< Apostelenes gerninger 18 >

1 Derefter forlod Paulus Athen og kom til Korinth
Bayan haka sai Bulus ya tafi Antakiya daga nan, ya wuce Korinti.
2 Der traf han en Jøde ved Navn Akvila, født i Pontus, som nylig var kommen fra Italien med sin Hustru Priskilla, fordi Klaudius havde befalet, at alle Jøderne skulde forlade Rom. Til disse gik han.
A can ya sadu da wani Bayahude mai sunan Akila, dan kasar Buntus ne; bai dade da zuwa garin ba, daga Italiya ya zo da matarsa mai suna Balkisu, saboda Kalaudiyas ya ba da umarni dukan Yahudawa su bar Roma; sai Bulus ya je wurinsu.
3 Og efterdi han øvede det samme Håndværk, blev han hos dem og arbejdede; thi de vare Teltmagere af Håndværk.
Bulus ya zauna a gidansu don sana'arsu daya ce, wato, masu aikin Tanti ne.
4 Men han holdt Samtaler i Synagogen på hver Sabbat og overbeviste Jøder og Grækere.
Saboda haka Bulus na zuwa majami'a, yana yin nazari tare da su a kowace Asabaci. Yana kokari ya rinjayi Yahudawa da Helinawa.
5 Men da Silas og Timotheus kom ned fra Makedonien, var Paulus helt optagen af at tale og vidnede for Jøderne, at Jesus er Kristus.
Amma a lokacin da Sila da Timoti suka iso Makidoniya, Ruhu ya matsa Bulus ya shaida wa Yahudawa cewa Yesu Almasihu ne.
6 Men da de stode imod og spottede, rystede han Støvet af sine Klæder og sagde til dem: "Eders Blod komme over eders Hoved! Jeg er ren; herefter vil jeg gå til Hedningerne."
Lokacin da Yahudawa suka tayar masa suna zarginsa. Bulus ya kakkabe rigansa a gabansu yana cewa, “Alhakin jininku yana kanku; daga yanzu zan koma wurin al'ummai.”
7 Og han gik bort derfra og gik ind til en Mand ved Navn Justus, som frygtede Gud, og hvis Hus lå ved Siden af Synagogen.
Da ya bar wurinsu, ya tafi gidan Taitus Yustus mai wa Allah sujada. Gidansa na kusa da majami'a.
8 Men Synagogeforstanderen Krispus troede på Herren tillige med hele sit Hus, og mange af Korinthierne, som hørte til, troede og bleve døbte.
Kiristus shine shugaban majami'a, sai shi da dukan iyalin gidansa sun ba da gaskiya ga Ubangiji. Korantiyawa da yawa suka ji jawabin Bulus suka ba da gaskiya, aka yi masu Baftisma.
9 Men Herren sagde til Paulus i et Syn om Natten: "Frygt ikke, men tal og ti ikke,
Da dare Ubangiji ya ce wa Bulus a cikin wahayi, “Kada ka ji tsoro, amma ka yi magana kada kuma ka yi shuru.
10 eftersom jeg er med dig, og ingen skal lægge Hånd på dig for at gøre dig noget ondt; thi jeg har et talrigt Folk i denne By."
Gama ina tare da kai, ba wanda zai cutar da kai, gama ina da mutane anan garin.”
11 Og han slog sig ned der et År og seks Måneder og lærte Guds Ord iblandt dem.
Bulus ya zauna a nan tsawon shekara daya da wata shida, yana koyar masu da maganar Allah.
12 Men medens Gallio var Statholder i Akaja, stode Jøderne endrægtigt op imod Paulus og førte ham for Domstolen og sagde:
Amma da Galiyo ya samu zaman gwamnan Akaya, sai Yahudawa suka tayar wa Bulus har suka kai shi gaban dakalin shari'a.
13 "Denne overtaler Folk til en Gudsdyrkelse imod Loven."
Suna cewa, “Wannan mutumin yana kokarin rinjayar mutane su yi sujadar da ta saba wa dokarmu.”
14 Og da Paulus vilde oplade Munden, sagde Gallio til Jøderne: " Dersom det var nogen Uret eller Misgerning, I Jøder! vilde jeg, som billigt var, tålmodigt høre på eder.
Duk da haka kafin Bulus ya yi magana, Galiyo ya ce wa Yahudawa, “Ku Yahudawa in da karar ku ta wani babban laifi ce wanda ya aikata, da sai in hukunta.
15 Men er det Stridsspørgsmål om Lære og Navne og om den Lov, som I have, da ser selv dertil; thi jeg vil ikke være Dommer over disse Ting."
Amma tun da ya ke akan al'amurar, kalmomi ne, da ta sunaye da dokokin ku, ku je ku sasanta al'amuran ku.”
16 Og han drev dem bort fra Domstolen.
Galiyo ya kore su daga dakalin shari'a.
17 Men alle grebe Synagogeforstanderen Sosthenes og sloge ham lige for Domstolen; og Gallio brød sig ikke om noget af dette.
Saboda haka sai suka kama Sastanisu, suka yi masa duka sosai a gaban dakalin shari'a. Amma Galiyo bai damu da yadda suka karasa ba.
18 Men Paulus blev der endnu i mange dage; derefter tog han Afsked med Brødrene og sejlede bort til Syrien og med ham Priskilla og Akvila, efter at han havde ladet sit Hår klippe af i Kenkreæ; thi han havde et Løfte på sig.
Bulus kuwa, bayan ya zauna tare da su na wasu kwanaki masu yawa, ya bar 'yan'uwan zuwa Suriya ta jirgin ruwa, tare da Balkisu da Akila. Kafin ya bar tashar jiragen ruwa da ke a Sankuriya, ya tafi saboda ya aske kansa, domin ya dauki alkawarin Banazare.
19 Men de kom til Efesus; og der lod han hine blive tilbage; men han selv gik ind i Synagogen og samtalede med Jøderne.
Da suka iso Afisa, Bulus ya bar Balkisu da Akila anan. Shi kuwa ya shiga majami'ar Yahudawa yana nazari tare da su.
20 Men da de bade ham om at blive i længere Tid, samtykkede han ikke;
Da suka roki Bulus ya zauna da su na tsawon lokaci, bai yarda ba.
21 men han tog Afsked og sagde: " (Jeg må endelig holde denne forestående Højtid i Jerusalem; men) jeg vil atter vende tilbage til eder, om Gud vil." Og han sejlede ud fra Efesus
Ya kama hanyarsa ya bar su ya ce, “In Allah ya yardar mani zan dawo wurinku wata rana.” Sai ya shiga jirgin ruwa daga Afisa.
22 og landede i Kæsarea, drog op og hilste på Menigheden og drog så ned til Antiokia.
Daga saukar su a Kaisariya, sai ya haura zuwa Urushalima ya gai da iklisiya daga nan ya tafi Antakiya.
23 Og da han havde opholdt sig der nogen Tid, drog han bort og rejste fra Sted til Sted igennem det galatiske Land og Frygien og styrkede alle Disciplene.
Bayan ya zauna na dan lokaci a wurin, Bulus ya kama hanyarsa zuwa yakin Galatiya da Firjiya anan ya karfafa almajirai.
24 Men en Jøde ved Navn Apollos, født i Aleksandria, en veltalende Mand, som var stærk i Skrifterne, kom til Efesus.
A nan dai akwai wani Bayahude mai suna Afolos, dan asalin Iskandariya ne da haihuwa, ya zo Afisa. Shi masani ne a maganar Allah.
25 Denne var undervist om Herrens Vej, og brændende i Ånden talte og lærte han grundigt om Jesus, skønt han kun kendte Johannes's Dåb.
Afolos dai ya sami horo daga maganar Ubangiji. Shi mai kokari ne a ruhu, yana wa'azi da koyarwa daidai game da Yesu. Amma ya san da Baftismar Yahaya ne kadai.
26 Og han begyndte at tale frimodigt i Synagogen. Men da Priskilla og Akvila hørte ham, toge de ham til sig og udlagde ham Guds Vej nøjere.
Afolos ya fara wa'azinsa da gabagadi a cikin majami'a. Da Balkisu da Akila suka ji shi sai suka yi abokantaka da shi, suka kara bayyana masa game da labarin hanyar Allah mafi daidai.
27 Men da han vilde rejse videre til Akaja, skrev Brødrene til Disciplene og opmuntrede dem til at tage imod ham. Da han var kommen derhen, var han ved Guds Nåde de troende til megen Nytte;
Da ya so ya wuce zuwa cikin Akaya 'yan'uwa suka karfafa shi, sun rubuta wa almajiran da ke a Akaya, don su karbe shi da hannu biyu. Da ya iso wurinsu, ya kuwa karfafa 'yan'uwa da sun ba da gaskiya ta wurin alheri.
28 thi han gendrev Jøderne offentligt med stor Kraft og beviste ved Skrifterne, at Jesus er Kristus.
Afolos ya ba Yahudawa mamaki da irin ikon da yake da shi da gwanintarsa, yadda yake nunawa daga nassoshi cewa Yesu shine Almasihu.

< Apostelenes gerninger 18 >