< 1 Samuel 2 >

1 Da bad Hanna og sagde: Mit Hjerte jubler over HERREN, mit Horn er løftet ved min Gud, min Mund vidt opladt mod mine Fjender, jeg glæder mig over din Frelse.
Sai Hannatu ta yi addu’a ta ce, “Zuciyata tana farin ciki a cikin Ubangiji; a cikin Ubangiji an sa ina jin daɗi ƙwarai. Na buɗe bakina na yi wa abokan gābana dariya. Kai! Ina murna domin ka cece ni!
2 Der er ingen Hellig som HERREN, nej, der er ingen uden dig, der er ingen Klippe som vor Gud
“Babu wani mai tsarki kamar Ubangiji babu wani, in ban da kai; babu wani dutse kamar Allahnmu.
3 Vær varsomme med eders store Ord, Frækhed undslippe ej eders Mund! Thi en vidende Gud er HERREN, og Gerninger vejes af ham.
“Ka daina maganganu na girman kai ka kuma daina faɗin kalmomin ɗaga kai; gama Ubangiji Allah ne masani daga gare shi kuma ana auna ayyuka.
4 Heltes Bue er brudt, men segnende omgjorder sig med Kraft;
“An kakkarya bakkuna masu yaƙi, amma su da ka raunana an ba su makaman ƙarfi.
5 mætte lader sig leje for Brød, men sultnes Slid hører op; den ufrugtbare føder syv, men den med de mange vansmægter.
Waɗanda a dā suna da abinci sosai; yanzu suna ƙodago saboda abinci, masu fama da yunwa kuwa sun daina jin yunwa. Ita da take bakararriya, ta haifi’ya’ya bakwai amma ita da tana da’ya’ya da yawa, ta zama mai baƙin ciki.
6 HERREN døder, gør levende, fører ned i Dødsriget og fører op; (Sheol h7585)
“Ubangiji ne ke kawo mutuwa, yă kuma rayar yana kai ga kabari, yă kuma tā da. (Sheol h7585)
7 HERREN gør fattig, gør rig, han nedbøjer
Ubangiji ne yakan aika da talauci da kuma dukiya; yakan ƙasƙantar yă kuma ɗaukaka.
8 han rejser ringe af Støvet, af Skarnet løfter han fattige for at bænke og give dem Ærespladsen. Thi HERRENs er Jordens Søjler, Jorderig bygged han på dem
Yakan tā da matalauci daga ƙura, yă kuma ɗaga mai bukata daga tarin toka; yă zaunar da su tare da’ya’yan sarki; yă kuma sa su gāji mulki na ɗaukaka. “Harsashin duniya na Ubangiji ne; a bisansu ne ya kafa duniya.
9 Han vogter sine frommes Skridt, men gudløse omkommer i Mørket; thi ingen vinder Sejr ved egen kraft.
Zai kiyaye ƙafafun masu tsarki, amma mugaye za su lalace cikin duhu. “Ba bisa ga ƙarfi mutum ba ne mutum ke nasara;
10 HERREN - hans Fjender forfærdes, den Højeste tordner i Himmelen, HERREN dømmer den vide Jord! Han skænker sin Konge Kraft, løfter sin Salvedes Horn!
waɗanda suke gāba da Ubangiji za su hallaka. Zai yi musu tsawa daga sama, Ubangiji zai hukunta dukan duniya. “Zai ba wa sarkinsa ƙarfi, yă kuma ɗaukaka shafaffensa.”
11 Så drog hun til Rama, men Drengen gjorde Tjeneste for HERREN under Præsten Elis Tilsyn.
Sa’an nan, Elkana ya koma gida a Rama amma yaron ya yi hidima a gaban Ubangiji a ƙarƙashin Eli firist.
12 Men Elis Sønner var Niddinger; de ænsede hverken HERREN
’Ya’yan Eli firist, mutane ne masu mugunta. Ba su ɗauki Ubangiji a bakin kome ba.
13 eller Præstens Ret over for Folket. Hver Gang en Mand bragte et Slagtoffer, kom Præstens Tjener, medens Kødet kogte, med en tregrenet Gaffel i Hånden
Al’ada ce ga firistoci da mutane cewa in wani ya miƙa hadaya, yayinda nama yake kan wuta, bawan firist zai zo da babban cokali mai yatsu,
14 og stak den ned i Karret, Krukken, Kedelen eller Gryden, og alt, hvad Gaffelen fik med op, tog Præsten for sin Del. Således bar de sig ad over for alle de Israelitter, som kom til Silo for at ofre der.
zai soka cokali mai yatsun a tukunyar, ko butar da ake dafan naman. Duk abin da cokali mai yatsun ya cako daga tukunyar, ya zama na firist. Haka aka yi ta yi wa Isra’ilawan da suka zo miƙa hadaya a Shilo.
15 Eller også kom Præstens Tjener, før de bragte Fedtet som Røgoffer, og sagde til Manden, som ofrede: "Giv Præsten Kød til at stege; han tager ikke mod kogt Kød af dig, kun råt!"
Tun ma kafin a ƙona kitse, bawan firist yakan zo yă ce wa mutumin da yake miƙa hadaya, “Ka ba wa firist nama domin yă gasa, ba zai karɓi dafaffen nama daga wurinka ba, sai ɗanye.”
16 Sagde Manden nu til ham: "Først må Fedtet bringes som Røgoffer, bagefter kan du tage så meget, du lyster!" svarede han: "Nej, giv mig det nu, ellers tager jeg det med Magt!"
In kuwa mutumin ya ce masa, “Bari kitse yă ƙone tukuna, sa’an nan ka ɗiba duk abin da kake so.” Sai bawan yă ce masa, “A’a, ka ba ni yanzu, in ka ƙi kuwa zan ɗiba ƙarfi da yaji.”
17 Og de unge Mænds Synd var såre stor for HERRENs Åsyn, idet de viste Ringeagt for HERRENs Offergaver.
Wannan zunubin samarin ya yi muni ƙwarai a gaban Ubangiji, domin sun wulaƙanta hadayar Ubangiji, ƙwarai da gaske.
18 Imidlertid gjorde Samuel Tjeneste for HERRENs Åsyn; og Drengen var iført en linned Efod.
Amma yaron nan Sama’ila, yana hidima a gaban Ubangiji yana sanye da efod na lilin.
19 Hans Moder lavede hvert År en lille Kappe til ham og bragte ham den, når hun drog op med sin Mand for at ofre det årlige Offer.
Kowace shekara mahaifiyarsa takan ɗinka’yar taguwa ta kai masa sa’ad da ita da mijinta suka je miƙa hadaya ta shekara.
20 Og Eli velsignede Elkana og hans Hustru og sagde: "HERREN give dig Afkom af denne Kvinde til Gengæld for ham, hun overlod HERREN!" Så gik de hjem igen.
Eli yakan sa wa Elkana da matarsa albarka, yă ce, Ubangiji yă ba ka waɗansu’ya’ya ta wurin matan nan, maimakon wanda ta roƙa daga Ubangiji, ta kuma ba da shi ga Ubangiji. Bayan haka sai su koma gida.
21 Og HERREN så til Hanna, og hun blev frugtsommelig og fødte tre Sønner og to Døtre. Men Drengen Samuel voksede op hos HERREN.
Hannatu kuwa ta sami alfarma daga Ubangiji. Ta yi ciki. Ana cikin haka Sama’ila kuwa sai girma yake ta yi a gaban Ubangiji.
22 Eli var meget gammel, og da han hørte, hvorledes hans Sønner behandlede hele Israel, og at de lå hos Kvinderne, som gjorde Tjeneste ved Indgangen til Åbenbaringsteltet,
To, Eli kuwa ya tsufa ƙwarai, yana kuma jin labari duk abin da’ya’yansa suke yi wa dukan Isra’ila, da yadda suke lalata da matan da suke hidima a bakin ƙofar Tentin Sujada.
23 sagde han til dem: "Hvorfor gør I sådanne Ting, som jeg hører alt Folket tale om?
Saboda haka ya ce musu, “Don me kuke yin waɗannan abubuwa? Na sami labari daga wurin mutane a kan duk ayyukan muguntanku.
24 Bær eder dog ikke således ad, mine Sønner! Thi det er ikke noget godt Rygte, jeg hører gå fra Mund til Mund i HERRENs Folk.
A’a,’ya’yana ba labari mai kyau nake ji cikin mutanen Ubangiji ba.
25 Når en Mand synder mod en anden, dømmer Gud dem imellem; men synder en Mand mod HERREN, hvem kan da optræde som Dommer til Gunst for ham?" Men de brød sig ikke om deres Faders Advarsel, thi HERREN vilde deres Død.
In mutum ya yi wa wani laifi Allah yakan kāre shi; amma in mutum ya yi wa Ubangiji zunubi wa zai kāre shi?” Duk da haka,’ya’yansa ba su kula da gargaɗin mahaifinsu ba, domin nufin Ubangiji ne yă hallaka su.
26 Men Drengen Samuel voksede til og gik stadig frem i Yndest både hos HERREN og Mennesker.
Yaron nan Sama’ila ya dinga girma cikin kwarjini da cikin tagomashi a gaba Ubangiji da mutane.
27 Da kom en Guds Mand til Eli og sagde: Så siger HERREN: "Se, jeg åbenbarede mig for dit Fædrenehus, dengang de var Trælle for Faraos Hus i Ægypten,
Wani mutum ya zo wurin Eli ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ashe ban bayana kaina sosai ga mahaifinka lokacin da yake a Masar a ƙarƙashin Fir’auna ba?
28 og jeg udvalgte det af alle Israels Stammer til at gøre Præstetjeneste for mig, til at træde op på mit Alter for at tænde Offerild og til at bære Efod for mit Åsyn; og jeg tildelte dit Fædrenehus alle Israeliternes Ildofre.
Na zaɓi mahaifinka daga cikin dukan kabilar Isra’ila yă zama firist nawa don yă yi hidima a bagade, don yă ƙona turare mai ƙanshi, don kuma yă sanya doguwar riga a gabana. Na kuma ba wa iyalin mahaifinka dukan hadaya ta ƙonawa da Isra’ila suka miƙa.
29 Hvor kan du da se ondt til mit Slagtoffer og Afgrødeoffer, som jeg har påbudt, og ære dine Sønner fremfor mig, idet l gør eder tilgode med det bedste at alle mit Folk Israels Offergaver!
Don me kuke rena hadayata da sadakokina da na ƙayyade domin mazaunina? Don me kake girmama’ya’yanka fiye da ni ta wurin cinye sashe mafi kyau na kowane hadayar da mutanena Isra’ila suka miƙa?’
30 Derfor lyder det fra HERREN, Israels Gud: Vel har jeg sagt, at dit Hus og dit Fædrenehus for stedse skulde færdes for mit Åsyn; men nu, lyder det fra HERREN, være det langt fra mig! Nej, dem, som ærer mig, vil jeg ære, og de, som ringeagter mig, skal beskæmmes.
“Saboda haka Ubangiji Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na yi alkawari cewa gidanka da gidan mahaifinka za su yi mini hidima a gabana har abada.’ Amma, yanzu Allah ya ce, ba zai yiwu ba; waɗanda suke girmama ni; Ni ma zan girmama su. Amma waɗanda suke ƙasƙantar da ni, haka za a ƙasƙantar da su.
31 Se, den Tid skal komme, da jeg, afhugger din og dit Fædrenehus's Arm, så ingen i dit Hus skal blive gammel;
Lokaci yana zuwa sa’ad da zan rage ƙarfinka da ƙarfin iyalin gidan mahaifinka. Domin kada a sāke samun tsohon mutum a zuriyarka.
32 og du skal se ondt til alt det gode, HERREN gør mod Israel, og ingen Sinde skal nogen i din Slægt blive gammel.
Za ka zama da ɓacin rai a mazaunina ko da yake za a yi wa Isra’ila alheri. A zuriyarka ba za a taɓa samun tsohon mutum ba.
33 Kun en eneste af din Slægt vil jeg undlade at bortrydde fra mit Alter for at lade hans Øjne hentæres og hans Sjæl vansmægte: men alle de andre i din Slægt skal dø for Menneskers Sværd.
Kowannenku da ban kashe daga hidima a bagadena ba, za a bar shi don yă cika idanunka da hawaye da kuma baƙin ciki, dukan sauran zuriyarka kuwa za su mutu a ƙuruciyarsu.
34 Og det Tegn, du får derpå, skal være det, der overgår dine to Sønner Hofni og Pinehas: På een Dag skal de begge dø.
“‘Abin da kuma ya faru da’ya’yanka biyu Hofni da Finehas zai zama alama a gare ka; saboda mutuwarsu za tă zama a rana ɗaya.
35 Men jeg vil udvælge mig en trofast Præst; han skal handle efter mit Hjerte og mit Sind, og ham vil jeg bygge et varigt Hus, så han altid skal færdes for min Salvedes Åsyn.
Zan tayar wa kaina amintaccen firist wanda zai aikata abin da nake so yă yi, zan kuwa ba shi zuriya da koyaushe za su yi aiki a gaban zaɓaɓɓen sarkina.
36 Da skal enhver, som er tilbage af din Slægt, komme og kaste sig til Jorden for ham for at få en Skilling eller en Skive Brød, og han skal sige: Und mig dog Plads ved et af dine Præsteskaber, for at jeg kan have en Bid Brød at spise!"
Sa’an nan duk wanda ya rage a zuriyarka zai zo yă durƙusa a gabansa yă roƙi kuɗi da abinci, zai kuma roƙa a yardar masa yă taimaki firistoci da aiki domin yă sami abin da zai ci.’”

< 1 Samuel 2 >