< 1 Mosebog 32 >

1 men Jakob fortsatte sin Rejse. Og Guds Engle mødte ham;
Yaƙub shi ma ya kama hanyarsa, sai mala’ikun Allah suka sadu da shi.
2 og da Jakob så dem, sagde han: "Her er Guds Lejr!" derfor kaldte han Stedet Mahanajim.
Sa’ad da Yaƙub ya gan su sai ya ce, “Wannan sansanin Allah ne!” Saboda haka ya kira wannan wuri Mahanayim.
3 Derpå sendte Jakob Sendebud i Forvejen til sin Broder Esau i Se'irs Land på Edoms Højslette,
Sai Yaƙub ya aiki manzanni su sha gabansa zuwa wurin ɗan’uwansa Isuwa a ƙasar Seyir, a ƙauyen Edom.
4 og han bød dem: "Sig til min Herre Esau: Din Træl Jakob lader dig vide, at jeg har levet som Gæst hos Laban og boet der indtil nu;
Ya umarce su, “Ga abin da za ku faɗa wa maigidana Isuwa, ‘Bawanka Yaƙub ya ce, na yi zama tare da Laban na kuwa kasance a can sai yanzu.
5 jeg har samlet mig Okser, Æsler og Småkvæg, Trælle og Trælkvinder; og nu sender jeg Bud til min Herre med Efterretning herom i Håb om at finde Nåde for dine Øjne!"
Ina da shanu da jakuna, tumaki da awaki, bayi maza da mata. Yanzu ina aika da wannan saƙo zuwa ga ranka yă daɗe, don in sami tagomashi a idanunka.’”
6 Men Sendebudene kom tilbage til Jakob og meldte: "Vi kom til din Broder Esau, og nu drager han dig i Møde med 400 Mand!"
Sa’ad da manzannin suka komo wurin Yaƙub, suka ce, “Mun tafi wurin ɗan’uwanka Isuwa, yanzu kuwa yana zuwa ya sadu da kai, da kuma mutum ɗari huɗu tare da shi.”
7 Da blev Jakob såre forfærdet, og i sin Angst delte han sine Folk, Småkvæget, Hornkvæget og Kamelerne i to Lejre,
Da tsoro mai yawa da kuma damuwa, Yaƙub ya rarraba mutanen da suke tare da shi ƙungiyoyi biyu, haka ma garkunan tumaki da awaki, da garkunan shanu da raƙuma.
8 idet han tænkte: "Hvis Esau møder den ene Lejr og slår den, kan dog den anden slippe bort."
Ya yi tunani, “In Isuwa ya zo ya fāɗa wa ƙungiya ɗaya, sai ƙungiya ɗayan da ta ragu ta tsira.”
9 Derpå bad Jakob: "Min Fader Abrahams og min Fader Isaks Gud, HERRE, du, som sagde til mig: Vend tilbage til dit Land og din Hjemstavn, så vil jeg gøre vel imod dig!
Sa’an nan Yaƙub ya yi addu’a, “Ya Allah na mahaifina Ibrahim, Allah na mahaifina Ishaku. Ya Ubangiji kai da ka ce mini, ‘Koma ƙasarka zuwa wurin danginka, zan kuma sa ka yi albarka.’
10 Jeg er for ringe til al den Miskundhed og Trofasthed, du har udvist mod din Tjener; thi med min Stav gik jeg over Jordan der, og nu er jeg blevet til to Lejre;
Ban cancanci dukan alheri da amincin da ka nuna wa bawanka ba. Da sanda kaɗai nake sa’ad da na ƙetare wannan Urdun, amma ga shi yanzu na zama ƙungiyoyi biyu.
11 frels mig fra min Broder Esaus Hånd, thi jeg frygter for, at han skal komme og slå mig, både Moder og Børn!
Ka cece ni, ina roƙonka daga hannun ɗan’uwana Isuwa, gama ina tsoro zai zo yă fāɗa mini, yă karkashe mu duka,’ya’ya da iyaye.
12 Du har jo selv sagt, at du vil gøre vel imod mig og gøre mit Afkom som Havets Sand, der ikke kan tælles for Mængde!"
Amma ka riga ka faɗa, ‘Tabbatacce zan sa ka yi albarka. Zan kuma sa zuriyarka su zama kamar yashin teku da ba a iya ƙirgawa.’”
13 Og han blev der om Natten. Af hvad han havde, udtog han så en Gave til sin Broder Esau,
Ya kwana a can, daga cikin abin da yake tare da shi kuwa, ya zaɓi kyauta domin ɗan’uwansa Isuwa,
14 200 Geder og 20 Bukke, 200 Får og 20 Vædre,
awaki ɗari biyu da bunsurai ashirin, tumaki ɗari biyu da raguna ashirin,
15 34 diegivende Kamelhopper med deres Føl, 40 Køer og 10 Tyre, 20 Aseninder og 10 Æselhingste;
raƙuma mata talatin tare da ƙananansu, shanu arba’in da bijimai goma, jakuna mata ashirin da kuma jakuna maza goma.
16 han delte dem i flere Hjorde og overlod sine Trælle dem, idet han sagde til dem: "Gå i Forvejen og lad en Plads åben mellem Hjordene!"
Ya sa su a ƙarƙashin kulawar bayinsa, kowane kashin garke ya kasance a ware. Ya ce wa bayinsa, “Ku sha gabana, ku kuma ba da rata tsakanin garke da garke.”
17 Og han bød den første: "Når min Broder Esau møder dig og spørger, hvem du tilhører, hvor du skal hen, og hvem din Drift tilhører,
Ya umarci wanda yake jagorar ya ce, “Sa’ad da ɗan’uwana Isuwa ya sadu da ku ya kuma yi tambaya, ‘Ku na wane ne, ina za ku, kuma wane ne mai dukan dabbobin nan da suke gabanku?’
18 skal du svare: Den tilhører din Træl Jakob; det er en Gave. han sender min Herre Esau; selv kommer han bagefter!"
Sai ku ce, ‘Na bawanka Yaƙub ne. Kyauta ce wa maigidana Isuwa, yana kuma tafe a bayanmu.’”
19 Og han bød den anden og den tredje og alle de andre, der fulgte med Hjordene, at sige det samme til Esau, når de traf ham:
Yaƙub ya kuma umarci na biyu da na uku da kuma dukan waɗansu da suka bi garkunan, “Sai ku faɗa irin abu guda ga Isuwa sa’ad da kuka sadu da shi.
20 "Din Træl Jakob kommer selv bagefter!" Thi han tænkte: "Jeg vil søge at forsone ham ved den Gave. der drager foran, og først bagefter vil jeg træde frem for ham; måske han da tager venligt imod mig!"
Ku kuma tabbata kun ce, ‘Bawanka Yaƙub yana tafe a bayanmu.’” Gama Yaƙub ya yi tunani cewa, “Zan kwantar da ran Isuwa da waɗannan kyautai, kafin mu sadu fuska da fuska, wataƙila yă karɓe shi.”
21 Så drog Gaven i Forvejen, medens han selv blev i Lejren om Natten.
Saboda haka kyautai Yaƙub suka sha gabansa, amma shi kansa ya kwana a sansani.
22 Samme Nat tog han sine to Hustruer, sine to Trælkvinder og sine elleve Børn og gik over Jakobs Vadested;
A wannan dare Yaƙub ya tashi ya ɗauki matansa biyu, da matan nan biyu masu hidima da’ya’yansa goma sha ɗaya ya haye rafin Yabbok.
23 han tog dem og bragte dem over Bækken; ligeledes bragte han alt. hvad han ejede, over.
Bayan ya sa suka haye rafin, haka ma ya tura dukan mallakarsa zuwa hayen.
24 Men selv blev Jakob alene tilbage. Da var der en, som brødes, med ham til Morgengry;
Saboda haka sai aka bar Yaƙub shi kaɗai. Sai ga wani mutum ya zo ya yi kokawa da shi har wayewar gari.
25 og da han så, at han ikke kunde få Bugt med ham, gav han ham et Slag på Hofteskålen; og Jakobs Hofteskål gik af Led, da han brødes med ham.
Da mutumin ya ga cewa bai fi ƙarfin Yaƙub ba, sai ya bugi kwarin ƙashin cinyar Yaƙub, sai gaɓar ƙashin cinyarsa ya goce, a sa’ad da yake kokawa da mutumin.
26 Da sagde han: "Slip mig, thi Morgenen gryr!" Men han svarede: "Jeg slipper dig ikke, uden du velsigner mig!"
Sa’an nan mutumin ya ce, “Bar ni in tafi, gama gari ya waye.” Amma Yaƙub ya amsa ya ce, “Ba zan bar ka ka tafi ba, sai ka sa mini albarka.”
27 Så spurgte han: "Hvad er dit Navn?" Han svarede: "Jakob!"
Mutumin ya tambaye shi ya ce, “Mene ne sunanka?” Yaƙub ya amsa ya ce, “Yaƙub.”
28 Men han sagde: "Dit Navn skal ikke mere være Jakob, men Israel; thi du har kæmpet med Gud og Mennesker og sejret!"
Sai mutumin ya ce, “Sunanka ba zai ƙara zama Yaƙub ba, amma Isra’ila, gama ka yi kokawa da Allah da mutane, ka kuwa yi rinjaye.”
29 Da sagde Jakob:"Sig mig dit Navn!" Men han svarede: "Hvorfor spørger du om mit Navn?" Og han velsignede ham der.
Yaƙub ya ce, “Ina roƙonka, faɗa mini sunanka.” Amma mutumin ya amsa ya ce, “Me ya sa kake tambayata sunana?” Sa’an nan ya albarkace shi.
30 Og Jakob kaldte Stedet Peniel, idet han sagde: "Jeg har skuet Gud Ansigt til Ansigt og har mit Liv frelst."
Saboda haka Yaƙub ya kira wurin Feniyel, yana cewa, “Domin na ga Allah fuska da fuska, duk da haka aka bar ni da rai.”
31 Og Solen stod op, da han drog forbi Penuel, og da haltede han på Hoften.
Rana ta yi sama a sa’ad da ya wuce Fenuwel yana kuma ɗingishi saboda ƙashin cinyarsa.
32 Derfor undlader Israeliterne endnu den Dag i Dag at spise Hoftenerven, der ligger over Hofteskålen, thi han gav Jakob et Slag på Hofteskålen, på Hoftenerven.
Wannan ya sa har wa yau Isra’ilawa ba sa cin jijiyar ƙashin cinya wadda take a kwarin ƙashin cinya, domin an taɓa kwarin ƙashin cinyar Yaƙub kusa da jijiyar.

< 1 Mosebog 32 >