< Jeremias 42 >

1 Så kom alle hærførerene og Johanan, Kareas søn, og Azarja, Maasejas Søn, med alt Folket, store og små,
Sa’an nan dukan shugabannin sojoji, haɗe da Yohanan ɗan Kareya da Yezaniya ɗan Hoshahiya, da dukan mutane daga ƙarami zuwa babba, suka zo wurin
2 og sagde til Profeten Jeremias: "Måtte vor Bøn nå dit Øre, så du beder til HERREN din Gud for hele denne Rest, thi som du ser os her, er vi kun få tilbage af mange.
Irmiya annabi suka ce masa, “Muna roƙonka ka ji kukanmu ka kuma yi addu’a ga Ubangiji Allahnka saboda dukan wannan raguwar mutane. Gama kamar yadda kake gani yanzu, ko da yake dā muna da yawa, yanzu ɗan kaɗan muka rage.
3 Måtte HERREN din Gud kundgøre os, hvilken Vej vi skal gå, og hvad vi skal gøre!"
Ka yi addu’a cewa Ubangiji Allahnka zai faɗa mana inda za mu tafi da kuma abin da za mu yi.”
4 Profeten Jeremias svarede: "Godt! Jeg vil bede til HERREN eders Gud, som I ønsker; og alt hvad HERREN svarer, vil jeg kundgøre eder uden at forholde eder et Ord."
Sai Irmiya ya amsa ya ce, “Na ji ku, tabbatacce zan yi addu’a ga Ubangiji Allahnku yadda kuka roƙa; zan faɗa muku duk abin da Ubangiji ya faɗa ba kuwa zan ɓoye muku kome ba.”
5 De sagde da til Jeremias: "HERREN skal være et sandt og troværdigt Vidne imod os, hvis vi ikke retter os efter hvert Ord, HERREN din Gud sender os ved dig.
Sa’an nan suka ce wa Irmiya, “Ubangiji ya zama shaida na gaskiya da kuma aminci a kanmu in ba mu yi bisa da duk abin da Ubangiji Allahnka ya aike ka ka faɗa mana ba.
6 Det være godt eller ondt, vi vil adlyde HERREN vor Guds Røst, til hvem vi sender dig, at det må gå os vel, når vi adlyder HERREN vor Guds Røst."
Ko ya gamshe mu ko bai gamshe mu ba, za mu yi biyayya da Ubangiji Allahnmu, ga wanda muke aikan ka, saboda ya zama mana da amfani, gama za mu yi biyayya da Ubangiji Allahnmu.”
7 Ti Dage efter kom HERRENs Ord til Jeremias.
Bayan kwana goma sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya.
8 Så sammenkaldte han Johaoan, Kareas Søn, alle Hærføreme, der var med ham, og alt Folket, store og små,
Saboda haka ya kira Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji waɗanda suke tare da shi da dukan jama’a daga ƙarami zuwa babba.
9 og sagde: Så siger HERREN, Israels Gud, til hvem I sendte mig, for at eders Bøn måtte nå ind for hans Åsyn:
Ya ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda kuka aike ni gare shi don in gabatar da kukanku, yana cewa,
10 Hvis I bliver her i Landet, vil jeg bygge eder og ikke nedbryde eder, plante eder og ikke rykke eder op, thi jeg angrer det onde, jeg har gjort eder.
‘In kuka zauna a wannan ƙasa, zan gina ku ba zan kuwa rushe ku ba; zan dasa ku ba kuwa zan tumɓuke ku ba, gama ina baƙin ciki a kan masifar da na aukar a kanku.
11 Frygt ikke for Babels Konge, således som I gør, frygt ikke for ham, lyder det fra HERREN, thi jeg er med eder for at frelse og redde eder af hans Hånd.
Kada ku ji tsoron sarkin Babilon, wanda kuke tsoro a yanzu. Kada ku ji tsoronsa, in ji Ubangiji, gama ina tare da ku zan kuma cece ku daga hannuwansa.
12 Jeg vil lade eder finde Barmhjertighed, og han skal forbarme sig over eder og lade eder bo i eders Land.
Zan nuna muku jinƙai don yă nuna muku jinƙai ya kuma maido da ku ƙasarku.’
13 Hvis I derimod ikke hører HERREN eders Guds Røst, idet I siger, at I ikke vil bo her i Landet,
“Amma fa, in kuka ce, ‘Ba za mu zauna a wannan ƙasa ba,’ ta haka kuka kuma nuna rashin biyayya ga Ubangiji Allahnku,
14 men drage til Ægypten og bo der for ikke mere at se Krig eller høre Hornets Klang eller hungre efter Brød,
in kuma kuka ce, ‘A’a, za mu tafi mu zauna a Masar, inda ba za mu ga yaƙi ko mu ji ƙarar ƙaho ko mu ji yunwa ba,’
15 så hør nu HERRENs Ord, Judas Rest. Så siger Hærskarers HERRE, Israels Gud: Hvis I virkelig har i Sinde at drage til Ægypten og drager derned for at bo der som fremmede,
to, ku ji maganar Ubangiji, ya raguwar Yahuda. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘In kun ƙudura ku tafi Masar kuka kuma tafi kun zauna a can,
16 så skal Sværdet, som I frygter, nå eder der i Ægypten, og Hungeren, som I ængstes for, skal følge efter eder til Ægypten, og I skal omkomme der;
takobin da kuke tsoro zai same ku a can, kuma yunwar da kuke tsoro za tă bi ku zuwa Masar, a can kuwa za ku mutu.
17 alle de Mænd, som har i Sinde at drage til Ægypten for at bo der som fremmede, skal dø ved Sværd, Hunger og Pest, og ingen af dem skal blive tilovers og undslippe fra den Ulykke, jeg sender over dem.
Tabbatacce, duk waɗanda suka ƙudura suka tafi Masar su zauna a can za su mutu ta wurin takobi, yunwa da annoba; ba ko ɗayansu zai tsira ko ya kuɓuta wa masifar da zan aukar a kansu.’
18 Thi så siger Hærskarers HERRE, Israels Gud: Som min Vrede og Harme udgød sig over Jerusalems Indbyggere, således skal min Harme udgyde sig over eder, når I drager til Ægypten, og I skal blive et. Edens, Rædselens, Forbandelsens og Spottens Tegn og ikke mere få dette Sted at se.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Kamar yadda na kwararo fushina da hasalata a kan mazaunan Urushalima, haka kuma zan kwararo fushina a kanku sa’ad da kuka tafi Masar. Za ku zama abin la’ana da abin tsoro, abin ƙyama da abin ba’a; ba za ku ƙara ganin wannan wuri ba.’
19 Dette er HERRENs Ord til eder. Judas Rest: Drag ikke til Ægypten! I skal vide, at jeg i Dag har advaret eder.
“Ya ku raguwar Yahuda, Ubangiji ya ce muku, ‘Kada ku je Masar.’ Ku tabbatar da wannan. Na gargaɗe ku yau
20 Thi I nedkalder ondt over eder selv, når I sender mig til HERREN eders Gud og siger: "Bed for os til HERREN vor Gud! Hvad HERREN vor Gud siger, skal du nøje kundgøre os, så vil vi gøre det,"
cewa in kun yi kuskure sa’ad da kuka aike ni wurin Ubangiji Allahnku kuka kuma ce, ‘Yi mana addu’a ga Ubangiji Allahnmu; ka faɗa mana duk abin da ya faɗa za mu kuwa aikata.’
21 og I så alligevel ikke adlyder HERREN eders Guds Røst og gør alt, hvad han sendte eder Bud om.
Na faɗa muku yau, amma har yanzu ba ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku cikin dukan abin da ya aiko ni in faɗa muku ba.
22 Så vid da nu, at I skal omkomme ved Sværd, Hunger og Pest på det Sted, hvor I agter at gå hen for at bo der somfremmede.
Saboda haka yanzu, ku tabbatar da wannan. Za ku mutu ta wurin takobi, yunwa da annoba a wurin da kuke so ku tafi ku zauna.”

< Jeremias 42 >