< Lukáš 8 >

1 I stalo se potom, že on chodil po městech a po městečkách, káže a zvěstuje království Boží, a dvanácte s ním.
Bayan wannan sai Yesu ya zazzaga gari da ƙauye, yana wa’azin bisharar mulkin Allah. Sha Biyun nan kuwa suna tare da shi,
2 I ženy některé, kteréž byl uzdravil od duchů zlých a od nemocí: Maria, kteráž slove Magdaléna, z níž bylo sedm ďáblů vyšlo,
da kuma waɗansu mata waɗanda aka warkar da su daga cututtukansu, da kuma mugayen ruhohi. Cikinsu akwai Maryamu (wadda ake kira Magdalin) wadda aljanu bakwai suka fito daga cikinta.
3 A Johanna manželka Chuzova, úředníka Heródesova, a Zuzanna, a jiné mnohé, kteréž posluhovaly jemu z statků svých.
Da Yowanna matar Kuza, manajan iyalin Hiridus; da Suzana; da waɗansu mata da yawa. Waɗannan mata suna taimaka musu cikin hidima, daga cikin abin da suke da shi na zaman gari.
4 Když se pak scházel zástup mnohý, a z měst hrnuli se k němu, mluvil v podobenství:
Yayinda taron mai girma na taruwa, mutane kuma daga garuruwa dabam-dabam suna zuwa wurin Yesu, sai ya ba da wannan misali ya ce,
5 Vyšel rozsevač, aby rozsíval símě své. A když on rozsíval, jedno padlo podlé cesty, i pošlapáno jest, a ptáci nebeští zzobali je.
“Wani manomi ya fita domin ya shuka irinsa. Da yana watsa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, aka tattaka su, tsuntsayen sararin sama kuma suka cinye su.
6 A jiné padlo na skálu, a vzešlé uvadlo, proto že nemělo vláhy.
Waɗansu suka fāɗi a kan dutse, da suka tsira sai suka yanƙwane don babu ruwa a wurin.
7 Jiné pak padlo mezi trní, a spolu zrostlé trní udusilo je.
Waɗansu kuma suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma tare, sai ƙayan suka shaƙe su.
8 A jiné padlo v zemi dobrou, a když vzešlo, učinilo užitek stý. To pověděv, volal: Kdo má uši k slyšení, slyš.
Waɗansu kuma har yanzu, suka fāɗi a ƙasa mai kyau, suka yi girma, suka ba da amfani riɓi ɗari-ɗari, fiye da abin da aka shuka.” Da faɗin haka sai ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
9 I otázali se ho učedlníci jeho, řkouce: Jaké jest to podobenství?
Almajiransa suka tambaye shi ma’anar wannan misali.
10 A on řekl: Vám dáno jest znáti tajemství království Božího, ale jiným v podobenství, aby hledíce, neviděli, a slyšíce, nerozuměli.
Sai ya ce, “Ku ne aka ba sanin asirin mulkin Allah, amma ga sauran mutane kam, ina magana da misalai, saboda, “‘ko da yake suna kallo, ba za su gani ba, ko da yake suna ji, ba za su gane ba.’
11 Jestiť pak podobenství toto: Símě jest slovo Boží.
“Ga ma’anar misalin, irin, shi ne maganar Allah.
12 A kteréž padlo podlé cesty, jsou ti, kteříž slyší, a potom přichází ďábel, a vynímá slovo z srdce jejich, aby nevěříce, spaseni nebyli.
Waɗanda suka fāɗi a kan hanya su ne mutanen da suka ji, amma Iblis, yakan zo ya ɗauke maganar daga zuciyarsu, don kada su gaskata, su sami ceto.
13 Ale kteříž na skálu, ti když slyší, s radostí přijímají slovo, ale ti kořenů nemají; ti na čas věří, a v čas pokušení odstupují.
Na kan dutse kuwa, su ne da jin maganar, sukan karɓa da murna, amma ba su da saiwa. Sukan gaskata na ɗan lokaci, amma lokacin gwaji, sai su ja da baya.
14 Kteréž pak mezi trní padlo, tiť jsou, kteříž slyší, ale po pečování a zboží a rozkošech života jdouce, bývají udušeni, a nepřinášejí užitku.
Irin da suka fāɗi a cikin ƙaya kuwa, su ne mutanen da suka ji, amma a kwana a tashi, tunanin kayan duniya, da neman arziki, da son jin daɗi, sukan hana su ba da’ya’ya.
15 Ale kteréž v zemi dobrou, ti jsou, kteříž v srdci ctném a dobrém, slyšíce slovo, zachovávají, a užitek přinášejí v trpělivosti.
Amma irin da suka fāɗi a ƙasa mai kyau kuwa, su ne mutane masu kyakkyawar zuciya, mai kyau, da suka ji, suka riƙe, suka kuma jimre har suka ba da’ya’ya.”
16 Žádný pak rozsvítě svíci, nepřikrývá jí nádobou, ani staví pod postel, ale na svícen staví, aby ti, kteříž vcházejí, světlo viděli.
“Ba mai ƙuna fitila sa’an nan ya ɓoye ta a cikin tulu, ko kuma ya sa ta a ƙarƙashin gado ba. A maimakon haka, yakan sa ta a kan wurin ajiye fitila, saboda mutane masu shigowa su ga haske.
17 Nebo nic není tajného, což by nemělo býti zjeveno, ani co ukrytého, což by nemělo poznáno býti, a na světlo vyjíti.
Ba abin da yake ɓoye da ba za a fallasa ba. Kuma ba abin da yake rufe, da ba za a sani ba, ko a fitar da shi a fili ba.
18 Protož vizte, jak slyšíte. Nebo kdož má, tomu bude dáno, a kdo nemá, i to, což domnívá se míti, bude odjato od něho.
Saboda haka, ku yi tunani da kyau yadda kuke saurara. Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda ba shi da shi kuma, abin da yake tsammani yana da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
19 Tedy přišli k němu matka a bratří jeho, ale nemohli ho dojíti pro zástup.
Sai uwar Yesu da’yan’uwansa suka zo, domin su gan shi, amma ba su iya zuwa kusa da shi ba, saboda taron.
20 I pověděli mu, řkouce: Matka tvá a bratří tvoji stojí vně, chtíce tebe viděti.
Sai wani ya faɗa masa cewa, “Ga uwarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje suna so su gan ka.”
21 A on odpověděv, řekl jim: Matka má a bratří moji jsou ti, kteříž slovo Boží slyší a plní je.
Ya amsa ya ce, “Mahaifiyata da’yan’uwana, su ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma aikata ta.”
22 Stalo se pak v jeden den, že on vstoupil na lodí i učedlníci jeho. I řekl jim: Přeplavme se přes jezero. I pustili se.
Wata rana Yesu ya ce wa almajiransa, “Mu haye zuwa wancan gefen tafkin.” Sai suka shiga jirgin ruwa suka fara tafiya.
23 A když se plavili, usnul. Tedy přišel vítr bouřlivý na jezero, a lodí se naplňovala, tak že v nebezpečenství byli.
Da suna cikin tafiya, sai barci ya kwashe shi. Sai wata babban iska ta taso kan tafkin, har ruwa ya fara shiga cikin jirgin. Suka shiga babban hatsari.
24 I přistoupivše, zbudili ho, řkouce: Mistře, Mistře, hyneme. A on procítiv, přimluvil větru a zdutí vod. I spokojili se, a stalo se utišení.
Almajiran suka je suka tashe shi daga barci, suka ce, “Ubangiji, Ubangiji, za mu nutse!” Ya tashi ya kwaɓe iskar da kuma haukar ruwan. Sai ruwan da iskar suka natsu. Kome ya yi tsit.
25 I řekl jim: Kdež jest víra vaše? Kteřížto bojíce se, podivili se, vespolek řkouce: I kdo jest tento, že i větrům přikazuje i vodám, a poslouchají ho?
Sai ya tambayi almajiransa, “Ina bangaskiyarku?” A cikin tsoro da mamaki, suka ce wa junansu, “Wane ne wannan? Yana ba da umarni ga iska da ruwa ma, kuma suna biyayya da shi?”
26 I přeplavili se do krajiny Gadarenské, kteráž jest proti Galilei.
Suka shiga jirgin ruwa zuwa yankin Gerasenawa da yake a hayin tafkin, daga wajen Galili.
27 A když vystoupil na zemi, potkal jej muž nějaký z města, kterýž měl ďábelství od mnoha časů, a rouchem se neodíval, ani v domě nebýval, ale v hrobích.
Da Yesu ya sauka daga jirgin, sai ga wani mutum mai aljanu daga garin. Mutumin ya daɗe bai sa tufafi ba, kuma ba ya zama a gida. Yana zama a cikin kaburbura.
28 Uzřev pak Ježíše a zkřikna, padl před ním, a hlasem velikým řekl: Co jest tobě do mne, Ježíši, Synu Boha nejvyššího? Prosím tebe, netrap mne.
Da ya ga Yesu, sai mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi, ya fāɗi a gabansa, yana ihu cewa, “Ina ruwanka da ni, Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ina roƙonka, kada ka ba ni wahala!”
29 Nebo přikazoval tomu duchu nečistému, aby vyšel z toho člověka. Po mnohé zajisté časy jím lomcoval, tak že býval ukován řetězy, a v poutech ostříhán, ale on polámaje okovy, býval od ďábelství puzen na poušť.
Gama Yesu ya riga ya umarci mugun ruhun ya fita daga mutumin. Sau da yawa mugun ruhun ya sha kamunsa. Ko da yake akan daure shi hannu da ƙafa, da sarƙa, a kuma yi gadinsa, amma yakan tsinke sarƙoƙinsa, aljanun kuma su kore shi zuwa wuraren kaɗaici, inda ba kowa.
30 I otázal se ho Ježíš, řka: Jakť říkají? A on řekl: Množství. Nebo bylo mnoho ďáblů vešlo do něho.
Yesu ya tambaye shi, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa, “Tuli,” gama aljanu masu ɗumbun yawa ne suna cikinsa.
31 Tedy prosili ho, aby jim nepřikazoval odtud odjíti do propasti. (Abyssos g12)
Suka yi ta roƙonsa kada yă umarce su su shiga ramin Abis. (Abyssos g12)
32 Bylo pak tu veliké stádo vepřů, kteříž se pásli na hoře. I prosili ho, aby jim dopustil do nich vjíti. I dopustil jim.
A wurin kuwa, akwai babban garken aladu da suke kiwo a gefen tudu. Aljanun suka roƙi Yesu ya bar su, su shiga cikin aladun, ya kuwa yardar musu.
33 I vyšedše ďáblové z toho člověka, vešli do vepřů, i hnalo se to stádo prudce s vrchu do jezera, a ztonulo.
Da aljanun suka fita daga cikin mutumin, sai suka shiga cikin aladun. Garken kuma ya gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, kuma suka nutse.
34 A viděvše pastýři, co se stalo, utekli, a šedše, vypravovali to v městě i po vsech.
Da masu kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka ruga da gudu zuwa garin da kewaye suka kai labari.
35 I vyšli, aby viděli, co se stalo. I přišli k Ježíšovi, a nalezli člověka toho, z kteréhož ďáblové vyšli, oděného a majícího rozum, an sedí u noh Ježíšových. I báli se.
Mutanen kuma suka fito don su ga abin da ya faru. Da suka iso wurin Yesu, sai suka tarar da mutumin da aljanun suka fita daga cikinsa, yana zaune kusa da Yesu sanye da tufafi, kuma cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
36 A vypravovali jim také ti, kteříž byli viděli, kterak jest ten vyproštěn, kterýž ďábelství měl.
Waɗanda suka ga abin da faru, suka gaya wa mutanen yadda aka warkar da mai aljanun.
37 I prosilo ho všecko množství té okolní krajiny Gadarenských, aby odšel od nich; nebo bázní velikou naplněni byli. A on vstoupiv na lodí, navrátil se.
Sai dukan mutanen yankin Gerasenawa suka roƙi Yesu ya bar su, don sun tsorata sosai. Sai Yesu ya shiga jirgin ruwa ya tafi.
38 Prosil ho pak muž ten, z kteréhož ďáblové vyšli, aby s ním byl. Ale Ježíš propustil ho, řka:
Mutumin da aka fitar da aljanun daga cikinsa, ya roƙi Yesu don yă tafi tare da shi, amma Yesu ya sallame shi ya ce,
39 Navrať se do domu svého, a vypravuj, kterak veliké věci učinil tobě Bůh. I odšel, po všem městě vypravuje, jak veliké věci učinil jemu Ježíš.
“Koma gida, ka shaida babban alherin da Allah ya yi maka.” Sai mutumin ya tafi yana faɗin abin da Yesu ya yi masa a duk garin.
40 Stalo se pak, když se navrátil Ježíš, že přijal jej zástup; nebo všickni očekávali ho.
Da Yesu ya koma, taron suka marabce shi, don dā ma duk suna jiransa.
41 A aj, přišel muž, kterémuž jméno bylo Jairus, a ten byl kníže školy. I padna k nohám Ježíšovým, prosil ho, aby všel do domu jeho.
Sai wani mutum mai suna Yayirus, wani mai mulkin majami’a, ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, yana roƙonsa ya zo gidansa,
42 Nebo měl dceru jedinou, asi ve dvanácti letech, a ta umírala. A když šel, tiskli jej zástupové.
domin diyarsa ɗaya tak, wadda ta kai shekara goma sha biyu, tana bakin mutuwa. Da Yesu yake kan hanyarsa, taron mutane masu yawa suka yi ta matsa shi a kowane gefe.
43 Tedy žena, kteráž nemoc svou trpěla od let dvanácti, a byla na lékaře vynaložila všecken statek, a od žádného nemohla uzdravena býti,
A wurin kuwa, akwai wata mace wadda tana da ciwon zubar da jini, har na shekara goma sha biyu, amma babu wanda ya iya warkar da ita.
44 Přistoupivši po zadu, dotkla se podolka roucha jeho, a hned přestala nemoc její.
Sai ta zo ta bayansa, ta taɓa bakin rigarsa. Nan da nan, zubar da jininta ya tsaya.
45 I řekl Ježíš: Kdo jest, ješto se mne dotekl? A když všickni zapírali, řekl Petr, a kteříž s ním byli: Mistře, zástupové tebe tisknou a tlačí, a pravíš: Kdo se mne dotekl?
Yesu ya yi tambaya, “Wa ya taɓa ni?” Bayan kowa ya yi musu, sai Bitrus ya ce, “Ubangiji, ai, mutane da yawa suna matsinka ta kowane gefe.”
46 I řekl Ježíš: Dotekl se mne někdo, nebo poznal jsem já, že moc ode mne vyšla.
Amma Yesu ya ce, “Wani ya taɓa ni, na san cewa iko ya fita daga wurina.”
47 A viduci ta žena, že by tajno nebylo, třesuci se, přistoupila a padla před ním, a pro kterou příčinu dotkla se ho, pověděla jemu přede vším lidem, a kterak jest hned uzdravena.
Sai macen, da ta ga ba halin ɓoyewa, sai ta fita, jikinta na rawa, ta fāɗi a gabansa. A gaban dukan mutanen, ta faɗi dalilin da ya sa ta taɓa shi, da yadda ta warke nan take.
48 A on řekl jí: Dobré mysli buď, dcero, víra tvá tebe uzdravila. Jdiž u pokoji.
Sai Yesu ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya.”
49 A když on ještě mluvil, přišel jeden od knížete školy, řka jemu: Umřela dcera tvá, nezaměstknávej Mistra.
Yayinda Yesu na cikin magana har yanzu, sai ga wani daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’ar ya ce, “Kada ka ƙara damun malam, diyarka ta rasu.”
50 Ale Ježíš uslyšav to, odpověděl jemu: Neboj se, věř toliko, a zdrávať bude.
Da Yesu ya ji wannan, sai ya ce wa Yayirus, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata, za a kuma warkar da ita.”
51 A všed do domu, nedopustil s sebou vjíti žádnému, než Petrovi a Jakubovi a Janovi, a otci a mateři té děvečky.
Da ya iso gidan Yayirus, sai ya hana kowa yă bi shi cikin ɗakin, sai dai Bitrus, da Yohanna, da Yaƙub, da kuma mahaifin da mahaifiyar.
52 Plakali jí pak všickni a kvílili. A on řekl: Neplačtež. Neumřelať, ale spí.
Ana cikin haka, dukan mutanen kuma sai kuka da makoki suke ta yi, domin yarinyar. Sai Yesu ya ce, “Ka daina yin kuka, ba tă mutu ba, tana barci ne.”
53 I posmívali se jemu, vědouce, že umřela.
Sai suka yi masa dariya, da yake sun san cewa, ta mutu.
54 On pak vyhnav ven všecky, a ujav ruku její, zvolal, řka: Děvečko, vstaň.
Amma Yesu ya kama ta a hannu ya ce, “Diyata, tashi.”
55 I navrátil se duch její, a vstala hned. I kázal jí dáti jísti.
Ruhunta ya dawo, kuma ta tashi, nan take. Yesu ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.
56 I divili se náramně rodičové její. A on jim kázal, aby žádnému nepravili o tom, co se bylo stalo.
Iyayenta suka yi mamaki, amma ya ba su umarni kada su faɗa wa kowa abin da ya faru.

< Lukáš 8 >