< Job 33 >

1 Men hør nu Job, på min Tale og lyt til alle mine Ord!
“Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
2 Se, jeg har åbnet min Mund, min Tunge taler i Ganen;
Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
3 mine Ord er talt af oprigtigt Hjerte, mine Læber fører lutret Tale.
Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
4 Guds Ånd har skabt mig, den Almægtiges Ånde har givet mig Liv.
Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
5 Svar mig, i Fald du kan, rust dig imod mig, mød frem!
Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
6 Se, jeg er din Lige for Gud, også jeg er taget af Ler;
Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
7 Rædsel for mig skal ikke skræmme dig, min Hånd skal ej ligge tyngende på dig.
Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
8 Dog, det har du sagt i mit Påhør, jeg hørte så lydende Ord:
“Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
9 "Jeg er ren og uden Brøde, lydeløs, uden Skyld;
‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
10 men han søger Påskud imod mig, regner mig for sin Fjende;
Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
11 han lægger mine Fødder i Blokken, vogter på alle mine Veje."
ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
12 Se, der har du Uret, det er mit Svar, thi Gud er større end Mennesket.
“Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
13 Hvorfor tvistes du med ham, fordi han ej svarer på dine Ord?
Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
14 Thi på een Måde taler Gud, ja på to, men man ænser det ikke:
Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
15 I Drømme, i natligt Syn, når Dvale falder på Mennesker, når de slumrende hviler på Lejet;
A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
16 da åbner han Menneskers Øre, gør dem angst med Skræmmebilleder
mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
17 for at få Mennessket bort fra Uret og udrydde Hovmod af Manden,
don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
18 holde hans Sjæl fra Graven, hans Liv fra Våbendød.
don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
19 Eller han revses med Smerter på Lejet, uafbrudt sfår der Hamp i hans Ben;
“Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
20 Livet i ham væmmes ved Brød og hans Sjæl ved lækker Mad
yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
21 hans Kød svinder hen, så det ikke ses, hans Knogler, som før ikke sås, bliver blottet;
Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
22 hans Sjæl kommer Graven nær, hans Liv de dræbende Magter.
Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
23 Hvis da en Engel er på hans Side, een blandt de tusind Talsmænd, som varsler Mennesket Tugt,
Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
24 og den viser ham Nåde og siger: "Fri ham fra at synke i Graven, Løsepenge har jeg fået!"
yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
25 da svulmer hans Legem af Friskhed, han oplever atter sin Ungdom.
Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
26 Han beder til Gud, og han er ham nådig, han skuer med Jubel hans Åsyn, fortæller Mennesker om sin Frelse.
Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
27 Han synger det ud for Folk: "Jeg synded og krænkede Retten og fik dog ej Løn som forskyldt!
Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
28 Han har friet min Sjæl fra at fare i Grav, mit Liv ser Lyset med Lyst!"
Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
29 Se, alle disse Ting gør Gud to Gange, ja tre med Mennesket
“Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
30 for at redde hans Sjæl fra Graven, så han skuer Livets Lys!
Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
31 Lyt til og hør mig, Job, ti stille, så jeg kan tale!
“Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
32 Har du noget at sige, så svar mig, tal, thi gerne gav jeg dig Ret;
In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
33 hvis ikke, så høre du på mig, ti stille, at jeg kan lære dig Visdom!
Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”

< Job 33 >