kuke da munafunci da mugunta.
29 Ve eder, I skriftkloge og Farisæere, I Hyklere! thi I bygge Profeternes Grave og pryde de retfærdiges Gravsteder og sige:
“Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan gina kaburbura don annabawa, ku kuma yi wa kaburburan mutane masu adalci ado.
30 Havde vi været til i vore Fædres Dage, da havde vi ikke været delagtige med dem i Profeternes Blod.
Kuna cewa, ‘Da mun kasance a zamanin kakanninmu, ai, da ba mu haɗa hannu da su muka karkashe annabawa ba.’
31 Altså give I eder selv det Vidnesbyrd, at I ere Sønner af dem, som have ihjelslået Profeterne.
Ta haka kuna ba da shaida a kanku cewa ku zuriyar waɗanda suka karkashe annabawa ne.
32 Så gører da også I eders Fædres Mål fuldt!
To, sai ku ci gaba ku cikasa ayyukan da kakanninku suka fara!
33 I Slanger! I Øgleunger! hvorledes kunne I undfly Helvedes Dom? (Geenna g1067)
“Ku macizai!’Ya’yan macizai! Ta yaya za ku tsere wa hukuncin jahannama ta wuta? (Geenna g1067)
34 Derfor se, jeg sender til eder Profeter og vise og skriftkloge; nogle af dem skulle I slå ihjel og korsfæste, og nogle af dem skulle I hudstryge i, eders Synagoger og forfølge fra Stad til Stad,
Saboda haka ina aika muku da annabawa, da masu hikima da malamai. Waɗansunsu za ku kashe ku kuma gicciye; waɗansu kuma za ku yi musu bulala a majami’unku kuna kuma binsu gari-gari.
35 for at alt det retfærdige Blod skal komme over eder, som er udgydt på Jorden, fra den retfærdige Abels Blod indtil Sakarias's, Barakias's Søns, Blod, hvem I sloge ihjel imellem Templet og Alteret.
Ta haka alhakin jinin masu adalcin da aka zubar a duniya, tun daga jinin Habila mai adalci, zuwa jinin Zakariya ɗan Berekiya, wanda kuka kashe tsakanin haikali da bagade zai koma kanku.
36 Sandelig, siger jeg eder, alt dette skal komme over denne Slægt.
Gaskiya nake gaya muku, duk wannan zai auko wa wannan zamani.
37 Jerusalem! Jerusalem! som ihjelslår Profeterne og stener dem, som ere sendte til dig, hvor ofte vilde jeg samle dine Børn, ligesom en Høne samler sine Kyllinger under Vingerne! Og I vilde ikke.
“Urushalima, ayya Urushalima, ke da kike kashe annabawa, kike kuma jifan waɗanda aka aiko gare ki, sau da sau na so in tattara’ya’yanki wuri ɗaya, yadda kaza takan tattara’ya’yanta cikin fikafikanta, amma kuka ƙi.
38 Se, eders Hus lades eder øde!
Ga shi, an bar muku gidanku a yashe.
39 Thi jeg siger eder: I skulle ingenlunde se mig fra nu af, indtil I sige: Velsignet være den, som kommer, i Herrens Navn!"
Gama ina gaya muku, ba za ku sāke ganina ba sai kun ce, ‘Mai albarka ne wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji.’”

< Matthæus 23 >