< Lukáš 1 >

1 Vážený Teofile! Mnozí přede mnou se snažili pravdivě vylíčit život a dílo Ježíše Krista na základě spolehlivých zpráv jeho žáků a jiných očitých svědků.
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 Nyní jsem se tedy rozhodl i já důkladně přezkoumat, utřídit a sepsat veškeré dostupné zprávy. Vznikl tento spisek, který ti věnuji,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 abys nabyl jistoty, že to, o čem ses již leccos dověděl, je pravda.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 Začnu tím, co se přihodilo židovskému knězi Zachariášovi, který žil v době vlády judského krále Heroda. Zachariáš byl členem jedné ze čtyřiadvaceti kněžských skupin, jejichž povinností bylo dvakrát do roka, vždy po celý týden, přisluhovat při bohoslužbách v jeruzalémském chrámu. Jeho manželka Alžběta pocházela z kněžského rodu Árónova.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Oba byli upřímně zbožní a řídili se svědomitě všemi Božími příkazy a předpisy.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 Byli to již starší lidé a zůstali bezdětní, protože Alžběta byla neplodná.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Jednoho dne šel Zachariáš do chrámu, aby tam splnil svoji kněžskou povinnost.
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 Tentokrát byl vylosován, aby vstoupil do svatyně a tam na oltáři pálil kadidlo.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 Zatím se venku shromáždění lidé modlili, jak bylo v té hodině zvykem.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Tu se knězi po pravé straně oltáře ukázala postava.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 Zachariáš se vyděsil.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 Boží posel ho však uklidňoval: „Neboj se, Zachariáši! Přišel jsem ti oznámit, že Bůh vyslyšel tvé modlitby. Tvoje manželka porodí syna, kterému dáte jméno Jan (Bůh je milostivý).
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 Přinese ti mnoho radosti a mnozí budou vděčni, že se narodil.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 Stane se jedním z velkých Božích mužů. Nedotkne se nikdy vína ani opojného nápoje. Duch svatý ho naplní hned od narození.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 Mnohé z židů přivede zpět k Bohu, jejich skutečnému Pánu.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 Svou duchovní mocí a horlivostí bude připomínat proroka Elijáše. Smíří otce se syny a vzpurným otevře oči pro pravdu. Jako královský posel připraví lidi na příchod Božího vládce.“
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 Zachariáš namítl: „Jak tomu mohu věřit? Vždyť jsem už starý a moje žena také není mladá.“
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 Anděl ho pokáral: „Já jsem Gabriel a přijímám rozkazy přímo od Boha. On sám mě poslal, abych ti vyřídil tyto radostné zprávy.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 Protože jsi však neuvěřil, budeš němý, dokud se má slova ve svůj čas nesplní.“
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 Lidé zatím venku čekali na Zachariáše a už jim bylo divné, že tak dlouho nejde.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 Když se konečně objevil, nemohl promluvit. Posunky jim dal najevo, že měl ve svatyni vidění.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 Když skončil týden jeho chrámové služby, vrátil se domů.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 Brzy na to Alžběta otěhotněla, ale tajila to před veřejností až do pátého měsíce.
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 Radovala se: „Bůh se nade mnou slitoval a sejmul ze mne pohrdání a neúctu lidí.“
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Asi půl roku po Zachariášově vidění poslal Bůh anděla Gabriela do galilejského městečka Nazaretu
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 k dívce jménem Marie. Byla snoubenkou Josefa, který pocházel z Davidova královského rodu.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 Anděl ji oslovil: „Blahopřeji ti, Marie, Bůh ze všech žen vyvolil právě tebe k velikému úkolu!“
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 Jeho slova ji znepokojila a nechápala jejich smysl.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 Posel pokračoval. „Neboj se, Marie. Bůh ti chce nevídaně požehnat.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 Narodí se ti syn a dáš mu jméno Ježíš (Bůh vysvobozuje).
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 Nebude to obyčejný člověk, ale právem bude nazýván ‚Syn Nejvyššího‘.
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 Usedne na trůn Davidův a bude nejen vládce Izraele, ale založí království, které nikdy neskončí.“ (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Marie namítla: „Jak se mi může narodit dítě? Vždyť nežiji s mužem!“
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 Anděl jí řekl: „Sám Stvořitel na tobě projeví svou moc. Duch svatý to způsobí, a tak tvé dítě bude svatý Boží Syn. U Boha není nic nemožného.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 Vždyť i tvá příbuzná Alžběta, po celý život neplodná, bude mít nyní ve svém stáří syna. Již za tři měsíce se jí narodí.“
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Marie na to řekla: „Chci přijmout, co mi Bůh ukládá. Ať se tedy stane, jak jsi řekl.“Pak anděl odešel.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Brzy nato se Marie vydala do judských hor, do města, kde žil Zachariáš s Alžbětou.
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 Když k nim vešla a pozdravila, pocítila Alžběta, jak se její dítě živě pohnulo. V tu chvíli Alžbětu nadchl Boží Duch
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 a zvolala: „Marie, Bůh tě vyvolil mezi všemi ženami a tvůj syn bude veliký dar lidem.
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 Jaká je to pro mne čest, že mne navštívila matka mého Pána!
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 Sotva jsem zaslechla tvůj pozdrav, děťátko ve mně radostí poskočilo.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 Jak je dobře, že jsi uvěřila Božím slibům. On je všechny splní.“
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Nato se Marie začala modlit: „Celým srdcem chválím Pána
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 a raduji se v Bohu, svém Spasiteli.
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 Mne, nepatrné, si povšiml. Lidé ze všech národů si mne budou vděčně připomínat pro velké věci, které mi Bůh prokázal. Je mocný a svatý,
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 ale neustále se slitovává nad těmi, kteří ho ctí v kterékoliv době.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 Vztahuje svoji mocnou ruku, aby mařil plány pyšných,
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 aby sesazoval mocné z trůnů, pozvedal ponížené,
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 sytil hladové dobrými věcmi a bohaté propouštěl s prázdnýma rukama.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 Ujímá se svého lidu, Izraele, protože slíbil našim otcům,
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 Abrahamovi i jeho potomkům, že k nim bude na věky milosrdný.“ (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 Marie pobyla u Alžběty asi tři měsíce a pak se vrátila domů.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Přišel Alžbětin čas a narodil se jí syn.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 Všichni sousedé a příbuzní se radovali, že ji Bůh tak obšťastnil.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 Sešli se osmého dne, kdy podle zákona bývali chlapci obřezáváni. Všichni předpokládali, že dítě se bude jmenovat po otci Zachariáš.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 Alžběta však chtěla, aby se jmenoval Jan.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 Namítali: „Ale vždyť se tak ve vaší rodině nikdo nejmenoval.“
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 Žádali, aby se k tomu vyjádřil otec.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 Ten vzal tabulku a k překvapení všech napsal: „Jeho jméno je Jan.“
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 A tehdy se jeho ústa zase otevřela a prvními slovy děkoval Bohu.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 Užaslí sousedé pochopili, že se tu děje něco mimořádného, a zpráva o tom se roznesla po judských horách.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 Kdo ji slyšel, uvažoval, co s tím dítětem Bůh zamýšlí. Všichni viděli, že ho provází Boží moc.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 Duch svatý vnukl Zachariášovi tato prorocká slova:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 „Chvála Pánu, Bohu Izraele, že přichází svému lidu na pomoc a vysvobozuje ho.
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 Posílá nám mocného Zachránce z rodu krále Davida,
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 kterého již dávno ústy svých proroků ohlašoval. (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 Ten nás vytrhne z rukou nepřátel a všech, kteří nás nenávidí.
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 Dnes se Bůh láskyplně přiznává k našim otcům a ke své smlouvě s nimi.
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 Vždyť se zavázal Abrahamovi, že jednou budeme sloužit Bohu po celý život, zbaveni útlaku a strachu, očištěni a poslušni. A ty, synu, budeš prorokem Nejvyššího. Připravíš cestu Božímu Synu: Lidem budeš ohlašovat, že je přichází zachránit a odpustit jim všechna provinění. V něm k nám přichází Bůh plný slitovné lásky. Slunce spásy již vychází,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 aby zazářilo všem, kdo žijí ve tmách a ve stínu smrti, a osvítilo nám cestu ke smíření s Bohem!“
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 Chlapec Jan se dobře rozvíjel tělesně i duševně. Později odešel na poušť, kde žil v ústraní až do chvíle, kdy vystoupil se svým poselstvím před veřejností.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Lukáš 1 >