< Hoseas 6 >

1 "Kom, vi vil tilbage til HERREN! Han sønderrev, han vil og læge, han slog os, vil også forbinde.
“Ku zo, mu koma ga Ubangiji. Ya yayyage mu kucu-kucu amma zai warkar da mu; ya ji mana ciwo amma zai daure mana miyakunmu.
2 Om to Dage gør han os levende, rejser os op den tredje; da lever vi for hans Åsyn.
Bayan kwana biyu zai rayar da mu, a rana ta uku zai tashe mu, don mu rayu a gabansa.
3 Så lad os da kende, jage efter at kende HERREN! Som Morgenrøden er hans Opgang vis. Da kommer han til os som Regn, som Vårregn, der væder Jorden."
Bari mu yarda da Ubangiji; bari mu nace gaba don mu yarda da shi. Muddin rana tana fitowa, zai bayyana; zai zo mana kamar ruwan bazara, kamar ruwan saman farko da yake jiƙe ƙasa.”
4 Hvor kan jeg hjælpe dig, Efraim, hvor kan jeg hjælpe dig, Juda? Eders Kærlighed er Morgentåge, Dug, som årle svinder!
“Me zan yi da kai Efraim? Me zan yi da kai Yahuda? Ƙaunarku tana kamar hazon safiya, kamar raɓar safiya da takan ɓace.
5 Thi hugged jeg løs ved Profeter, dræbte med Ord af min Mund, min Ret stråler frem som Lys:
Saboda haka na yayyaga ku kucu-kucu tare da annabawana, na kashe ku da kalmomin bakina; hukuntaina sun haskaka kamar walƙiya a kanku.
6 Ej Slagtoffer Kærlighed vil jeg, ej Brændofre Kendskab til Gud!
Gama jinƙai nake bukata, ba hadaya ba, ku kuma san Allah a maimakon hadayun ƙonawa.
7 De bryder Pagten i Adam er mig utro der;
Kamar Adamu, sun tā da alkawari, sun yi mini rashin aminci a can.
8 Gilead er Udådsmænds By, den er sølet i Blod.
Gileyad birni ce ta mugayen mutane, da tabon alamun jini.
9 Som en Stimandsflok er Præsternes Flok, de myrder på Vejen til Sikem gør Niddingsværk.
Kamar yadda mafasa sukan yi fakon mutum, haka ƙungiyoyin firistoci suke; suna kisa a hanya zuwa Shekem, suna aikata laifofi bankunya.
10 Grufulde Ting har jeg set i Israels Hus, der har Efraim bolet, Israel blev uren.
Na ga wani abu mai bantsoro a gidan Isra’ila. A can Efraim ya miƙa wuya ga karuwanci Isra’ila kuma ta ƙazantu.
11 Juda, også for dig er der fastsat en Høst, når jeg vender mit Folks Skæbne, når jeg læger Israel.
“Ku kuma, ya mutanen Yahuda, na shirya muku ranar girbi. “A duk sa’ad da zan mayar da dukiya wa mutanena,

< Hoseas 6 >