< Lukas 1 >

1 Efterdi mange have taget sig for at forfatte en Beretning om de Ting, som ere fuldbyrdede iblandt os,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 saaledes som de, der fra Begyndelsen bleve Øjenvidner og Ordets Tjenere, have overleveret os:
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 saa har ogsaa jeg besluttet, efter nøje at have gennemgaaet alt forfra, at nedskrive det for dig i Orden, mægtigste Theofilus!
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 for at du kan erkende Paalideligheden af de Ting, hvorom du er bleven mundtligt undervist.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 I de Dage, da Herodes var Konge i Judæa, var der en Præst af Abias Skifte, ved Navn Sakarias; og han havde en Hustru af Arons Døtre, og hendes Navn var Elisabeth.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Men de vare begge retfærdige for Gud og vandrede udadlelige i alle Herrens Bud og Forskrifter.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 Og de havde intet Barn, efterdi Elisabeth var ufrugtbar, og de vare begge fremrykkede i Alder.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Men det skete, medens han efter sit Skiftes Orden gjorde Præstetjeneste for Gud,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 tilfaldt det ham efter Præstetjenestens Sædvane at gaa ind i Herrens Tempel og bringe Røgelseofferet.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 Og hele Folkets Mængde holdt Bøn udenfor i Røgelseofferets Time.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Men en Herrens Engel viste sig for ham, staaende ved den højre Side af Røgelsealteret.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 Og da Sakarias saa ham, forfærdedes han, og Frygt faldt over ham.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 Men Engelen sagde til ham: „Frygt ikke, Sakarias! thi din Bøn er hørt, og din Hustru Elisabeth skal føde dig en Søn, og du skal kalde hans Navn Johannes.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 Og han skal blive dig til Glæde og Fryd, og mange skulle glædes over hans Fødsel;
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 thi han skal være stor for Herren. Og Vin og stærk Drik skal han ej drikke, og han skal fyldes med den Helligaand alt fra Moders Liv,
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 og mange af Israels Børn skal han omvende til Herren deres Gud.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 Og han skal gaa foran for ham i Elias's Aand og Kraft for at vende Fædres Hjerter til Børn og genstridige til retfærdiges Sind for at berede Herren et velskikket Folk.‟
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 Og Sakarias sagde til Engelen: „Hvorpaa skal jeg kende dette? thi jeg er gammel, og min Hustru er fremrykket i Alder.‟
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 Og Engelen svarede og sagde til ham: „Jeg er Gabriel, som staar for Guds Aasyn, og jeg er udsendt for at tale til dig og for at forkynde dig dette Glædesbudskab.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 Og se, du skal blive stum og ikke kunne tale indtil den Dag, da dette sker, fordi du ikke troede mine Ord, som dog skulle fuldbyrdes i deres Tid.‟
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 Og Folket biede efter Sakarias, og de undrede sig over, at han tøvede i Templet.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 Og da han kom ud, kunde han ikke tale til dem, og de forstode, at han havde set et Syn i Templet; og han gjorde Tegn til dem og forblev stum.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 Og det skete, da hans Tjenestes Dage vare fuldendte, gik han hjem til sit Hus.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 Men efter disse Dage blev hans Hustru Elisabeth frugtsommelig, og hun skjulte sig fem Maaneder og sagde:
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 „Saaledes har Herren gjort imod mig i de Dage, da han saa til mig for at borttage min Skam iblandt Mennesker.‟
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Men i den sjette Maaned blev Engelen Gabriel sendt fra Gud til en By i Galilæa, som hedder Nazareth,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 til en Jomfru, som var trolovet med en Mand ved Navn Josef, af Davids Hus; og Jomfruens Navn var Maria.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 Og Engelen kom ind til hende og sagde: „Hil være dig, du benaadede, Herren er med dig, du velsignede iblandt Kvinder!‟
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 Men hun blev forfærdet over den Tale, og hun tænkte, hvad dette skulde være for en Hilsen.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 Og Engelen sagde til hende: „Frygt ikke, Maria! thi du har fundet Naade hos Gud.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 Og se, du skal undfange og føde en Søn, og du skal kalde hans Navn Jesus.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 Han skal være stor og kaldes den Højestes Søn; og Gud Herren skal give ham Davids, hans Faders Trone.
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 Og han skal være Konge over Jakobs Hus evindelig, og der skal ikke være Ende paa hans Kongedømme.‟ (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Men Maria sagde til Engelen: „Hvorledes skal dette gaa til, efterdi jeg ikke ved af nogen Mand?‟
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 Og Engelen svarede og sagde til hende: „Den Helligaand skal komme over dig, og den Højestes Kraft skal overskygge dig; derfor skal ogsaa det hellige, som fødes, kaldes Guds Søn.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 Og se, Elisabeth din Frænke, ogsaa hun har undfanget en Søn i sin Alderdom, og denne Maaned er den sjette for hende, som kaldes ufrugtbar.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 Thi intet vil være umuligt for Gud.‟
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Men Maria sagde: „Se, jeg er Herrens Tjenerinde; mig ske efter dit Ord!‟ Og Engelen skiltes fra hende.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Men Maria stod op i de samme Dage og drog skyndsomt til Bjergegnen til en By i Juda.
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 Og hun kom ind i Sakarias's Hus og hilste Elisabeth.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 Og det skete, da Elisabeth hørte Marias Hilsen, sprang Fosteret i hendes Liv. Og Elisabeth blev fyldt med den Helligaand
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 og raabte med høj Røst og sagde: „Velsignet er du iblandt Kvinder! og velsignet er dit Livs Frugt!
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 Og hvorledes times dette mig, at min Herres Moder kommer til mig?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 Thi se, da din Hilsens Røst naaede mine Øren, sprang Fosteret i mit Liv med Fryd.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 Og salig er hun, som troede; thi det skal fuldkommes, hvad der er sagt hende af Herren.‟
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Og Maria sagde: „Min Sjæl ophøjer Herren;
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 og min Aand fryder sig over Gud, min Frelser;
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 thi han har set til sin Tjenerindes Ringhed. Thi se, nu herefter skulle alle Slægter prise mig salig,
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 fordi den mægtige har gjort store Ting imod mig. Og hans Navn er helligt;
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 og hans Barmhjertighed varer fra Slægt til Slægt over dem, som frygte ham.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 Han har øvet Vælde med sin Arm; han har adspredt dem, som ere hovmodige i deres Hjertes Tanke.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 Han har nedstødt mægtige fra Troner og ophøjet ringe.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 Hungrige har han mættet med gode Gaver, og rige har han sendt tomhændede bort.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 Han har taget sig af sin Tjener Israel for at ihukomme Barmhjertighed
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 imod Abraham og hans Sæd til evig Tid, saaledes som han talte til vore Fædre.‟ (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 Og Maria blev hos hende omtrent tre Maaneder, og hun drog til sit Hjem igen.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Men for Elisabeth fuldkommedes Tiden til, at hun skulde føde, og hun fødte en Søn.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 Og hendes Naboer og Slægtninge hørte, at Herren havde gjort sin Barmhjertighed stor imod hende, og de glædede sig med hende.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 Og det skete paa den ottende Dag, da kom de for at omskære Barnet; og de vilde kalde det Sakarias efter Faderens Navn.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 Og hans Moder svarede og sagde: „Nej, han skal kaldes Johannes.‟
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 Og de sagde til hende: „Der er ingen i din Slægt, som kaldes med dette Navn.‟
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 Men de gjorde Tegn til hans Fader om, hvad han vilde, det skulde kaldes.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 Og han forlangte en Tavle og skrev disse Ord: „Johannes er hans Navn.‟ Og de undrede sig alle.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 Men straks oplodes hans Mund og hans Tunge, og han talte og priste Gud.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 Og der kom en Frygt over alle, som boede omkring dem, og alt dette rygtedes over hele Judæas Bjergegn.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 Og alle, som hørte det, lagde sig det paa Hjerte og sagde: „Hvad mon der skal blive af dette Barn?‟ Thi Herrens Haand var med ham.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 Og Sakarias, hans Fader, blev fyldt med den Helligaand, og han profeterede og sagde:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 „Lovet være Herren, Israels Gud! thi han har besøgt og forløst sit Folk
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 og har oprejst os et Frelsens Horn i sin Tjener Davids Hus,
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 saaledes som han talte ved sine hellige Profeters Mund fra fordums Tid, (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 en Frelse fra vore Fjender og fra alle deres Haand, som hade os,
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 for at gøre Barmhjertighed imod vore Fædre og ihukomme sin hellige Pagt,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 den Ed, som han svor vor Fader Abraham, at han vilde give os,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 at vi, friede fra vore Fjenders Haand, skulde tjene ham uden Frygt,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 i Hellighed og Retfærdighed for hans Aasyn, alle vore Dage.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 Men ogsaa du, Barnlille! skal kaldes den Højestes Profet; thi du skal gaa foran for Herrens Aasyn for at berede hans Veje,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 for at give hans Folk Erkendelse af Frelse ved deres Synders Forladelse,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 for vor Guds inderlige Barmhjertigheds Skyld, ved hvilken Lyset fra det høje har besøgt os
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 for at skinne for dem, som sidde i Mørke og i Dødens Skygge, for at lede vore Fødder ind paa Fredens Vej.‟
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 Men Barnet voksede og blev styrket i Aanden; og han var i Ørknerne indtil den Dag, da han traadte frem for Israel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Lukas 1 >