< Lukas 5 >

1 Men det skete, da Folkeskaren trængte sig sammen om ham og hørte Guds Ord, og han stod ved Genezareths Sø,
Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
2 da saa han to Skibe staa ved Søen; men Fiskerne vare gaaede fra dem og toede Garnene.
sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
3 Og han gik om Bord i et af Skibene, som var Simons, og bad ham at lægge lidt fra Land; og han satte sig og lærte Skarerne fra Skibet.
Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
4 Men da han holdt op med at tale, sagde han til Simon: „Far ud paa Dybet, og kaster eders Garn ud til en Dræt!‟
Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
5 Og Simon svarede og sagde til ham: „Mester! vi have arbejdet hele Natten og fik intet; men paa dit Ord vil jeg kaste Garnene ud.‟
Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
6 Og da de gjorde det, fangede de en stor Mængde Fisk, og deres Garn sønderreves.
Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
7 Og de vinkede ad deres Stalbrødre i det andet Skib, at de skulde komme og hjælpe dem; og de kom, og de fyldte begge Skibene, saa at de vare nær ved at synke.
Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
8 Men da Simon Peter saa det, faldt han ned for Jesu Knæ og sagde: „Gaa bort fra mig, thi jeg er en syndig Mand, Herre!‟
Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
9 Thi en Rædsel var paakommen ham og alle dem, som vare med ham, over den Fiskedræt, som de havde faaet;
Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
10 ligeledes ogsaa Jakob og Johannes, Zebedæus's Sønner, som vare Simons Stalbrødre. Og Jesus sagde til Simon: „Frygt ikke, fra nu af skal du fange Mennesker.‟
Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
11 Og de lagde Skibene til Land og forlode alle Ting og fulgte ham.
Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
12 Og det skete, medens han var i en af Byerne, se, da var der en Mand fuld af Spedalskhed; og da han saa Jesus, faldt han paa sit Ansigt, bad ham og sagde: „Herre! om du vil, kan du rense mig.‟
Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
13 Og han udrakte Haanden og rørte ved ham og sagde: „Jeg vil; bliv ren!‟ Og straks forlod Spedalskheden ham.
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
14 Og han bød ham, at han skulde ikke sige det til nogen, men „gaa bort, og fremstil dig for Præsten, og offer for din Renselse, saaledes som Moses har befalet, til Vidnesbyrd for dem!‟
Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
15 Men Rygtet om ham udbredte sig end mere, og store Skarer kom sammen for at høre og for at helbredes for deres Sygdomme.
Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
16 Men han gik bort til Ørkenerne og bad.
Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
17 Og det skete en af de Dage, at han lærte, og der sad Farisæere og Lovlærere, som vare komne fra enhver Landsby i Galilæa og Judæa og fra Jerusalem; og Herrens Kraft var hos ham til at helbrede.
Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
18 Og se, nogle Mænd bare paa en Seng en Mand, som var værkbruden, og de søgte at bære ham ind og lægge ham foran ham.
Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 Og da de ikke fandt nogen Vej til at bære ham ind for Skarens Skyld, stege de op oven paa Taget og firede ham tillige med Sengen ned imellem Tagstenene midt iblandt dem foran Jesus.
Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
20 Og da han saa deres Tro, sagde han: „Menneske! dine Synder ere dig forladte.‟
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
21 Og de skriftkloge og Farisæerne begyndte at tænke saaledes ved sig selv: „Hvem er denne, som taler Gudsbespottelser? Hvem kan forlade Synder, uden Gud alene?‟
Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
22 Men da Jesus kendte deres Tanker, svarede han og sagde til dem: „Hvad tænke I paa i eders Hjerter?
Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
23 Hvilket er lettest at sige: Dine Synder ere dig forladte? eller at sige: Staa op og gaa?
Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
24 Men for at I skulle vide, at Menneskesønnen har Magt paa Jorden til at forlade Synder, ‟ saa sagde han til den værkbrudne: „Jeg siger dig, staa op, og tag din Seng, og gaa til dit Hus!‟
Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
25 Og han stod straks op for deres Øjne og tog det, som han laa paa, og gik hen til sit Hus og priste Gud.
Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
26 Og Forfærdelse betog alle, og de priste Gud; og de bleve fulde af Frygt og sagde: „Vi have i Dag set utrolige Ting.‟
Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
27 Og derefter gik han ud og saa en Tolder ved Navn Levi sidde ved Toldboden, og han sagde til ham: „Følg mig!‟
Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
28 Og han forlod alle Ting og stod op og fulgte ham.
Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
29 Og Levi gjorde et stort Gæstebud for ham i sit Hus; og der var en stor Skare af Toldere og andre, som sade til Bords med dem.
Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
30 Og Farisæerne og deres skriftkloge knurrede imod hans Disciple og sagde: „Hvorfor spise og drikke I med Toldere og Syndere?‟
Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
31 Og Jesus svarede og sagde til dem: „De raske trænge ikke til Læge, men de syge.
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
32 Jeg er ikke kommen for at kalde retfærdige, men Syndere til Omvendelse.‟
Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 Men de sagde til ham: „Johannes's Disciple faste ofte og holde Bønner og Farisæernes ligesaa; men dine spise og drikke?‟
Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
34 Men Jesus sagde til dem: „Kunne I vel faa Brudesvendene til at faste, saa længe Brudgommen er hos dem?
Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
35 Men der skal komme Dage, da Brudgommen bliver tagen fra dem; da skulle de faste i de Dage.‟
Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
36 Men han sagde ogsaa en Lignelse til dem: „Ingen river en Lap af et nyt Klædebon og sætter den paa et gammelt Klædebon; ellers river han baade det nye sønder, og Lappen fra det nye vil ikke passe til det gamle.
Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
37 Og ingen kommer ung Vin paa gamle Læderflasker; ellers sprænger den unge Vin Læderflaskerne, og den spildes, og Læderflaskerne ødelægges.
Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
38 Men man skal komme ung Vin paa nye Læderflasker, saa blive de begge bevarede.
A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
39 Og ingen, som har drukket den gamle, vil have den unge; thi han siger: Den gamle er god.‟
Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”

< Lukas 5 >