< Første Kongebog 5 >

1 Da Kong Hiram af Tyrus hørte, at Salomo var salvet til Konge i stedet for sin Fader, sendte han nogle af sine Folk til ham; thi Hiram havde altid været Davids Ven.
Sa’ad da Hiram sarkin Taya ya ji an shafe Solomon sarki yă gāji mahaifinsa Dawuda, sai ya aika da jakadunsa zuwa wurin Solomon, gama shi da Dawuda abokai ne sosai dukan kwanakinsa.
2 Og Salomo sendte Hiram følgende Bud:
Solomon ya mayar da wannan saƙo ga Hiram ya ce,
3 "Du ved, at min Fader David ikke kunde bygge HERREN sin Guds Navn et Hus for de Kriges Skyld, man fra alle Sider påførte ham, indtil HERREN lagde hans Fjender under hans Fødder.
“Ka san cewa saboda yaƙe-yaƙen da abokan gāba suka yi da mahaifina a kowane gefe, ya sa bai iya gina haikali domin Sunan Ubangiji Allahnsa ba, sai da Ubangiji ya sa abokan gābansa a ƙarƙashin ƙafafunsa.
4 Men nu har HERREN min Gud skaffet mig Ro til alle Sider; der findes ingen Modstandere, og der er ingen Fare på Færde.
Amma yanzu Ubangiji Allahna ya ba ni hutu a kowane gefe, babu kuma gāba ko masifa.
5 Se, derfor har jeg i Sinde at bygge HERREN min Guds Navn et Hus efter HERRENs Ord til min Fader David: Din Søn, som jeg sætter på din Trone i dit Sted, han skal bygge Huset for mit Navn.
Ina niyya in gina haikali domin Sunan Ubangiji Allahna, yadda Ubangiji ya faɗa wa mahaifina Dawuda, sa’ad da ya ce, ‘Ɗanka wanda zai gāje ka, shi zai gina haikali domin Sunana.’
6 Giv derfor Ordre til, at der fældes Cedre til mig på Libanon. Mine Folk skal arbejde sammen med dine, og jeg vil give dineFolk den Løn, du kræver; thi du ved jo, at der ikke findes nogen hos os, der kan fælde Træer som Zidonierne!"
“Don haka, ka ba da umarni a yanka mini itatuwan al’ul na ƙasar Lebanon. Ma’aikatana za su haɗa hannu da ma’aikatanka, ni kuwa zan biya ka albashin ma’aikatanka kamar yadda ka faɗa. Gama ka san cewa babu wani a cikinmu da ya iya yanka itacen katako kamar Sidoniyawa.”
7 Da Hiram modtog dette Bud fra Salomo, glædede det ham meget, og han sagde: "Lovet være HERREN i dag, fordi han har givet David en viis Søn til at herske over dette store Folk!"
Da Hiram ya ji saƙon Solomon, sai ya ji daɗi ƙwarai, ya kuma ce, “Yabo ga Ubangiji a yau, gama ya ba wa Dawuda ɗa mai hikima yă yi mulki a bisa wannan al’umma mai girma.”
8 Og Hiram sendte Salomo følgende Svar: "Jeg har modtaget det Bud, du sendte mig, og jeg skal opfylde alt, hvad du ønsker med Hensyn til Ceder- og Cyprestræer;
Sai Hiram ya aike wa Solomon da kalmomin nan, “Na sami saƙon da ka aika mini, zan kuma yi duk abin da kake so ta wurin tanada katakan al’ul da na fir.
9 mine Folk skal bringe dem fra Libanon ned til Havet, og så skal jeg lade dem samle til Tømmerflåder på Havet og sende dem til det Sted, du anviser mig; der skal jeg lade dem skille ad, så at du kan lade dem hente. Men du vil da også opfylde mit Ønske og sende Fødevarer til mit Hof!"
Ma’aikatana za su gangara da su daga Lebanon zuwa bakin teku. Zan sa a ɗaɗɗaura su su bi ruwan teku daga Lebanon zuwa bakin Bahar Rum da za ka nuna mini. A can zan kunce maka su, sa’an nan ka kwashe. Kai kuma za ka biya bukatata ta wurin tanadin abinci wa gidana.”
10 Så sendte Hiram Salomo alt, hvad han ønskede af Ceder- og Cyprestræer;
A haka Hiram ya ci gaba da aika wa Solomon al’ul da kuma fir da yake bukata.
11 og Salomo sendte Hiram 20 000 Kor Hvede til Underhold for hans Hof og 20 Kor Olie af knuste Oliven. Så meget sendte Salomo Hiram År efter År.
Solomon kuma ya ba wa Hiram mudu gari dubu ashirin na alkama a matsayin abinci domin gidansa, ya ƙara da garwa dubu ashirin na tataccen man zaitun. Solomon ya ci gaba da yin haka ga Hiram, shekara-shekara.
12 Og HERREN gav Salomo Visdom, som han havde lovet ham; og der var Fred mellem Hiram og Salomo, og de sluttede Pagt med hinanden.
Ubangiji ya ba wa Solomon hikima, kamar yadda ya yi masa alkawari. Dangantakar zaman lafiya ta kasance tsakanin Hiram da Solomon, su biyun suka yi yarjejjeniya.
13 Kong Salomo udskrev nu Hoveriarbejdere overalt i Israel, og Hoveriarbejderne udgjorde 30 000 Mand.
Sarki Solomon ya ɗebi ma’aikata daga dukan Isra’ila, su dubu talatin.
14 Dem sendte han så til Libanon, et Hold på 10 000 om Måneden, således at de var en Måned på Libanon og to Måneder hjemme. Adoniram havd Tilsyn med Hoveriarbejderne.
Ya riƙa aika su dubu goma-goma zuwa Lebanon kowane wata, saboda su yi wata ɗaya a Lebanon, watanni biyu kuma a gida. Adoniram ne ya lura da aikin gandun.
15 Salomo havde 70 000 Lastdragere og 80 000 Stenhuggere i Bjergene
Solomon ya kasance da’yan ɗauko guda dubu saba’in da masu yankan duwatsu guda dubu tamanin a cikin tuddai,
16 foruden Overfogeder, der ledede Arbejdet, 3 300 Mand, som havde Opsyn med Folkene, der arbejdede.
ya kuma kasance da shugabanni dubu uku da ɗari uku waɗanda suke lura da aikin, su ne kuma suke bi da ma’aikatan.
17 På Kongens Bud brød de store Stenblokke, kostbare Sten til Templets Grundvold, Kvadersten;
Bisa ga umarnin sarki sai suka cire manyan duwatsu masu kyau don a tanada tushen duwatsun da aka gyara domin haikalin daga wurin haƙar duwatsun.
18 og Salomos og Hiroms Bygmestre og Folkene fra Gebal huggede dem til, og de gjorde Træstammerne og Stenene i Stand til Templets Opførelse.
Gwanayen Solomon da na Hiram da kuma mutanen Gebal, su suka yanka, suka kuma shirya katako da dutse don ginin haikali.

< Første Kongebog 5 >