< Anden Krønikebog 25 >

1 Amazja var fem og tyve År gammel, da han blev Konge, og han herskede ni og tyve År i Jerusalem. Hans Moder hed Jehoaddan og var fra Jerusalem.
Amaziya yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Yehoyaddin ce; ita daga Urushalima ne.
2 Han gjorde, hvad der var ret i HERRENs Øjne, dog ikke med et helt Hjerte.
Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, amma ba da dukan zuciyarsa ba.
3 Da han havde sikret sig Magten, lod han dem af sine Folk dræbe, der havde dræbt hans Fader Kongen,
Bayan sarauta ta kahu a ƙarƙashinsa, sai ya kashe hafsoshin da suka kashe mahaifinsa sarki.
4 men deres Børn lod han ikke ihjelslå, i Henhold til hvad der står skrevet i Moses's Lovbog, hvor HERREN påbyder: "Fædre skal ikke lide Døden for Børns Skyld, og Børn skal ikke lide Døden for Fædres Skyld. Men enhver skal lide Døden for sin egen Synd."
Duk da haka bai kashe’ya’yansu maza ba amma ya yi bisa ga abin da yake a rubuce a cikin Doka, a cikin Littafin Musa, inda Ubangiji ya umarta, “Ba za a kashe iyaye saboda’ya’yansu ba; ba kuwa za a kashe’ya’ya saboda iyayensu ba; kowa zai mutu saboda zunubansa ne.”
5 Amazja samlede Judæerne og opstillede dem efter Fædrenehuse under Tusind- og Hundredførerne, hele Juda og Benjamin, og da han mnønstrede dem fra Tyveårsalderen og opefter, fandt han, at de udgjorde 300.000 udvalgte Folk, øvede Krigere, der har Skjold og Spyd.
Amaziya ya tattara mutanen Yahuda ya kuma ba su aiki bisa ga iyalansu, ya ba da aiki ga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, a dukan Yahuda da Benyamin. Ya kuma tattara waɗanda suke’yan shekara ashirin da haihuwa ko fiye ya sami mutane dubu ɗari uku da suke a shirye don aikin soja, da suka isa riƙe māshi da garkuwa.
6 Dertil lejede han i Israel 100.000 dygtige Krigere for 100 Sølvtalenter.
Ya kuma ɗauko sojan haya jarumawa dubu ɗari ɗaya daga Isra’ila a kan talenti ɗari na azurfa.
7 Men en Guds Mand kom til ham og sagde: "Israels Hær må ikke følge dig, Konge, thi HERREN er ikke med Israel, ikke med nogen af Efraimiterne;
Amma mutumin Allah ya zo wurinsa ya ce, “Ya sarki, waɗannan runduna daga Isra’ila ba za su tafi tare da kai ba, gama Ubangiji ba ya tare da Isra’ila, ba ya nan da wani cikin mutanen Efraim.
8 og hvis du mener, at du kan vinde Styrke på den Måde, vil Gud bringe dig til Fald for Fjenden, thi hos Gud er der Kraft til at hjælpe og til at bringe til Fald!"
Ko da ma ya tafi ya yi faɗa da ƙwazo a cikin yaƙi, Allah zai tumɓuke shi a gaban abokan gāba, gama Allah yana da iko yă taimaka ko yă tumɓuke.”
9 Amazja spurgte den Guds Mand: "Hvad så med de 100 Sølvtalenter, jeg gav de israelitiske Krigsfolk?" Og den Guds Mand svarede: "HERREN kan give dig langt mere end det!"
Amaziya ya tambayi mutumin Allah ya ce, “Amma game da talenti ɗarin da na biya saboda waɗannan rundunonin Isra’ila fa?” Mutumin Allah ya amsa, “Ubangiji zai ba ka fiye da wannan.”
10 Da udskilte Amazja de Krigsfolk, der var kommet til ham fra Efraim, og lod dem drage hjem; men deres Vrede blussede heftigt op mod Juda, og de vendte hjem i fnysende Vrede.
Saboda haka Amaziya ya sallame rundunonin da suka zo daga Efraim, ya kuma mayar da su gida. Suka husata da Yahuda suka koma gida da fushi sosai.
11 Amazja tog nu Mod til sig og førte sine Krigere til Saltdalen og nedhuggede 10.000 af Se'iriterne;
Sa’an nan Amaziya ya yi ƙarfin hali ya jagoranci mayaƙansa zuwa Kwarin Gishiri, inda ya kashe mutanen Seyir dubu goma.
12 desuden tog Judæerne 10.000 levende til Fange; dem førte de op på Klippens Top og styrtede dem ned derfra, så de alle knustes.
Mayaƙan Yahuda suka kuma kama mutane dubu goma da rai, suka ɗauke su zuwa ƙwanƙolin dutsen, suka yi ta tunkuɗa su ƙasa suka yi kaca-kaca.
13 Men de Krigsfolk, Amazja havde sendt hjem, så de ikke kom til at følge ham i Krigen, faldt ind i Judas Byer fra Samaria til Bet-Horon, huggede 3.000 af Indbyggerne ned og gjorde stort Bytte.
Ana cikin haka, sai rundunar da Amaziya ya mai da su gida, waɗanda ba a bari suka tafi yaƙin ba, suka kai wa garuruwan Yahuda daga Samariya zuwa Bet-Horon hari. Suka kashe mutane dubu uku suka kwashe ganima mai yawan gaske.
14 Da Amazja kom hjem fra Sejren over Edomiterne, havde han Se'iriternes Guder med, og han opstillede dem som sine Guder, tilbad dem og tændte Offerild for dem.
Da Amaziya ya dawo daga kisan mutanen Edom, sai ya dawo da allolin mutanen Seyir. Ya kafa su a matsayin allolinsa, ya rusuna musu, ya kuma miƙa musu hadayun ƙonawa.
15 Da blussede HERRENs Vrede op mod Amazja, og han sendte en Profet til ham, og denne sagde til ham: "Hvorfor søger du dette Folks Guder, som ikke kunde frelse deres Folk af din Hånd?"
Fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan Amaziya, sai ya aiki wani annabi wurinsa wanda ya ce, “Me ya sa ka nemi shawarar allolin mutanen nan, waɗanda ba za su cece mutanensu daga hannunka ba?”
16 Men da han talte således, sagde Kongen til ham: "Har man gjort dig til Kongens Rådgiver? Hold inde, ellers bliver du slået ihjel!" Da holdt Profeten inde og sagde: "Jeg indser, at Gud har i Sinde at ødelægge dig, siden du bærer dig således ad og ikke hører mit Råd!"
Tun yana cikin magana, sai sarki ya ce masa, “Yaushe muka naɗa ka mai ba sarki shawara? Rufe mana baki! Me zai hana a kashe ka?” Sai annabin ya yi shiru, amma ya ce, “Na dai sani Allah ya riga ya shirya zai hallaka ka, saboda ka aikata wannan, ba ka kuma saurari shawarata ba.”
17 Efter at have overtænkt Sagen sendte Kong Amazja af Juda Bud til Jehus Søn Joahaz's Søn, Kong Joas af Israel, og lod sige: "Kom, lad os se hinanden under Øjne!"
Bayan Amaziya sarkin Yahuda ya nemi shawara mashawartansa, sai ya kalubalanci Yowash ɗan Yehoyahaz, ɗan Yehu, sarkin Isra’ila, “Zo mu gamu fuska da fuska.”
18 Men Kong Joas af Israel sendte Kong Amazja, af Juda det Svar: "Tidselen på Libanon sendte engang det Bud til Cederen på Libanon: Giv min Søn din Datter til Ægte! Men Libanons vilde Dyr løb hen over Tidselen og trampede den ned!
Amma Yowash sarkin Isra’ila ya amsa wa Amaziya sarkin Yahuda ya ce, “Wata ƙaya ce a Lebanon, ta aika da saƙo wa itacen al’ul na Lebanon cewa, ‘Ka ba ɗana’yarka aure.’ Sai wani naman jeji na Lebanon ya zo ya tattake ƙayar.
19 Du tænker: Se, jeg har slået Edom! Og det har gjort dig overmodig, så du vil vinde mere Ære. Bliv, hvor du er! Hvorfor vil du udfordre Ulykken og udsætte både dig selv og Juda for Fald?"
Ka ce wa kanka cewa ka ci Edom da yaƙi, yanzu kuwa kana fariya da ɗaga kai. Amma tsaya dai a gida! Me ya sa kake neman faɗa kana neman fāɗuwarka da ta Yahuda?”
20 Men Amazja vilde intet høre, thi Gud føjede det såledesfor at give dem til Pris, fordi de søgte Edoms Guder.
Amma Amaziya bai saurara ba gama Allah ya yi haka domin yă miƙa su ga Yehowash, domin sun nemi shawarar allolin Edom.
21 Så drog Kong Joas af Israel ud, og han og Kong Amazja af Juda så hinanden under Øjne ved Bet-Sjemesj i Juda;
Saboda haka Yowash sarkin Isra’ila ya kai yaƙi. Shi da Amaziya sarkin Yahuda suka fuskanci juna a Bet-Shemesh a Yahuda.
22 Juda blev slået af Israel, og de flygtede hver til sit.
Isra’ila ta fatattaki Yahuda, sai kowane mutum ya gudu zuwa gidansa.
23 Men Kong Joas af Israel tog Joahaz's Søn Joas's Søn, Kong Amazja af Juda, tifange ved Bet-Sjemesj og førte ham til Jerusalem. Derpå nedrev han Jerusalems Mur på en Strækning af 400 Alen, fra Efraimsporten til Hjørneporten;
Yehowash sarkin Isra’ila ya kama Amaziya sarkin Yahuda, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya a Bet-Shemesh. Sa’an nan Yehowash ya kawo shi Urushalima ya farfasa katangar Urushalima daga Ƙofar Efraim har zuwa Ƙofar Kusurwa, wani sashe mai tsawon ƙafa ɗari shida.
24 og han tog alt det Guld og Sølv og alle de Kar, der fandtes i Guds Hus hos Obed-Edom og i Skatkammeret i Kongens Palads; desuden tog han Gidsler og vendte så tilbage til Samaria.
Ya kwashe dukan zinariya da azurfa da dukan kayayyakin da aka samu a haikalin Allah waɗanda suke a ƙarƙashin kulawar Obed-Edom, da kaya masu daraja na gidan sarki, da waɗanda aka kamo cikin yaƙi, ya kawo Samariya.
25 Joas's Søn, Kong Amazja af Juda, levede endnu femten År, efter at Joahaz's Søn, Kong Joas at Israel, var død.
Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya rayu shekara goma sha biyar bayan mutuwar Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila.
26 Hvad der ellers er at fortælle om Amazja fra først til sidst, står optegnet i Bogen om Judas og Israels Konger.
Game da sauran ayyukan mulkin Amaziya, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
27 Men ved den Tid Amazja faldt fra HERREN, stiftedes der en Sammensværgelse mod ham i Jerusalem, og han flygtede til Lakisj, men der blev sendt Folk efter ham til Lakisj, og de dræbte ham der.
Sa’ad da Amaziya ya bar bin Ubangiji, aka shirya masa maƙarƙashiya a Urushalima, sai ya gudu zuwa Lakish, amma suka aiki mutane suka bi shi zuwa Lakish, a can suka kashe shi.
28 Så løftede man ham op på Heste og jordede ham hos hans Fædre i Davidsbyen.
Aka dawo da shi a kan doki, aka binne shi tare da kakanninsa a Birnin Yahuda.

< Anden Krønikebog 25 >