< 5 Mosebog 1 >

1 Dette er de Ord, Moses talte til hele Israel hinsides Jordan i Ørkenen, i Arabalavningen, lige over for Suf, mellem Paran og Tofel, Laban, Hazerot og Di Zahab,
Waɗannan su ne kalmomin da Musa ya yi wa dukan Isra’ila, a hamada gabas da Urdun, wato, Araba, ɗaura da Suf, tsakanin Faran da Tofel, Laban, Hazerot da Dizahab.
2 elleve Dagsrejser fra Horeb, regnede over Seirs Bjerge til Kadesj Barnea.
(Yakan ɗauki kwana goma sha ɗaya daga Horeb zuwa Kadesh Barneya ta hanyar Dutsen Seyir.)
3 I det fyrretyvende År på den første Dag i den elevte Måned kundgjorde Moses Israelitterne alt, hvad HERREN havde pålagt ham angående dem,
A shekara ta arba’in, a rana ta fari ga wata na goma sha ɗaya, Musa ya yi shela ga Isra’ilawa game da dukan abin da Ubangiji ya umarta shi game da su.
4 efter at han havde slået Amoriterkongen Sihon, der boede i Hesjbon, og Kong Og af Basan, der boede i Asjtarot og Edrei.
Wannan ya faru bayan ya ci Sihon sarkin Amoriyawa wanda ya yi mulki a Heshbon da yaƙi. A Edireyi kuma ya ci Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot da yaƙi.
5 Hinsides Jordan i Moabs Land tog Moses sig for at fremsætte følgende Lovudlægning:
Gabas da iyakar Mowab, Musa ya fara bayyana wannan doka, yana cewa,
6 HERREN vor Gud talede til os ved Horeb og sagde: "I har nu længe nok opholdt eder ved Bjerget her;
Ubangiji Allahnmu ya faɗa mana a Horeb cewa, “Daɗewarku a wannan dutse ya isa haka.
7 bryd derfor op og drag til Amoriternes Bjerge og til alle deres Naboer i Arabalavningen, på Bjergene, i Lavlandet, i Sydlandet og ved Kysten, til Kana'anæernes Land og Libanon, lige til den store Flod, Eufratfloden.
Ku tashi, ku ci gaba zuwa ƙasar tudun Amoriyawa; ku tafi wurin dukan maƙwabta a cikin Araba, a cikin duwatsu, a gindin yammancin tuddai, a Negeb da kuma a ta kwaruruka, da ƙasar Kan’aniyawa da kuma zuwa Lebanon, har zuwa babban kogi, wato, Yuferites.
8 Se, jeg giver Landet i eders Magt; drag derind og tag det Land i Besiddelse, som jeg tilsvor eders Fædre, Abraham, Isak og Jakob, at ville give dem og deres Afkom efter dem."
Duba na riga na ba ku wannan ƙasa. Ku shiga ku mallaki ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninku, ga Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub, da kuma ga zuriyarsu bayansu.”
9 Dengang talte jeg til eder og sagde: "Jeg kan ikke ene bære eder.
A wancan lokaci na faɗa muku cewa, “Ku kaya ne masu nauyi da ni kaɗai ba zan iya ɗauka ba.
10 HERREN eders Gud har gjort eder talrige, og se, I er nu så mange som Stjernerne på Himmelen;
Ubangiji Allahnku ya ƙara yawanku har yau kuka zama da yawa kamar taurari a sarari.
11 måtte kun HERREN, eders Fædres Gud, gøre eder tusinde Gange så talrige endnu og velsigne eder, som han har forjættet eder;
Bari Ubangiji, Allahn kakanninku yă ƙara yawanku sau dubu, yă kuma albarkace ku yadda ya yi alkawari!
12 men hvorledes skal jeg ene kunne bære hele Besværet og Arbejdet med eder og eders Stridigheder?
Amma yaya zan ɗauka dukan damuwoyinku da nawayarku da kuma faɗace-faɗacenku duka ni kaɗai?
13 Sørg derfor for at finde nogle kloge, forstandige. og erfarne Mænd i hver Stamme, som jeg kan sætte i Spidsen for eder!"
Ku zaɓi waɗansu masu hikima, masu ganewa, da kuma mutanen da ake girmama daga kowace kabilarku, zan kuma sa su a kanku.”
14 Dertil svarede I og sagde: "Det Forslag, du har fremsat, er godt!"
Kuka amsa mini, kuka ce, “Abin da ka ce za ka yi, yana da kyau.”
15 Derfor tog jeg Overhovederne for eders Stammer, kloge og erfarne Mænd, og satte dem i Spidsen for eder som Øverste over tusinde, hundrede, halvtredsindstyve eller ti og som Tilsynsmænd over eders Stammer.
Saboda haka na ɗauko shugabannin kabilanku masu hikima, waɗanda suka saba da ma’amala da jama’a, na sa su shugabanni a gabanku, waɗansu suka zama shugabanni a kan dubu-dubu, waɗansu a kan ɗari-ɗari, waɗansu a kan hamsin-hamsin, waɗansu kuma a kan goma-goma. Na sa su zama shugabanni a kabilanku.
16 Dengang gav jeg så eders Dommere det Påbud: "Hold Forhør, når der er Stridigheder mellem eders Landsmænd, og døm retfærdigt, når en Mand har en Sag, enten det er med en Landsmand eller med en, der bor som fremmed hos ham;
Na kuma umarci alƙalanku a wancan lokaci, na ce, “Ku yi adalci cikin shari’a tsakanin’yan’uwanku, ko damuwar tana tsakanin’yan’uwa Isra’ilawa ne, ko kuwa tsakanin Isra’ilawa da baƙin da suke zaune a cikinku.
17 vis ingen Personsanseelse for Retten; hør på den ringeste som på den største og frygt ikke for nogen; thi Dommen er Guds! Men Sager, som er eder for vanskelige, skal I forebringe mig, så skal jeg holde Forhør i dem!"
Kada ku nuna sonkai a cikin hukuncinku, ku saurari kowane ɓangare, babba da ƙarami, kada ku ji tsoron wani, gama hukunci na Allah ne. Ku kawo kowane batun da ya sha ƙarfinku, zan kuwa saurare shi.”
18 Og dengang gav jeg eder så Pålæg om alt, hvad I skulde gøre.
A wancan lokacin kuwa na faɗa muku dukan abin da ya kamata ku yi.
19 Derpå brød vi op fra Horeb og drog gennem hele denne store, grufulde Ørken, som I selv har set, i Retning af Amoriternes Bjerge, således som HERREN vor Gud havde pålagt os. Og vi kom til Kadesj Barnea.
Sa’an nan, muka kama hanya daga Horeb muka ratsa wajen ƙasar tudun Amoriyawa ta dukan hamadarta mai fāɗi, da kuma mai bantsoron da kuka gani, muka kuma kai Kadesh Barneya yadda Ubangiji, Allahnmu ya umarce mu.
20 Da sagde jeg til eder: "I er nu kommet til Amoriternes Bjerge, som HERREN vor Gud vil give os.
Sai na ce muku, “Kun iso ƙasar tudun Amoriyawa, wadda Ubangiji, Allahnmu yake ba mu.
21 Se, HERREN din Gud har givet Landet i din Magt, drag derfor op og tag det i Besiddelse, således som HERREN, dine Fædres Gud, har sagt til dig. Frygt ikke, men vær uforsagt!"
Duba, Ubangiji Allahnku ya ba ku ƙasar. Ku haura ku mallake ta yadda Ubangiji Allahn kakanninku ya faɗa muku. Kada ku ji tsoro, kada ku fid da zuciya.”
22 Da kom I alle hen til mig og sagde: "Lad os sende nogle Mænd i forvejen til at udspejde Landet for os og bringe os Underretning om den Vej, vi skal drage op ad, og om de Byer, vi kommer til!"
Sai dukanku kuka zo wurina kuka ce, “Bari mu aiki mutane su yi gaba su leƙi mana asirin ƙasar, su kuma kawo mana labari game da hanyar da za mu bi, da kuma biranen da za mu shiga.”
23 Jeg billigede det og udtog tolv Mænd iblandt eder, en af hver Stamme.
Ra’ayin nan naku ya yi mini kyau, saboda haka na zaɓe ku goma sha biyu, mutum guda daga kowace kabila.
24 De begav sig på Vej og drog op i Bjergene og kom til Esjkoldalen og udspejdede den;
Suka tafi, suka haura zuwa ƙasar tudu, suka kai Kwarin Eshkol, suka leƙo asirin ƙasar.
25 og de tog nogle af Landets Frugter med og bragte dem ned til os, og de meldte os tilbage: "Det er et herligt Land, HERREN vor Gud vil give os!"
Suka ɗebi’ya’yan itatuwan ƙasar, suka sauko mana da su, suka kuma ba da labari cewa, “Ƙasar da Ubangiji Allahnmu yake ba mu, kyakkyawa ce.”
26 Men I vilde ikke drage op, I var genstridige mod HERREN eders Guds Befaling.
Amma ba ku yi niyya ku haura ba, kuka yi tawaye gāba da umarnin Ubangiji Allahnku.
27 I knurrede i eders Telte og sagde: "Af Had til os førte HERREN os ud af Ægypten for at give os i Amoriternes Hånd og lade os gå til Grunde!
Kuka yi gunaguni a cikin tentunanku, kuna cewa, “Ubangiji ya ƙi mu; shi ya sa ya fitar da mu daga Masar don yă ba da mu ga hannuwan Amoriyawa su hallaka mu.
28 Hvor er det dog, vi skal hen? Vore Brødre tog Modet fra os, da de sagde: Det er et Folk, der er større og højere end vi, og der er store Byer med himmelhøje Fæstningsværker, ja, vi så endog Efterkommere af Anakiterne der!"
Ina za mu?’Yan’uwanmu suka sa muka fid da zuciya. Suka ce, ‘Mutanen sun fi mu ƙarfi, sun kuma fi mu tsayi; biranen manya ne, da katanga har sama. Mun ma ga Anakawa a can.’”
29 Men jeg sagde til eder: "Lad eder ikke skræmme og frygt ikke for dem!
Sai na ce muku, “Kada ku firgita; kada ku ji tsoronsu.
30 HERREN eders Gud, der vandrer foran eder, vil selv stride for eder, som I så, han gjorde det for eder i Ægypten
Ubangiji Allahnku yana a gabanku, zai yi yaƙi saboda ku, kamar yadda ya yi a kan idanunku a Masar,
31 og i Ørkenen, hvor du så, at HERREN din Gud bar dig, som en Mand bærer sin Søn, hele den Vej I har vandret, lige til I nåede hertil!"
da kuma a cikin hamada. A can ma kun ga yadda Ubangiji Allahnku ya riƙe ku ko’ina da kuka tafi, kamar yadda mahaifi yakan riƙe ɗansa, sai da kuka kai wannan wuri.”
32 Men alligevel troede I ikke på HERREN eders Gud,
Duk da haka, ba ku amince da Ubangiji Allahnku ba,
33 skønt han vandrede foran eder på Vejen for at udsøge Lejrpladser til eder, om Natten i Ilden, for at I kunde se, hvor I skulde gå, og om dagen i Skyen.
shi da ya sha gabanku a tafiyarku, cikin wuta da dad dare da kuma girgije da rana, don yă nemi wurare domin ku kafa sansani, don kuma yă nuna muku hanyar da za ku bi.
34 Men da HERREN hørte eders Ord, blev han vred og svor:
Da Ubangiji ya ji abin da kuka faɗa, sai ya husata, ya kuma yi rantsuwa ya ce,
35 "Ikke en eneste af disse Mænd, af denne onde Slægt, skal få det herlige Land at se, som jeg svor at ville give eders Fædre,
“Babu wani a cikin wannan muguwar tsara da zai ga ƙasa mai kyau da na rantse zan ba wa kakanninku,
36 undtagen Kaleb, Jefunnes Søn; han alene skal få det at se, og ham og hans Børn vil jeg give det Land, han har betrådt, fordi han har vist HERREN fuld Lydighed!"
sai dai Kaleb ɗan Yefunne. Zai gan ta, zan ba shi duk ƙasar da tafin ƙafarsa ta taka, shi da zuriyarsa, gama ya bi Ubangiji da zuciya ɗaya.”
37 Også på mig blev HERREN vred for eders Skyld, og han sagde: "Heller ikke du skal komme derind!
Saboda ku Ubangiji ya husata da ni, ya kuma ce, “Kai ma, ba za ka shiga ƙasar ba.
38 Josua, Nuns Søn, der står i din Tjeneste, han skal komme derind; sæt Mod i ham, thi han skal skaffe Israel det i Eje."
Amma mataimakinka, Yoshuwa ɗan Nun, zai shiga. Ka ƙarfafa shi gama shi ne zai jagoranci Isra’ila su gāje ta.
39 Og dets små Børn, som I sagde skulde blive til Bytte, eders Børn, som i Dag ikke kender Forskel på godt og ondt, de skal komme derind, dem vil jeg give det, og de skal tage det i Besiddelse.
Amma’ya’yanku ƙanana waɗanda ba su san mugunta ko nagarta ba, waɗanda kuke tsammani za a kwashe su ganima, su za su shiga ƙasar. Zan ba da ita gare su, za su kuwa mallake ta.
40 I selv derimod skal vende om og begive eder på Vej til Ørkenen i Retning af det røde Hav!"
Amma ku kam, sai ku juya, ku koma cikin hamada ta hanyar Jan Teku.”
41 Da svarede I og sagde til mig: "Vi har syndet imod HERREN! Vi vil drage op og kæmpe, som HERREN vor Gud har befalet os!" Og alle iførte I eder eders Våben og vilde i Letsindighed drage op i Bjergene.
Sai kuka amsa, kuka ce, “Mun yi zunubi ga Ubangiji. Za mu haura mu yi yaƙi yadda Ubangiji Allahnmu ya umarce mu.” Saboda haka kowannenku ya yi ɗamara da kayan yaƙinsa, kuka yi tsammani zai zama muku da sauƙi ku ci ƙasar tuddai da yaƙi.
42 Men HERREN sagde til mig: Sig til dem: Drag ikke op og indlad eder ikke i Kamp, thi jeg er ikke iblandt eder; gør I det, bliver I slået af eders Fjender!"
Amma Ubangiji ya ce mini, “In faɗa muku, ‘Kada ku fāɗa musu da yaƙi, gama ba zai kasance tare da ku ba. Idan kuka kuskura, abokan gābanku za su murƙushe ku.’”
43 Men da jeg sagde det til eder, adlød I ikke, men var genstridige mod HERRENs Bud og formastede eder til at drage op i Bjergene.
Sai na faɗa muku, amma ba ku saurara ba. Kuka yi tawaye ga umarnin Ubangiji, a cikin jahilcinku kuwa kuka taka, kuka haura cikin ƙasar tudu.
44 Da drog Amoriterne, der bor i Bjergene der, ud imod eder, og de forfulgte eder som Bier og slog eder fra Seir til Horma.
Amoriyawan da suke zama a waɗannan tuddai, suka fito kamar tarin ƙudan zuma gāba da ku, suka kore ku, suka fatattake ku daga Seyir har zuwa Horma.
45 Da I så kom tilbage, græd I for HERRENs Åsyn; men HERREN vilde ikke høre eder og låne eder Øre.
Kuka dawo, kuka yi kuka a gaban Ubangiji, amma bai kula da ku ba, balle yă saurare ku.
46 Så blev I hele den lange Tid i Kadesj.
Haka kuwa kuka zauna a Kadesh kwanaki masu yawa, kuka ci lokaci a can.

< 5 Mosebog 1 >