< 1 Samuel 12 >

1 Da sagde Samuel til hele Israel: "Se, jeg har føjet eder i alt, hvad I har bedt mig om, og sat en Konge over eder.
Sama’ila ya ce wa Isra’ilawa duka, “Na saurari abubuwan da kuka faɗa mini, na kuma naɗa muku sarki.
2 Se, nu færdes Kongen for eders Ansigt; jeg er gammel og grå, og mine Sønner er nu iblandt eder; men jeg har færdedes for eders Ansigt fra min Ungdom indtil i Dag.
Yanzu kuna da sarki a matsayin shugaba, ni kuwa na tsufa har da furfura, yarana maza kuma suna tare da ku. Na yi shugabancinku tun ina yaro.
3 Se, her står jeg; viden imod mig i HERRENs og hans, Salvedes Påhør! Hvis Okse har jeg taget? Hvis Æsel har jeg taget? Hvem har jeg, undertrykt? Hvem har jeg gjort Uret? Af hvem har jeg taget Gave og derfor lukket Øjnene? I så Fald vil jeg give eder Erstatning!"
Ga ni a gabanku. Idan na yi wani abin da ba daidai ba sai ku faɗa a gaban Ubangiji, da gaban sarkin da ya keɓe. Ko na taɓa ƙwace saniya ko jakin wani? Ko na taɓa cuce wani, ko in danne hakkinsa? Ko na taɓa cin hanci daga hannun ɗayanku? Idan na taɓa yi ɗaya daga cikin waɗannan, sai ku faɗa mini, zan kuwa mayar masa.”
4 Da sagde de: "Du har ikke undertrykt os eller gjort os Uret eller taget noget fra nogen."
Suka ce, “Ba ka cuci ko danne hakkin kowa ba, ba ka ƙwace kome daga hannun kowa ba.”
5 Derpå sagde han til dem: "Så er HERREN i Dag Vidne over for eder, også hans Salvede er Vidne, at I ikke har fundet noget hos mig." De sagde: "Ja!"
Sama’ila ya ce musu, “Ubangiji yă zama shaida a kanku, shafaffensa kuma yă zama shaida a wannan rana cewa ba ku same ni da wani laifin kome ba.” Suka ce, “I, shi ne shaida.”
6 Da sagde Samuel til Folket: "HERREN er Vidne, han, som udrustede Moses og Aron og førte eders Fædre op fra Ægypten.
Sa’an nan Sama’ila ya ce wa mutane, Ubangiji ne ya naɗa Musa da Haruna suka fitar da kakanninku daga Masar.
7 Så træd nu frem, at jeg kan gå i Rette med eder for HERRENs Åsyn og kundgøre eder alle de Gerninger, HERREN i sin Retfærdigher har øvet mod eder og eders Fædre.
Yanzu ku tsaya nan zan yi fito-na-fito da ku da shaida a gaban Ubangiji kan dukan ayyuka masu alherin da Ubangiji ya aikata saboda ku da kakanninku.
8 Da Jakob og hans Sønner var kommet til Ægypten, og Ægypterne plagede dem, råbte eders Fædre til HERREN, og HERREN sendte Moses og Aron, som førte eders Fædre ud af Ægypten, og han lod dem bosætte sig her.
Bayan da Yaƙub da’ya’yansa suka shiga Masar suka yi kukan neman taimako daga Ubangiji, Ubangiji kuwa ya aika musu da Musa da Haruna. Su ne suka kawo kakanni-kakanninku daga Masar suka zauna a nan.
9 Men de glemte HERREN deres Gud; derfor prisgav han dem til Kong Jabin af Hazors Hærfører Sisera, til Filisterne og til Moabs Konge, så de angreb dem.
Amma suka manta da Ubangiji Allahnsu, shi kuma ya bashe su a hannun Sisera shugaban rundunar Hazor da kuma hannun Filistiyawa da sarkin Mowab wanda suka yi yaƙi da su.
10 Da råbte de til HERREN og sagde: Vi har syndet, thi vi forlod HERREN og dyrkede Ba'alerne og Astarterne; men fri os nu af vore Fjenders Hånd, så vil vi dyrke dig!
Suka yi kuka a gaban Ubangiji suka ce, “Mun yi zunubi mun bar Ubangiji, muka bauta wa Ba’al da Ashtarot. Amma ka cece mu yanzu daga hannun abokan gābanmu, mu kuwa za mu bauta maka.”
11 Så sendte HERREN Jerubba'al, Barak, Jefta og Samuel; og han friede eder af eders Fjenders Hånd rundt om, så I kunde bo i Tryghed.
Sai Ubangiji ya aiki Yerub-Ba’al da Bedan da Yefta da Sama’ila, ya cece ku daga hannun abokan gābanku a kowane gefe domin ku sami cikakken zaman lafiya.
12 Men da I så Ammoniterkongen Nahasj rykke frem imod eder, sagde I til mig: Nej, en Konge skal herske over os uagtet HERREN eders Gud var eders Konge!
Amma da kuka ga Nahash sarkin Ammonawa yana matsowa yă yaƙe, sai kuka ce mini, “Sam, muna so sarki yă shugabance mu.” Ko da yake Ubangiji Allahnku ne yake mulkinku.
13 Og nu, her står Kongen, som I har valgt og krævet; se, HERREN har sat en Konge over eder!
Yanzu ga sarkinku da kuka zaɓa wanda kuka nema, ga shi Ubangiji ya naɗa muku sarki.
14 Hvis I frygter HERREN og tjener ham, adlyder hans Røst og ikke er genstridige mod HERRENs Bud, men følger HERREN eders Gud, både I og Kongen, som har fået Herredømmet over eder, da skal det gå eder vel.
In kuka ji tsoron Ubangiji, kuka bauta masa, kuka yi masa biyayya, ba ku kuwa ƙi bin umarninsa ba, in kuma ku da sarkin da yake mulkinku kun bi Ubangiji Allahnku, to, za ku zauna lafiya.
15 Adlyder I derimod ikke HERRENs Røst, men er genstridige mod HERRENs Bud, da skal HERRENs Hånd ramme eder og eders Konge og ødelægge eder.
Amma in ba ku yi biyayya ga Ubangiji ba, in kuma kuka ƙi bin umarnansa, fushinsa zai zauna a kanku.
16 Træd nu frem og se den vældige Gerning, HERREN vil øve for eders Øjne!
Yanzu ku tsaya tsit ku ga abin da Ubangiji ke dab da yi a gabanku.
17 Har vi ikke Hvedehøst nu? Men jeg vil råbe til HERREN, at han skal sende Torden og Regn, for at I kan kende og se, at det i HERRENs Øjne var en stor Brøde I begik, da I krævede en Konge!"
Ba lokacin yankan alkama ke nan ba? Zan roƙi Ubangiji yă aiko da tsawa da ruwan sama, za ku kuwa gane wace irin mugunta kuka yi a gaban Ubangiji sa’ad da kuka roƙa a ba ku sarki.
18 Derpå råbte Samuel til HERREN, og HERREN sendte samme Dag Torden og Regn. Da frygtede hele folket såre for HERREN og Samuel,
Sai Sama’ila ya roƙi Ubangiji, a ranar kuwa Ubangiji ya aiko da tsawa da ruwan sama. Dukan mutane suka ji tsoron Ubangiji da kuma Sama’ila.
19 og hele Folket sagde til Samuel: "Bed for dine Trælle til HERREN din Gud, at vi ikke skal dø, fordi vi til vore andre Synder har føjet den Brøde at kræve en Konge!"
Dukan mutane suka ce wa Sama’ila, “Ka yi addu’a ga Ubangiji Allahnka saboda bayinka, domin kada mu mutu, gama mun ƙara wa kanmu zunubi da muka roƙa a yi mana sarki.”
20 Da sagde Samuel til Folket: "Frygt ikke! Vel har I øvet al den Synd; men vend eder nu ikke fra HERREN, tjen ham af hele eders Hjerte
Sama’ila ya ce, “Kada ku ji tsoro.” Kun yi waɗannan mugunta duk da haka kada ku bar bin Ubangiji, amma ku bauta wa Ubangiji da dukan zuciyarku.
21 og vend eder ikke til dem, som er Tomhed og hverken kan hjælpe eller frelse, fordi de er Tomhed.
Kada ku bi alloli marasa amfani. Ba za su iya yi muku kome nagari ba, ba kuwa za su iya cece ku ba, gama ba su da amfani.
22 Thi for sit store Navns Skyld vil HERREN ikke forstøde sit Folk, da det jo har behaget HERREN at gøre eder til sit Folk.
Saboda suna mai girma da Ubangiji yake da shi, ba zai taɓa ƙin mutanensa ba. Gama Ubangiji ya ji daɗi da ya yi ku mutanensa.
23 Det være også langt fra mig at synde mod HERREN og høre op med at bede for eder; jeg vil også vise eder den gode og rette Vej;
Ni kam ba zai taɓa yiwu in yi wa Ubangiji zunubi ta wurin ƙin yin addu’a dominku ba. Zan koya muku hanyar da tana da kyau da ta kuma cancanta.
24 men frygt HERREN og tjen ham oprigtigt af hele eders Hjerte; thi se, hvor store Ting han gjorde imod eder!
Amma ku amince za ku ji tsoron Ubangiji, ku bauta masa da aniya da dukan zuciyarku, kuna da manyan abubuwan da ya yi muku.
25 Men hvis I handler ilde, skal både I og eders Konge gå til Grunde!"
Amma in kuka duƙufa cikin aikin mugunta da ku da sarkinku za a hallaka ku.

< 1 Samuel 12 >