< Lukas 23 >

1 Og hele Mængden stod op og førte ham for Pilatus.
Sai dukan majalisa suka tashi, suka kai shi gaban Bilatus.
2 Og de begyndte at anklage ham og sagde: „Vi have fundet, at denne vildleder vort Folk og forbyder at give Kejseren Skat og siger om sig selv, at han er Kristus, en Konge.‟
Suka fara zarginsa suna cewa, “Mun sami wannan mutum yana rikitar da al’ummarmu. Yana hana a biya haraji ga Kaisar. Yana kuma cewa, shi Kiristi ne, sarki kuma.”
3 Men Pilatus spurgte ham og sagde: „Er du Jødernes Konge?‟ Og han svarede og sagde til ham: „Du siger det.‟
Sai Bilatus ya tambayi Yesu ya ce, “Kai ne sarkin Yahudawa?” Yesu ya amsa ya ce, “I, haka yake, kamar yadda ka faɗa.”
4 Men Pilatus sagde til Ypperstepræsterne og til Skarerne: „Jeg finder ingen Skyld hos dette Menneske.‟
Sai Bilatus ya sanar wa manyan firistoci da taron ya ce, “Ni fa, ban sami wani ainihin abin zargi game wannan mutum nan ba.”
5 Men de bleve ivrigere og sagde: „Han oprører Folket, idet han lærer over hele Judæa fra Galilæa af, hvor han begyndte, og lige hertil.‟
Amma suka nace, suna cewa, “Yana tā da hankulan mutane, ko’ina a Yahudiya da koyarwarsa. Ya fara daga Galili, ga shi har ya kai nan.”
6 Men da Pilatus hørte om Galilæa, spurgte han, om Manden var en Galilæer.
Da Bilatus ya ji haka, sai ya yi tambaya, “Ko shi mutumin Galili ne?”
7 Og da han fik at vide, at han var fra Herodes's Omraade, sendte han ham til Herodes, som ogsaa selv var i Jerusalem i disse Dage.
Da ya ji cewa, Yesu yana ƙarƙashin mulkin Hiridus ne, sai ya aika da shi zuwa wurin Hiridus, don a lokacin Hiridus yana Urushalima.
8 Men da Herodes saa Jesus, blev han meget glad; thi han havde i lang Tid gerne villet se ham, fordi han hørte om ham, og han haabede at se et Tegn blive gjort af ham.
Da Hiridus ya ga Yesu, sai ya yi murna ƙwarai, don tun dā ma yana marmari ya gan shi a kan abin da ya ji game da shi. Ya yi fata ya ga Yesu, yă kuma yi waɗansu ayyukan banmamaki.
9 Og han gjorde ham mange Spørgsmaal; men han svarede ham intet.
Ya yi masa tambayoyi masu yawa, amma Yesu bai ba shi ko amsa ba.
10 Men Ypperstepræsterne og de skriftkloge stode og anklagede ham heftigt.
Manyan firistoci da malaman dokoki suna tsaye a wurin, suna kawo zargi masu ƙarfi a kansa.
11 Men da Herodes med sine Krigsfolk havde haanet og spottet ham, kastede han et prægtigt Klædebon om ham og sendte ham til Pilatus igen.
Sai Hiridus da sojojinsa suka wulaƙanta shi, suka yi masa ba’a. Sa’an nan, suka sa masa babban riga, suka mai da shi wurin Bilatus.
12 Paa den Dag bleve Herodes og Pilatus Venner med hinanden; thi de vare før i Fjendskab med hinanden.
A ranar, Hiridus da Bilatus suka zama abokan juna, don tun dā ma, su abokan gāba ne.
13 Men Pilatus sammenkaldte Ypperstepræsterne og Raadsherrerne og Folket
Bilatus ya tara manyan firistoci, da masu mulki, da mutane,
14 og sagde til dem: „I have ført dette Menneske til mig som en, der forfører Folket til Frafald; og se, jeg har forhørt ham i eders Paahør og har ingen Skyld fundet hos dette Menneske i det, som I anklage ham for,
ya ce musu, “Kun kawo mini wannan mutum, a matsayin wanda yana zuga mutane su yi tawaye. Na bincike shi a gabanku, ban ga a kan me kuka kawo kararsa ba.
15 og Herodes ikke heller, thi han sendte ham tilbage til os; og se, han har intet gjort, som han er skyldig at dø for.
Haka ma Hiridus, shi ya sa ya dawo da shi nan wurinmu. Kamar yadda ku ma kun gani, ba abin da mutumin nan ya yi, da ya isa mutuwa.
16 Derfor vil jeg revse ham og lade ham løs.‟
Saboda haka, zan yi masa bulala, in sāke shi.”
17 [Men han var nødt til at løslade dem een paa Højtiden.]
18 Men de raabte alle sammen og sagde: „Bort med ham, men løslad os Barabbas!‟
Suka yi ihu gaba ɗaya suka ce, “A yi gaba da wannan mutum! A sake mana Barabbas!”
19 Denne var kastet i Fængsel for et Oprør, som var sket i Staden, og for Mord.
(Barabbas yana kurkuku saboda laifin tā da hankali a birnin, da kuma don kisankai.)
20 Og atter talte Pilatus til dem, da han gerne vilde løslade Jesus.
Sai Bilatus ya sāke yin musu magana don yana so ya saki Yesu.
21 Men de raabte til ham og sagde: „Korsfæst, korsfæst ham!‟
Amma sai suka ci gaba da ihu, suna cewa, “A gicciye shi! A gicciye shi!”
22 Men han sagde tredje Gang til dem: „Hvad ondt har da denne gjort? Jeg har ingen Dødsskyld fundet hos ham; derfor vil jeg revse ham og lade ham løs.‟
Ya sāke ce musu, sau na uku, “Don me? Wane laifi wannan mutum ya yi? Ni dai ban same shi da wani dalilin da ya isa a kashe shi ba. Saboda haka, zan sa a hore shi, sa’an nan in sāke shi.”
23 Men de trængte paa med stærke Raab og forlangte, at han skulde korsfæstes; og deres Raab fik Overhaand.
Amma suna ihu, suna nacewa, suna cewa, dole a gicciye shi, har ihunsu ya rinjaye shi.
24 Og Pilatus dømte, at deres Forlangende skulde opfyldes;
Sai Bilatus ya biya bukatarsu da ya ji roƙonsu.
25 og han løslod den, de forlangte, som var kastet i Fængsel for Oprør og Mord; men Jesus overgav han til deres Villie.
Ya saki mutumin da aka jefa a kurkuku saboda tā da hankali, da kisankai, shi wanda suka roƙa. Sa’an nan ya ba da Yesu ga nufinsu.
26 Og da de førte ham bort, toge de fat paa en vis Simon fra Kyrene, som kom fra Marken, og lagde Korset paa ham, for at han skulde bære det bag efter Jesus.
Sa’ad da suna tafiya da Yesu, sai wani da ake kira Siman, mutumin Sairin, yana zuwa daga ƙauye. Suka kama shi, suka aza masa gicciyen, suka tilasta shi ya ɗauki gicciyen, ya bi Yesu a baya.
27 Men der fulgte ham en stor Hob af Folket, og af Kvinder, som jamrede og græd over ham.
Mutane da yawa sosai suka bi shi, a cikinsu ma da mata waɗanda suka yi makoki da kuka dominsa.
28 Men Jesus vendte sig om til dem og sagde: „I Jerusalems Døtre! græder ikke over mig, men græder over eder selv og over eders Børn!
Yesu ya juya, ya ce musu, “’Yan matan Urushalima, kada ku yi kuka saboda ni, amma ku yi kuka saboda kanku, da kuma saboda’ya’yanku.
29 Thi se, der kommer Dage, da man skal sige: Salige ere de ufrugtbare og de Liv, som ikke fødte, og de Bryster, som ikke gave Die.
Gama lokaci yana zuwa da za ku ce, ‘Masu albarka ne bakararru, wato, mata marasa haihuwa, da mahaihuwar da ba su taɓa haihuwa ba, da kuma mama da ba su taɓa shayar da nono ba!’
30 Da skulle de begynde at sige til Bjergene: Falder over os! og til Højene: Skjuler os!
Sa’an nan “‘za su ce wa duwatsu, “Ku fāɗi a kanmu!” Za su ce wa tuddai kuma, “Ku rufe mu!”’
31 Thi gør man dette ved det grønne Træ, hvad vil da ske med det tørre?‟
Gama in mutane suna yin waɗannan abubuwa a lokacin da itace na ɗanye, me zai faru in ya bushe?”
32 Men der blev ogsaa to andre Misdædere førte ud for at henrettes med ham.
Tare da shi akwai mutum biyu masu laifi, da aka tafi da su don a gicciye.
33 Og da de vare komne til det Sted, som kaldes „Hovedskal‟, korsfæstede de ham der, og Misdæderne, den ene ved hans højre, og den anden ved hans venstre Side.
Da suka isa wurin da ake kira “Ƙoƙon Kai,” nan suka gicciye shi, tare da masu laifin nan, ɗaya a hannun damansa, ɗayan kuma a hagunsa.
34 Men Jesus sagde: „Fader! forlad dem; thi de vide ikke, hvad de gøre.‟ Men de delte hans Klæder imellem sig ved Lodkastning.
Yesu ya ce, “Ya Uba ka yi musu gafara, don ba su san abin da suke yi ba.” Suka rarraba tufafinsa ta wurin jefa ƙuri’a.
35 Og Folket stod og saa til; men ogsaa Raadsherrerne spottede ham og sagde: „Andre har han frelst, lad ham frelse sig selv, dersom han er Guds Kristus, den udvalgte.‟
Mutanen suka tsaya suna kallo. Har masu mulki ma suka yi masa ba’a, suna cewa, “Ya ceci waɗansu, to, ya ceci kansa in shi ne Kiristi na Allah, Zaɓaɓɓe.”
36 Men ogsaa Stridsmændene spottede ham, idet de traadte til, rakte ham Eddike og sagde:
Sojoji su ma, suka zo suka yi masa ba’a. Suka miƙa masa ruwan tsami.
37 „Dersom du er Jødernes Konge, da frels dig selv!‟
Suka ce, “In kai ne sarkin Yahudawa, ka ceci kanka mana.”
38 Men der var ogsaa sat en Overskrift over ham [skreven paa Græsk og Latin og Hebraisk]: „Denne er Jødernes Konge.‟
Bisa da shi kuma akwai rubutun da ya ce, Wannan shi ne Sarkin Yahudawa.
39 Men en af de ophængte Misdædere spottede ham og sagde: „Er du ikke Kristus? Frels dig selv og os!‟
Ɗaya daga cikin masu laifin da aka gicciye a wurin ya zazzage shi ya ce, “Shin, ba kai ne Kiristi ba? To, ka ceci kanka, ka kuma cece mu mana!”
40 Men den anden svarede og irettesatte ham og sagde: „Frygter heller ikke du Gud, da du er under den samme Dom?
Amma ɗayan mai laifi ya kwaɓe shi ya ce, “Ba ka da tsoron Allah ne, wai saboda kana ƙarƙashin hukunci ɗaya tare da shi?
41 Og vi ere det med Rette; thi vi faa igen, hvad vore Gerninger have forskyldt; men denne gjorde intet uskikkeligt.‟
Horonmu, daidai aka yi mana, sakamakon abin da muka yi ne. Amma wannan mutum, bai yi wani laifi ba.”
42 Og han sagde: „Jesus! kom mig i Hu, naar du kommer i dit Rige!‟
Sai ya ce, “Yesu, ka tuna da ni sa’ad da ka shiga mulkinka.”
43 Og han sagde til ham: „Sandelig, siger jeg dig, i Dag skal du være med mig i Paradiset.‟
Yesu ya amsa, ya ce masa, “Gaskiya nake faɗa maka, yau ɗin nan, za ka kasance tare da ni, a mulkina a sama.”
44 Og det var nu ved den sjette Time, og der blev Mørke over hele Landet indtil den niende Time,
Yanzu kuwa wajen sa’a ta shida ne, kuma duhu ya rufe ko’ina a ƙasar, har zuwa sa’a ta tara,
45 idet Solen formørkedes; og Forhænget i Templet splittedes midt over.
domin rana ta daina haskakawa. Labulen da yake cikin haikali kuma ya yage kashi biyu.
46 Og Jesus raabte med høj Røst og sagde: „Fader! i dine Hænder befaler jeg min Aand; ‟ og da han havde sagt det, udaandede han.
Yesu ya yi kira da babbar murya ya ce, “Ya Uba, na danƙa ruhuna a hannunka.” Da ya faɗi haka, sai ya ja numfashi na ƙarshe.
47 Men da Høvedsmanden saa det, som skete, gav han Gud Æren og sagde: „I Sandhed, dette Menneske var retfærdigt.‟
Da jarumin ya ga abin da ya faru, sai ya yabi Allah ya ce, “Gaskiya, wannan mutum mai adalci ne.”
48 Og alle Skarerne, som vare komne sammen til dette Skue, sloge sig for Brystet, da de saa, hvad der skete, og vendte tilbage.
Da dukan mutanen da suka taru, domin shaidar waɗannan abubuwa, suka ga abin da ya faru, sai suka buga ƙirjinsu suka tafi.
49 Men alle hans Kyndinge stode langt borte, ligesaa de Kvinder, som fulgte med ham fra Galilæa, og saa dette.
Amma dukan mutanen da suka san Yesu, tare da mata da suka bi shi daga Galili, suka tsaya daga nesa suna kallon abubuwan nan.
50 Og se, en Mand ved Navn Josef, som var Raadsherre, en god og retfærdig Mand,
Akwai wani mutum mai suna Yusuf, ɗan Majalisa, wanda shi nagari ne, mai adalci,
51 han havde ikke samtykket i deres Raad og Gerning, han var fra Arimathæa, en jødisk By, og han forventede Guds Rige;
shi dā ma bai yarda da shawararsu, da kuma abin da suka yi ba. Shi daga Arimateya ne wani garin Yahudiya. Yana kuma jiran zuwa mulkin Allah.
52 han gik til Pilatus og bad om Jesu Legeme.
Sai ya je wurin Bilatus ya roƙa a ba shi jikin Yesu.
53 Og han tog det ned og svøbte det i et fint Linklæde, og han lagde ham i en Grav, som var hugget i en Klippe, hvor endnu ingen nogen Sinde var lagt.
Sai ya saukar da jikin, ya nannaɗe shi a cikin zanen lilin, ya sa shi a wani kabari da aka fafe a cikin dutse, wadda ba a taɓa sa kowa ba.
54 Og det var Beredelsesdag, og Sabbaten stundede til.
An yi haka ne a Ranar Shirye-shirye, ranar Asabbaci kuma yana dab da farawa.
55 Men Kvinderne, som vare komne med ham fra Galilæa, fulgte efter og saa Graven, og hvorledes hans Legeme blev lagt.
Matan da suka zo tare da Yesu, daga Galili suka bi Yusuf suka ga kabarin, da kuma yadda aka ajiye jikin.
56 Og de vendte tilbage og beredte vellugtende Urter og Salver; og Sabbaten over holdt de sig stille efter Budet.
Sa’an nan, suka koma gida, suka shirya kayan ƙanshi da turare. Amma suka huta a ranar Asabbaci don kiyaye doka.

< Lukas 23 >