< Esajas 30 >

1 Ve de genstridige Børn så lyder det fra HERREN som fuldbyrder Råd, der ej er fra mig, slutter Forbund, uden min Ånd er med, for at dynge Synd på Synd,
“Kaiton’ya’ya masu tayarwa,” in ji Ubangiji, “ga waɗanda suke ƙulle-ƙullen da ba nawa ba, suna yin yarjejjeniya, amma ba ta Ruhuna ba, suna jibga zunubi a kan zunubi;
2 de, som går ned til Ægypten uden at spørge min Mund for at værne sig ved Faraos Værn, søge Ly i Ægyptens Skygge!
waɗanda suka gangara zuwa Masar ba tare da sun nemi shawarata; waɗanda suke neman taimakon kāriyar Fir’auna, don neman inuwar mafakar Masar.
3 Faraos Værn skal blive jer til Skam og Lyet i Ægyptens Skygge til Skændsel.
Amma kāriyar Fir’auna za tă zama muku abin kunya, inuwar Masar za tă jawo muku kunya.
4 Thi er end hans Fyrster i Zoan, hans Sendebud nået til Hanes,
Ko da yake suna da shugabanni a Zowan kuma jakadunsu sun iso Hanes,
5 enhver skal få Skam af et Folk, der ikke kan bringe dem Hjælp, ej være til Gavn eller Hjælp, men kun til Skam og Skændsel.
kowa zai sha kunya saboda mutanen da ba su da amfani gare su, waɗanda ba sa taimako ko amfani, sai dai jawo kunya da da-na-sani.”
6 Et Udsagn om Sydlandets Dyr: Gennem Angstens og Trængselens Land, hvor Løvinde og Løve har hjemme, Giftsnog og vinget Slange, fører de på Æslers Ryg deres Gods, på Kamelers Pukkel deres Skatte til et Folk, der ikke kan hjælpe.
Allah ya faɗa game da dabbobin Negeb cewa, Ta cikin ƙasa mai wahala da mai hatsari inda zakoki da zakanya, inda macizai masu dafi da macizai masu tashi sama suke, jakadu na ɗaukan arzikinsu a kan jakuna, dukiyarsu a kan raƙuma, zuwa ƙasan nan marar riba,
7 Ægyptens Hjælp er Vind og Luft. Derfor kalder jeg det "Rahab, der hytter sig."
zuwa Masar, wadda taimakonta marar amfani ne. Saboda haka na yi mata laƙabi Rahab Marar Yin Kome.
8 Gå nu hen og skriv det på en Tavle i deres Påsyn og optegn det i en Bog, at det i kommende Tider kan stå som Vidnesbyrd evindelig.
Tafi yanzu, ka rubuta musu a kan allo, ka rubuta shi a kan littafi, cewa kwanaki suna zuwa zai zama madawwamin shaida.
9 Thi det er et stivsindet Folk, svigefulde Børn, Børn, der ikke vil høre HERRENs Lov,
Waɗannan mutane masu tawaye,’ya’ya masu ruɗu,’ya’yan da ba sa niyya su saurara ga umarnan Ubangiji.
10 som siger til Seerne: "Se ingen Syner!" til fremsynte: "Skuer os ikke det rette! Tal Smiger til os, skuer os Blændværk,
Sukan ce wa masu gani, “Kada ku ƙara ganin wahayi!” Ga annabawa kuwa sukan ce, “Kada ku ƙara ba mu wahayin abin da yake daidai! Faɗa mana abubuwan da muke so mu ji ne kawai, ku yi annabcin abin da zai ruɗe mu.
11 vig bort fra Vejen, bøj af fra Stien, lad os være i Fred for Israels Hellige!"
Ku bar wannan hanya, ku tashi daga wannan hanya, ku kuma daina kalubalantarmu da Mai Tsarkin nan na Isra’ila!”
12 Derfor, så siger Israels Hellige: Siden I ringeagter dette Ord og stoler på krumt og kroget og støtter jer til det,
Saboda haka, ga abin da Mai Tsarkin nan na Isra’ila yake cewa, “Saboda haka kun ƙi wannan saƙo, kuka dogara ga aikin kama-karya kuka kuma dogara ga yin ruɗu,
13 derfor skal denne Brøde blive for eder som en truende, voksende Revne i en knejsende Mur, hvis Fald vil indtræffe brat, lige i et Nu;
wannan zunubi zai zama muku kamar bango mai tsayi, tsagagge da yake kuma fāɗuwa, da zai rushe nan da nan, ba tsammani.
14 den sønderbrydes som Lerkar; der skånselsløst knuses; blandt Stumperne finder man ikke et Skår, hvori man kan hente en Glød fra Bålet eller øse Vand af Brønden.
Zai rushe kucu-kucu kamar tukunyar yumɓu, ya ragargaje ƙaf har cikin gutsattsarinsa ba za a sami ko ɗan katanga don ɗiba garwashin wuta ko a ɗiba ruwa daga tanki ba.”
15 Thi således sagde den Herre HERREN, Israels Hellige: Ved Omvendelse og Stilhed skal I frelses, i Ro og Tillid er eders Styrke.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya faɗa, “Cikin tuba da hutu ne kaɗai cetonku yake, cikin shiru da dogara gare ni ne za ku sami ƙarfinku, amma ba za ku sami ko ɗaya a cikinsu ba.
16 Men I vilde ikke; I sagde: "Nej, vi jager på Heste" I skal derfor jages!"Vi rider på Rapfod" I skal derfor forfølges af rappe.
Kun ce, ‘A’a, za mu gudu a kan dawakai.’ Saboda haka za ku gudu! Kun ce, ‘Za mu hau dawakai masu sauri mu gudu.’ Saboda haka masu fafararku za su fi ku gudu!
17 Tusind skal fly for een, som truer; Flugten skal I tage for fem, som truer, til I kun er en Rest som Stangen på Bjergets Tinde, som Banneret oppe på Højen.
Dubu za su gudu don barazanar mutum guda; da jin barazanar mutane biyar dukanku za ku yi ta gudu sai an bar ku kamar sandar tuta a kan dutse, kamar tuta a kan tudu.”
18 Derfor længes HERREN efter at vise eder Nåde, derfor står han op for at forbarme sig over eder. Thi Rettens Gud er HERREN; salige alle, der længes efter ham!
Duk da haka Ubangiji yana marmari ya yi muku alheri; ya tashi don yă nuna muku jinƙai. Gama Ubangiji Allah ne mai aikata gaskiya. Masu albarka ne dukanku waɗanda suke dogara gare shi!
19 Ja, du Folk i Zion, du, som bor i Jerusalem, lad ikke Gråden overmande dig! Nådig vil han vise dig Nåde, når du råber; så snart han hører dig, svarer han.
Ya mutanen Sihiyona, waɗanda suke zama a Urushalima, ba za ku ƙara kuka ba. Zai zama mai alheri sa’ad da kuka yi kukan neman taimako! Da zarar ya ji, zai amsa muku.
20 Herren skal give eder Trængselsbrød og Fængselsdrik; men så skal din Vejleder ikke mere dølge sig, dine, Øjne skal skue din Vejleder;
Ko da yake Ubangiji yakan ba da abincin azaba da ruwan wahala, ba za a ƙara ɓoye malamanku ba; da idanunku za ku gan su.
21 dine Ører skal høre det Ord bag ved dig: "Her er Vejen, I skal gå!" hver Gang I er ved at vige til højre eller venstre.
Ko kun juye dama ko hagu, kunnuwanku za su ji murya a bayanku tana cewa, “Ga hanya; ku yi tafiya a kai.”
22 Da skal du holde dine Sølvbilleders Overtræk og dine Guldbilleders Klædning for urene; du skal slænge dem bort som Skarn. "Herud!" skal du sige til dem.
Sa’an nan za ku ƙazantar da gumakanku da kuka dalaye da zinariya; za ku zubar da su kamar rigar al’adar mace ku kuma ce musu, “Ku ɓace mana da gani!”
23 Da giver han Regn til Sæden, du, sår i din Jord; og Brødet, som din Jord bærer, skal være kraftigt og nærende. På hin Dag græsser dit Kvæg på vide Vange;
Zai kuma aiko muku da ruwan sama don shuki a ƙasa, kuma abincin da zai fito daga gona zai zama mai albarka da kuma mai yawa. A wannan rana shanu za su yi kiwo a wadatacciyar makiyaya.
24 Okserne og Æslerne, der arbejder på Marken, skal æde saltet Blandfoder, renset med Kasteskovl og Fork.
Shanunku da jakunanku da suke huɗar gonakinku za su ci harawa mafi kyau, wanda an sheƙe shi da babban cokali mai yatsu da kuma babban cokali.
25 På hvert højt Bjerg og hver knejsende Banke skal Kilder vælde frem med rindende Vand på det store Blodbads Dag, når Tårne falder.
A ranar babban kisa, sa’ad da hasumiyoyi za su fāɗi, rafuffukan ruwa za su malalo a kan kowane dutse da kowane tudu mai tsawo.
26 Månens Lys skal blive som Solens, og Solens Lys skal blive syvfold stærkere, som syv Dages Lys, på hin Dag da HERREN forbinder sit Folks Brud og læger dets slagne Sår.
Wata zai yi haske kamar rana, kuma hasken rana zai ma yi sau bakwai na haskenta, kamar hasken cikakku ranaku bakwai, sa’ad da Ubangiji zai ɗaura raunukan mutanensa ya kuma warkar da raunukan da ya yi musu.
27 Se, HERRENs Navn kommer langvejsfra i brændende Vrede, med tunge Skyer; hans Læber skummer af Vrede, fortærende Ild er hans Tunge,
Duba, Sunan Ubangiji yana zuwa daga nesa, tare da fushi mai ƙuna da kuma baƙin hayaƙi; leɓunansa sun cika da fushi, harshensa kuma wuta ce mai cinyewa.
28 hans Ånde som en rivende Strøm, der når til Halsen. Folkene ryster han i Undergangens Sold, lægger Vildelsens Bidsel i Folkeslags Mund.
Numfashinsa kamar raƙuman ruwa masu gudu yana tashi har zuwa wuya. Yakan tankaɗe al’ummai cikin lariyar hallaka; yakan sa a muƙamuƙan mutane linzamin da zai jagorance su su kauce.
29 Sang skal der være hos eder som i Natten, når Højtid går ind, en Hjertens Glæde som en Vandring til Fløjte mod HERRENs Bjerg, mod Israels Klippe.
Za ku kuma rera kamar a daren da kuke shagalin biki mai tsarki; zukatanku za su yi farin ciki kamar sa’ad da mutane sukan haura da busa zuwa dutsen Ubangiji, zuwa Dutse na Isra’ila.
30 HERREN lader høre sin Højheds Røst og viser sin Arm, der slår ned med fnysende Vrede, ædende Lue, Skybrud, skyllende Regn og Hagl.
Ubangiji zai sa mutane su ji muryarsa mai daraja ya kuma sa su ga hannunsa na saukowa tare da fushi mai ƙuna da kuma wuta mai cinyewa, gizagizai za su ɓarke, za a yi hadarin tsawa da ƙanƙara.
31 For HERRENs Røst bliver Assur ræd, med Kæppen slår han;
Muryar Ubangiji za tă firgita Assuriya da sandar mulkinsa zai kashe su.
32 hvert et Slag af Tugtelsens Stok, som HERREN lader falde på Assur, er til Paukers og Citres Klang; med Svingnings Kampe kæmper han mod det.
Kowane bugun da Ubangiji zai yi musu da bulalarsa na hukunci zai zama kiɗi ga ganguna da garaya, yayinda yake yaƙi da su da naushin hannunsa.
33 Thi for længst står et Alter rede mon det og er rejst for Molok? han gjorde dets Ildfang dybt og bredt, bragte Ild og Ved i Mængde; HERRENs Ånde sætter det i Brand som en Strøm af Svovl.
An riga an shirya wurin ƙonawa; an shirya shi saboda sarki. An haƙa ramin wutarsa da zurfi da kuma fāɗi, da isashen wuta da itacen wuta; numfashin Ubangiji, yana kamar kibiritu mai ƙuna, da aka sa masa wuta.

< Esajas 30 >