< 3 Mosebog 19 >

1 HERREN talede fremdeles til Moses og sagde:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Tal til hele Israeliternes Menighed og sig til dem: I skal være hellige, thi jeg HERREN eders Gud er hellig!
“Yi wa taron jama’ar Isra’ila gaba ɗaya magana, ka ce musu, ‘Ku zama masu tsarki, domin Ni, Ubangiji Allahnku, mai tsarki ne.
3 I skal frygte hver sin Moder og sin Fader, og mine Sabbater skal I holde. Jeg er HERREN eders Gud!
“‘Dole kowannenku yă girmama mahaifiyarsa da mahaifinsa, dole kuma ku kiyaye Asabbacina. Ni ne Ubangiji Allahnku.
4 Vend eder ikke til Afguderne og gør eder ikke støbte Gudebilleder! Jeg er HERREN eders Gud!
“‘Kada ku juyo ga gumaka, ko ku yi wa kanku allolin da aka yi zubi da ƙarfe. Ni ne Ubangiji Allahnku.
5 Når I ofrer Takoffer til HERREN, skal I ofre det således, at I kan vinde Guds Velbehag.
“‘Sa’ad da kuka miƙa hadaya ta salama ga Ubangiji, ku miƙa ta yadda za tă karɓu a madadinku.
6 Den Dag, I ofrer det, og Dagen efter må det spises, men hvad der levnes til den tredje Dag, skal opbrændes;
Za a ci ta a ranar da kuka miƙa ta, ko kuwa a kashegarin; duk abin da ya rage har kwana ta uku dole a ƙone shi.
7 spises det den tredje Dag, er det at regne for råddent Kød og vinder ikke Guds Velbehag;
In aka ci ta a rana ta uku, marar tsabta ce, ba kuma za a karɓe ta ba.
8 den, der spiser deraf, skal undgælde for sin Brøde, thi han vanhelliger det, som var helliget HERREN, og det Menneske skal udryddes af sin Slægt.
Duk wanda ya ci ta zai zama da laifi domin ya ƙazantar da abin da yake da tsarki ga Ubangiji, dole a raba mutumin nan da mutanensa.
9 Når I høster eders Lands Høst, må du ikke høste helt hen til Kanten af din Mark, ej heller må du sanke Efterslætten efter din Høst.
“‘Sa’ad da kuka yi girbin amfanin gonarku, kada ku girbe har zuwa gefen gonar, ko ku yi kalan girbinku.
10 Heller ikke må du bolde Efterhøst eller sanke de nedfaldne Bær i din Vingård; til den fattige og den fremmede skal du lade det blive tilbage. Jeg er HERREN eders Gud!
Kada ku koma gonar inabinku kuna kala, ko ku tattara’ya’yan inabin da suka fāffāɗi. Ku bar su domin matalauta da kuma baƙi. Ni ne Ubangiji Allahnku.
11 I må ikke stjæle, I må ikke lyve, I må ikke bedrage hverandre.
“‘Kada ku yi sata. “‘Kada ku yi ƙarya. “‘Kada ku ruɗe juna.
12 I må ikke sværge falsk ved mit Navn, så du vanhelliger din Guds Navn. Jeg er HERREN!
“‘Kada ku rantse bisa ƙarya da sunana, ta haka har ku ƙasƙantar da sunan Allahnku. Ni ne Ubangiji.
13 Du må intet aftvinge din Næste, du må intet røve; Daglejerens Løn må ikke blive hos dig Natten over.
“‘Kada ku zalunci maƙwabcinku, ko ku yi masa ƙwace. “‘Kada ku riƙe albashin ma’aikaci yă kwana.
14 Du må ikke forbande den døve eller lægge Stød for den blindes Fod, du skal frygte din Gud. Jeg er HERREN!
“‘Kada ku zagi kurma, ko ku sa abin tuntuɓe a gaban makaho, amma ku ji tsoron Allahnku. Ni ne Ubangiji.
15 I må ikke øve Uret, når I holder Rettergang; du må ikke begunstige den ringe, ej heller tage Parti for den store, men du skal dømme din Næste med Retfærdighed.
“‘Kada ku yi rashin adalci cikin shari’a; kada ku nuna sonkai ga matalauci, ko ku goyi bayan mai arziki, amma ku shari’anta maƙwabci cikin gaskiya.
16 Du må ikke gå rundt og bagvaske din Landsmand eller stå din Næste efter Livet. Jeg er HERREN!
“‘Kada ku yi ta yawo kuna yaɗa ƙarya a cikin mutanenku. “‘Kada ku yi wani abin da zai sa ran maƙwabcinku cikin hatsari. Ni ne Ubangiji.
17 Du må ikke bære Nag til din Broder i dit Hjerte, men du skal tale din Næste til Rette, at du ikke skal pådrage dig Synd for hans Skyld.
“‘Kada ka yi ƙiyayyar ɗan’uwanka a zuciya. Ka tsawata wa maƙwabcinka da gaske don kada ka sami rabo cikin laifinsa.
18 Du må ikke hævne dig eller gemme på Vrede mod dit Folks Børn, du skal elske din Næste som dig selv. Jeg er HERREN!
“‘Kada ka nemi yin ramuwa, ko ka riƙe wani cikin mutanenka a zuciya, amma ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka. Ni ne Ubangiji.
19 Hold mine Anordninger! Du må ikke lade to Slags Kvæg parre sig med hinanden; du må ikke så to Slags Sæd i din Mark; og du må ikke bære Klæder, der er vævede af to Slags Garn.
“‘Ku kiyaye farillaina. “‘Kada ku sa dabbobin da ba iri ɗaya ba su yi barbara. “‘Kada ku yi shuki iri biyu a gonarku. “‘Kada ku sa rigar da aka saƙa da yadi iri biyu.
20 Når en Mand har Samleje med en Kvinde, og det er en Trælkvinde, en anden Mands Medhustru, som ikke er løskøbt eller frigivet, så skal Afstraffelse finde Sted; dog skal de ikke lide Døden, thi hun var ikke frigivet.
“‘In wani ya kwana da mace wadda take baiwa, wadda aka yi wa wani alkawari amma bai fanshe ta ba, ko kuwa ba a’yantar da ita ba, dole a yi hukuncin da ya dace. Duk da haka ba za a kashe su ba, domin ba a’yantar da ita ba.
21 Og han skal bringe sit Skyldoffer for HERREN til Åbenbaringsteltets Indgang, en Skyldoffervæder,
Dole mutumin da ya kwana da ita yă kawo rago a ƙofar Tentin Sujada domin hadaya don laifi ga Ubangiji.
22 og Præsten skal med Skyldoffervæderen skaffe ham Soning for HERRENs Åsyn for den Synd, han har begået, så han finder Tilgivelse for den Synd, han har begået.
Da ragon hadaya don laifin ne firist zai yi kafara saboda mutumin a gaban Ubangiji saboda zunubin da ya yi, za a kuwa gafarta zunubinsa.
23 Når I kommer ind i Landet og planter alskens Frugttræer, skal I lade deres Forhud, den første Frugt, urørt; i tre År skal de være eder uomskårne og må ikke spises;
“‘Sa’ad da kuka shiga ƙasar kuka kuma shuka kowane irin itace mai’ya’ya na ci, ku ɗauki’ya’yan itatuwan nan a matsayi an hana ku ci. Shekara uku za ku ɗauka a matsayi an hana ku, ba za ku ci su ba.
24 det fjerde År skal al deres Frugt under Høstjubel helliges HERREN;
A shekara ta huɗu, dukan’ya’yansu za su zama tsarkakakku, hadaya ta yabo ga Ubangiji.
25 først det femte År må I spise deres Frugt, for at I kan få så meget større Udbytte deraf. Jeg er HERREN eders Gud!
Amma a shekara ta biyar, za ku iya cin’ya’yan itatuwan. Ta haka girbinku zai ƙaru. Ni ne Ubangiji Allahnku.
26 I må ikke spise noget med Blodet i. I må ikke give eder af med at tage Varsler og øve Trolddom.
“‘Kada ku ci wani abinci tare da jini a cikinsa. “‘Kada ku yi duba ko sihiri.
27 I må ikke runde Håret på Tindingerne; og du må ikke studse dit Skæg;
“‘Ba za ka aske gefe-gefe na gashin kanka ba, ko ku aske gemunku.
28 I må ikke gøre Indsnit i eders Legeme for de dødes Skyld eller indridse Tegn på eder. Jeg er HERREN!
“‘Kada ku tsattsaga jikunanku saboda matattu, ba kuwa za ku yi wa kanku zāne-zāne a jiki ba. Ni ne Ubangiji.
29 Du må ikke vanhellige din Datter ved at lade hende bedrive Hor, for at ikke Landet skal forfalde til Horeri og fyldes med Utugt.
“‘Kada ka ƙasƙantar da’yarka ta wurin mai da ita karuwa, in ba haka ba ƙasar za tă juya ga karuwanci tă kuma cika da mugunta.
30 Mine Sabbater skal I bolde, og min Helligdom skal I frygte. Jeg er HERREN!
“‘Ku kiyaye Asabbacina, ku kuma girmama wuri mai tsarkina. Ni ne Ubangiji.
31 Henvend eder ikke til Genfærd og Sandsigerånder; søg dem ikke, så I gør eder urene ved dem. Jeg er HERREN eders Gud!
“‘Kada ku juya ga masu duba, ko ku nemi shawarar bokaye, gama za ku ƙazantu ta wurinsu. Ni ne Ubangiji Allahnku.
32 Du skal rejse dig for de grå Hår og ære Oldingen, og du skal frygte din Gud. Jeg er HERREN!
“‘Ku miƙe tsaye a gaban tsofaffi, ku nuna bangirma ga waɗanda suka tsufa, ku kuma girmama Allahnku. Ni ne Ubangiji.
33 Når en fremmed bor hos dig i eders Land, må I ikke lade ham lide Overlast;
“‘Sa’ad da baƙo yana zama tare da ku a ƙasarku, kada ku wulaƙanta shi.
34 som en af eders egne skal I regne den fremmede, der bor hos eder, og du1 skal elske ham som dig selv, thi I var selv fremmede i Ægypten. Jeg et HERREN eders Guld!
Dole ku ɗauki baƙon da yake zama tare da ku kamar haifaffe ɗan ƙasa. Ku ƙaunace shi kamar kanku, gama dā ku ma baƙi ne a Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.
35 Når I holder Rettergang, må I ikke øve Uret ved Længdemål, Vægt eller Rummål;
“‘Kada ku yi amfani da mudun ƙarya sa’ad da kuke awon tsawo, nauyi, ko yawan abu.
36 Vægtskåle, der vejer rigtigt, Lodder, der holder Vægt, Efa og Hin, der holder Mål, skal I have. Jeg er HERREN eders Gud, som førte eder ud af Ægypten!
Ku yi amfani da ma’auni na gaskiya da mudu na gaskiya, da kuma magwaji na gaskiya. Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar.
37 Hold alle mine Anordninger og Lovbud og gør efter dem. Jeg er HERREN!
“‘Ku kiyaye dukan farillaina da kuma dukan dokokina, ku kuma bi su. Ni ne Ubangiji.’”

< 3 Mosebog 19 >