< 1 Mosebog 21 >

1 HERREN så til Sara, som han havde lovet, og HERREN gjorde ved Sara, som han havde sagt,
Ana nan sai Ubangiji ya nuna wa Saratu alheri kamar yadda ya ce, Ubangiji kuma ya yi wa Saratu abin da ya yi alkawari.
2 og hun undfangede og fødte Abraham en Søn i hans Alderdom, til den Tid Gud havde sagt ham.
Saratu ta yi ciki, ta kuma haifa wa Ibrahim ɗa a tsufansa; a daidai lokacin da Allah ya yi masa alkawari.
3 Abraham kaldte den Søn, han fik med Sara, Isak;
Ibrahim ya sa wa ɗan da Saratu ta haifa masa suna Ishaku.
4 og Abraham omskar sin Søn Isak, da han var otte Dage gammel, således som Gud havde pålagt ham.
Sa’ad da ɗansa Ishaku ya kai kwana takwas da haihuwa, sai Ibrahim ya yi masa kaciya, kamar yadda Allah ya umarce shi.
5 Abraham var 100 År gammel, da hans Søn Isak fødtes ham.
Ibrahim yana da shekara ɗari, sa’ad da aka haifa masa ɗansa Ishaku.
6 Da sagde Sara: "Gud ham beredt mig Latter; enhver, der hører det, vil le ad mig."
Saratu ta ce, “Allah ya sa na yi dariya, kuma duk wanda ya ji game da wannan, zai yi dariya tare da ni.”
7 Og hun sagde: "Hvem skulde have sagt Abraham, at Sara ammer Børn! Sandelig, jeg har født ham en Søn i hans Alderdom!"
Ta kuma ƙara da cewa, “Dā, wa zai iya ce wa Ibrahim, Saratu za tă yi renon yara? Duk da haka na haifar masa ɗa cikin tsufansa.”
8 Drengen voksede til og blev vænnet fra, og Abraham gjorde et stort Gæstebud, den dag Isak blev vænnet fra.
Yaron ya yi girma, aka kuma yaye shi, a ranar da aka yaye shi kuwa, Ibrahim ya yi babban biki.
9 Men da Sara så Ægypterinden Hagars Søn, som hun havde født Abraham, lege med hendes Søn Isak,
Amma Saratu ta ga cewa yaron da Hagar, mutuniyar Masar ta haifa wa Ibrahim yana wa ɗanta Ishaku gori,
10 sagde hun til Abraham: "Jag den Trælkvinde og hendes Søn bort, thi ikke skal denne Trælkvindes Søn arve sammen med min Søn, med Isak!"
sai ta ce wa Ibrahim, “Ka kori baiwan nan tare da ɗanta, saboda ɗan baiwan nan ba zai taɓa raba gādo da ɗana Ishaku ba.”
11 Derover blev Abraham såre ilde til Mode for sin Søns Skyld;
Al’amarin ya ɓata wa Ibrahim rai sosai domin zancen ya shafi ɗansa.
12 men Gud sagde til Abraham: "Vær ikke ilde til Mode over Drengen og din Trælkvinde, men adlyd Sara i alt, hvad hun siger dig, thi efter Isak skal dit Afkom nævnes;
Amma Allah ya ce wa Ibrahim, “Kada hankalinka yă tashi game da yaron nan da kuma baiwarka. Ka saurari duk abin da Saratu ta faɗa maka, saboda ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.
13 men også Trælkvindens Søn vil jeg gøre til et stort Folk; han er jo dit Afkom!"
Zan ba ɗan baiwan nan al’umma shi ma, domin shi zuriyarka ne.”
14 Tidligt næste Morgen tog da Abraham Brød og en Sæk Vand og gav Hagar det, og Drengen satte han på hendes Skulder, hvorpå han sendte hende bort. Som hun nu vandrede af Sted, for hun vild i Be'ersjebas Ørken,
Kashegari da sassafe sai Ibrahim ya ɗauki abinci da salkar ruwa, ya ba wa Hagar. Ya ɗora su a kafaɗunta, sa’an nan ya sallame ta da yaron. Ta kama hanyarta ta kuma yi ta yawo a cikin jejin Beyersheba.
15 og Vandet slap op i hendes Sæk; da lagde hun Drengen hen under en af Buskene
Sa’ad da ruwan da yake cikin salkan ya ƙare, sai ta ajiye yaron a ƙarƙashin wani ƙaramin itace.
16 og gik hen og satte sig i omtrent et Pileskuds Afstand derfra, idet hun sagde ved sig selv: "Jeg kan ikke udholde at se Drengen dø!" Og således sad hun, medens Drengen græd højt.
Sai ta tafi, ta zauna ɗan nesa da yaron, misalin nisan harbin baka, gama ta yi tunani ta ce, “Ba zan iya kallon yaron yana mutuwa ba.” Da ta zauna nesa da yaron, sai ta fara kuka.
17 Da hørte Gud Drengens Gråd, og Guds Engel råbte til Hagar fra Himmelen og sagde til hende: "Hvad fattes dig, Hagar? Frygt ikke, thi Gud har hørt Drengens Røst der, hvor, han ligger;
Allah kuwa ya ji yaron yana kuka, sai mala’ikan Allah ya kira Hagar daga sama ya ce mata, “Mene ne damuwarki, Hagar? Kada ki ji tsoro, Allah ya ji yaron yana kuka yayinda yake kwance a can.
18 rejs dig, hjælp Drengen op og tag ham ved Hånden, thi jeg vil gøre ham til et stort Folk!"
Ki ɗaga yaron ki riƙe shi a hannu, gama zan mai da shi al’umma mai girma.”
19 Da åbnede Gud hendes Øjne, så hun fik Øje på en Brønd med Vand; og hun gik hen og fyldte Sækken med Vand og gav Drengen at drikke.
Sa’an nan Allah ya buɗe idanunta ta ga wata rijiyar ruwa. Don haka sai ta tafi ta cika salkan da ruwa, ta kuma ba wa yaron ruwa ya sha.
20 Og Gud var med Drengen, og han voksede til; og han bosatte sig i Ørkenen og blev Bueskytte.
Allah ya kasance da yaron, yayinda yake girma. Ya yi zama a jeji, ya kuma zama maharbi.
21 Han boede i Parans Ørken, og hans Moder tog ham en Hustru fra Ægypten.
Yayinda yake zama a Jejin Faran, sai mahaifiyarsa ta samo masa mata daga Masar.
22 Ved den Tid sagde Abimelek og hans Hærfører Pikol til Abraham: "Gud er med dig i alt, hvad du tager dig for;
A lokacin nan Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka zo suka ce wa Ibrahim, “Allah yana tare da kai a ko mene ne kake yi.
23 tilsværg mig derfor her ved Gud, at du aldrig vil være troløs mod mig eller mine Efterkommere, men at du vil handle lige så venligt mod mig og det Land, du gæster, som jeg har handlet mod dig!"
Yanzu ka rantse mini a nan a gaban Allah cewa, ba za ka yaudare ni ko’ya’yana ko kuma zuriyata ba. Ka nuna mini alheri, kai da ƙasar da kake zama baƙunci kamar yadda na nuna maka.”
24 Da svarede Abraham: "Jeg vil sværge!"
Ibrahim ya ce, “Na rantse.”
25 Men Abraham krævede Abimelek til Regnskab for en Brønd, som Abimeleks Folk havde tilranet sig.
Sa’an nan Ibrahim ya kawo kuka ga Abimelek game da rijiyar ruwan da bayin Abimelek suka ƙwace.
26 Da svarede Abimelek: "Jeg ved intet om, hvem der har gjort det; hverken har du underrettet mig derom, ej heller har jeg hørt det før i Dag!"
Sai Abimelek ya ce, “Ban san wanda ya yi wannan ba. Ba ka faɗa mini ba, ban kuwa taɓa ji ba, sai yau.”
27 Da tog Abraham Småkvæg og Hornkvæg og gav Abimelek det, og derpå sluttede de Pagt med hinanden.
Sai Ibrahim ya kawo tumaki da shanu ya ba wa Abimelek, sai su biyun suka yi yarjejjeniya.
28 Men Abraham satte syv Lam til Side,
Ibrahim ya ware’yan raguna bakwai daga cikin garke,
29 og da Abimelek spurgte ham: "Hvad betyder de syv Lam, du der har sat til Side?"
sai Abimelek ya ce wa Ibrahim, “Mene ne ma’anar’yan raguna bakwai da ka keɓe?”
30 svarede han: "Jo, de syv Lam skal du modtage af min Hånd til Vidnesbyrd om, at jeg har gravet denne Brønd."
Ibrahim ya amsa ya ce, “Ka karɓi waɗannan’yan tumaki bakwai daga hannuna a matsayin shaida cewa ni ne na haƙa wannan rijiya.”
31 Derfor kaldte man dette Sted Be'ersjeba, thi der svor de hinanden Eder;
Saboda haka aka kira wurin Beyersheba, domin a nan ne su biyun suka yi rantsuwa.
32 og de sluttede Pagt ved Be'ersjeba. Så brød Abimelek og hans Hærfører Pikol op og vendte tilbage til Filisternes Land.
Bayan da aka yi yarjejjeniya a Beyersheba, sai Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka koma ƙasar Filistiyawa.
33 Men Abraham plantede en Tamarisk i Be'ersjeba og påkaldte der HERREN den evige Guds Navn.
Sai Ibrahim ya shuka itacen tsamiya a Beyersheba, a can kuma ya kira bisa sunan Ubangiji, Allah Madawwami.
34 Og Abraham boede en Tid lang; som fremmed i Filisternes Land.
Ibrahim kuwa ya zauna a ƙasar Filistiyawa na dogon lokaci.

< 1 Mosebog 21 >