< Prædikeren 1 >

1 Ord af Prædikeren, Davids Søn, Konge i Jerusalem.
Kalmomin Malami, ɗan Dawuda, Sarki a Urushalima.
2 Endeløs Tomhed, sagde Prædikeren, endeløs Tomhed, alt er Tomhed!
“Ba amfani! Ba amfani!” In ji Malami. “Gaba ɗaya ba amfani! Kome ba shi da amfani!”
3 Hvad Vinding har Mennesket af al den Flid, han gør sig under Solen?
Wace riba ce mutum yake samu daga wahalar da yake fama a duniya?
4 Slægt går, og Slægt kommer, men Jorden står til evig Tid.
Zamanai sukan zo zamanai su wuce, amma duniya tana nan har abada.
5 Sol står op, og Sol går ned og haster igen til sin Opgangs Sted.
Rana takan fito rana ta kuma fāɗi, ta kuma gaggauta zuwa inda takan fito.
6 Vinden går mod Syd og drejer mod Nord, den drejer atter og atter og vender tilbage til samme Kredsløb.
Iska takan hura zuwa kudu ta kuma juya zuwa arewa; tă yi ta kewayewa, tă yi ta koma inda take fitowa.
7 Alle Bække løber i Havet, men Havet bliver ikke fuldt; det Sted, til hvilket Bækkene løber, did bliver de ved at løbe.
Dukan rafuffuka sukan gangara zuwa teku, duk da haka teku ba ya cika. Daga inda rafuffukan suke fitowa, a can suke komawa kuma.
8 Alting slider sig træt; Mand hører ikke op med at tale, Øjet bliver ikke mæt af at se, Øret ej fuldt af at høre.
Dukan abubuwa suna kawo gajiya, gaban magana. Ido ba ya gaji da gani, haka ma kunne yă ƙoshi da ji.
9 Det, der kommer, er det, der var, det, der sker, er det, der skete; der er slet intet nyt under Solen.
Abin da ya taɓa kasancewa, zai sāke kasance, abin da aka yi za a sāke yi kuma; babu wani abu sabo a duniya.
10 Kommer der noget, om hvilket man siger: "Se, her er da noget nyt!"det har dog for længst været til i Tiderne forud for os
Akwai wani abin da za a ce, “Duba! Ga wani abu sabo”? Abin yana nan, tun dā can, ya kasance kafin lokacinmu.
11 Ej mindes de svundne Slægter, og de ny, som kommer engang, skal ej heller mindes af dem, som kommer senere hen.
Ba a tunawa da mutanen dā, haka su ma da ba a haifa ba tukuna waɗanda za su biyo bayansu ba za a tuna da su ba.
12 Jeg, Prædikeren, var Konge over Israel i Jerusalem.
Ni, Malami, sarki ne bisa Isra’ila a Urushalima.
13 Jeg vendte min Hu til at ransage og med Visdom udgranske alt, hvad der sker under Himmelen; det er et ondt Slid, som Gud har givet Menneskens Børn at slide med.
Na dauri aniyata in gwada don in bincika ta wurin hikima dukan abin da ake yi a duniya. Kaya mai nauyi ne Allah ya ɗora a kan mutane!
14 Jeg så alt, hvad der sker under Solen, og se, det er alt sammen Tomhed og Jag efter Vind.
Na ga dukan abubuwan da ake yi a duniya, dukansu ba su da amfani, naushin iska ne kawai.
15 Kroget kan ej blive lige, og halvt kan ej blive helt.
Abin da yake tanƙwararre ba zai miƙu ba; ba za a kuma iya ƙidaya abin da ba shi ba.
16 Jeg tænkte ved mig selv: "Se, jeg har vundet større og rigere Visdom end alle de, der før mig var over Jerusalem, og mit Hjerte har skuet Visdom og Kundskab i Fylde."
Na yi tunani a raina na ce, “Duba, na yi girma, na kuma ƙaru da hikima fiye da duk wanda ya taɓa mulki a bisa Urushalima kafin ni; na ɗanɗana hikima mai yawa da kuma ilimi.”
17 Jeg vendte min Hu til at fatte, hvad der er Visdom og Kundskab, og hvad der er Dårskab og Tåbelighed; jeg skønnede, at også det er Jag efter Vind.
Sa’an nan na ɗaura aniyata ga fahimtar hikima, in kuma san bambanci tsakanin hauka da wauta, amma na koyi cewa wannan ma, naushin iska ne kawai.
18 Thi megen Visdom megen Græmmelse, øget Kundskab øget Smerte.
Gama yawan hikima yakan kawo yawan baƙin ciki; yawan sani, yawan ɓacin rai.

< Prædikeren 1 >