< Žalmy 7 >

1 Osvědčení neviny Davidovy, o čemž zpíval Hospodinu z příčiny slov Chusi syna Jeminova. Hospodine Bože můj, v toběť doufám, vysvoboď mne ode všech protivníků mých, a vytrhni mne,
Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
2 Aby neuchvátil jako lev duše mé, a neroztrhal, když by nebyl, kdo by vysvobodil.
in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
3 Hospodine Bože můj, učinil-li jsem to, jest-li nepravost při mně,
Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
4 Činil-li jsem zle tomu, kdož se ke mně pokojně choval, (nýbrž spomáhal jsem protivícímu se mi bez příčiny),
in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
5 Nechať stihá nepřítel duši mou, i popadne, a pošlapá na zemi život můj, a slávu mou v prach uvede. (Sélah)
to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
6 Povstaň, Hospodine, v hněvě svém, vyvyš se proti vzteklostem mých nepřátel, a prociť ke mně, nebo jsi soud nařídil.
Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
7 I shrne se k tobě shromáždění lidí; pro ně tedy u výsost navrať se zase.
Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
8 Hospodin souditi bude lidi. Sudiž mne, Hospodine, podlé spravedlnosti mé, a podlé nevinnosti mé, kteráž při mně jest.
bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
9 Ó by již k skončení přišla nešlechetnost bezbožných, spravedlivého pak abys utvrdil ty, kterýž zkušuješ srdce a ledví, Bože spravedlivý.
Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
10 Bůh jest štít můj, kterýž spaseny činí upřímé srdcem.
Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
11 Bůh jest soudce spravedlivý, Bůh silný hněvá se na bezbožného každý den.
Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
12 Neobrátí-li se, naostříť meč svůj; lučiště své natáhl, a naměřil je.
In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
13 Připravil sobě i zbroj smrtelnou, střely své proti škůdcím přistrojil.
Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
14 Aj, rodí nepravost; nebo počav těžkou bolest, urodí lež.
Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
15 Jámu kopal, i vykopal ji, ale padne do dolu, kterýž přistrojil.
Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
16 Obrátíť se usilování jeho na hlavu jeho, a na vrch hlavy jeho nepravost jeho sstoupí.
Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
17 Slaviti budu Hospodina podlé spravedlnosti jeho, a žalmy zpívati jménu Hospodina nejvyššího.
Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.

< Žalmy 7 >