< Jeremiáš 11 >

1 Slovo, kteréž se stalo k Jeremiášovi od Hospodina, řkoucí:
Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji.
2 Slyšte slova smlouvy této, kteráž byste mluvili mužům Judským, a obyvatelům Jeruzalémským,
“Ka saurari zancen wannan alkawari ka kuma faɗe su ga mutanen Yahuda da kuma waɗanda suke zaune a Urushalima.
3 A rci jim: Takto praví Hospodin Bůh Izraelský: Zlořečený ten člověk, kterýž by neposlechl slov smlouvy této,
Ka faɗa musu cewa ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa, ‘La’ananne ne wanda bai kula da zancen alkawarin nan ba,
4 Kterouž jsem vydal otcům vašim tehdáž, když jsem je vyvedl z země Egyptské, z peci železné, řka: Poslouchejte hlasu mého, a čiňte to všecko, tak jakž přikazuji vám, i budete lidem mým, a já budu Bohem vaším,
zancen da na umarci kakanni-kakanninku sa’ad da na fitar da su daga Masar, daga cikin tanderun narkewar ƙarfe.’ Na ce, ‘Ku yi mini biyayya ku kuma aikata kowane abin da na umarce ku, za ku kuwa zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnku.
5 Abych splnil přísahu, kterouž jsem učinil otcům vašim, že jim dám zemi oplývající mlékem a strdí, jakž dnešní den jest. Jemuž odpověděv, řekl jsem: Amen, Hospodine.
Sa’an nan zan cika rantsuwar da na yi wa kakanni-kakanninku, da zan ba su ƙasa mai zub da madara da kuma zuma’ ƙasar da kuka mallaka a yau.” Sai na amsa na ce, “Amin, Ubangiji.”
6 Potom řekl mi Hospodin: Ohlašuj všecka slova tato po městech Judských, a po ulicích Jeruzalémských, řka: Slyšte slova smlouvy této, a čiňte je.
Sai Ubangiji ya ce mini, “Ka yi shelar dukan maganan nan a biranen Yahuda da titunan Urushalima duka cewa, ‘Su saurari zancen alkawarin nan, su aikata.
7 Nebo častokrát osvědčoval jsem se otcům vašim, od toho dne, jakž jsem je vyvedl z země Egyptské, až do dne tohoto; ráno přivstávaje a osvědčuje se, říkával jsem: Poslouchejte hlasu mého.
Daga lokacin da na fitar da kakanni-kakanninku daga Masar har yă zuwa yau, na gargaɗe su sau da sau, ina cewa, “Ku yi mini biyayya.”
8 Ale neposlouchali, aniž naklonili ucha svého, nýbrž chodil jeden každý po zdání srdce svého zlého. Pročež uvedl jsem na ně všecka slova smlouvy této, kterouž jsem přikázal plniti, ale neplnili.
Amma ba su kasa kunne ko su saurara ba, a maimako, sai suka bi taurinkai na mugayen zukatansu. Saboda haka na kawo musu dukan la’anonin alkawarin da na riga na umarce su, su bi amma ba su kiyaye ba.’”
9 Tehdy řekl mi Hospodin: Nalézá se spiknutí mezi muži Judskými, a mezi obyvateli Jeruzalémskými.
Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, “Akwai maƙarƙashiya a cikin mutanen Yahuda da waɗanda suke zaune a Urushalima.
10 Obrátili se k nepravostem otců svých starých, kteříž nechtěli poslouchati slov mých. Tolikéž tito chodí za bohy cizími, sloužíce jim; dům Izraelský a dům Judský zrušili smlouvu mou, kterouž jsem učinil s otci jejich.
Sun koma ga zunuban kakanni kakanninsu, waɗanda suka ƙi su saurari maganata. Suka bi waɗansu alloli don su bauta musu. Da gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda duk sun take alkawarin da na yi da kakanni kakanninsu.
11 Protož takto praví Hospodin: Aj, já uvedu na ně zlé, z něhož nebudou moci vyjíti. By pak volali ke mně, nevyslyším jich.
Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Zan kawo masifa a kansu wadda ba za su iya tsere mata ba. Ko da yake suna kuka gare ni, ba zan saurare su ba.
12 I půjdou města Judská i obyvatelé Jeruzalémští, a budou volati k bohům těm, kterýmž kadí, ale nikoli nevysvobodí jich v čas bídy jejich,
Garuruwan Yahuda da mutanen Urushalima za su tafi su yi kuka ga allolin da suke ƙona wa turare, amma ba za su taimake su ba sam sa’ad da masifar ta auku.
13 Ačkoli podlé počtu měst máš bohy své, ó Judo, a podlé počtu ulic Jeruzalémských nastavěli jste oltářů ohavnosti té, oltářů, na nichž byste kadili Bálovi.
Kuna da alloli masu yawa yadda kuke da garuruwa, ya Yahuda; kuma bagadan da kuka yi don ƙona turare wa allahn nan Ba’al abin kunya sun yi yawa kamar titunan Urushalima.’
14 Protož ty nemodl se za lid tento, aniž pozdvihuj za ně hlasu a modlitby; neboť nikoli nevyslyším jich v ten čas, když by volali ke mně příčinou svého zlého.
“Kada ka yi addu’a domin wannan mutane ko ka miƙa wani roƙo ko kuka dominsu, domin ba zan saurara ba sa’ad da suka kira gare ni a lokacin ƙuncinsu.
15 Co jest milému mému do mého domu, poněvadž nestydatě páše nešlechetnosti s mnohými, a oběti svaté odešly od tebe, a že v zlosti své pléšeš?
“Mene ne ƙaunatacciyata take yi a haikali da yake ta yin ƙulle-ƙullen mugayen makircinta tare da mutane masu yawa? Tsarkakar nama zai iya kawar da hukuncinki? Sa’ad da kike yin muguntarki sa’an nan ki yi farin ciki.”
16 Byltě Hospodin nazval jméno tvé olivou zelenající se, pěknou pro ovoce ušlechtilé, ale s zvukem bouře veliké zapálí ji s hůry, když polámí ratolesti její.
Ubangiji ya kira ki itacen zaitun mai inuwa kyakkyawa mai’ya’ya masu kyau. Amma da ƙugin babbar hadari zai cinna masa wuta, rassansa za su kakkarye.
17 Nebo Hospodin zástupů, kterýž tě byl štípil, vyřkl zlé proti tobě, pro nešlechetnost domu Izraelského a domu Judského, kterouž mezi sebou páchali, aby mne popouzeli, kadíce Bálovi.
Ubangiji Maɗaukaki, wanda ya dasa ki, ya furta miki masifa, domin gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda sun aikata mugunta suka kuma tsokane ni in yi fushi ta wurin ƙona wa Ba’al turare.
18 Hospodin zajisté oznámil mi, i dověděl jsem se. Tehdáž jsi mi ukázal předsevzetí jejich,
Domin Ubangiji ya bayyana mini maƙarƙashiyarsu, na santa, gama a wannan lokaci ya nuna mini abin da suke yi.
19 Když jsem já byl jako beránek a volček, kterýž veden bývá k zabití. Nebo nevěděl jsem, by proti mně rady skládali: Zkazme strom s ovocem jeho, a vyhlaďme jej z země živých, aby jméno jeho nebylo připomínáno více.
Na kasance kamar ɗan rago marar faɗa wanda aka kai mayanka; ban gane cewa sun ƙulla mini maƙarƙashiya, suna cewa, “Bari mu lalatar da itacen duk da’ya’yansa; bari mu datse shi daga ƙasar masu rai, har da ba za a ƙara tunawa da sunansa ba.”
20 Ale ó Hospodine zástupů, soudce spravedlivý, kterýž zkušuješ ledví i srdce, nechť se podívám na pomstu tvou nad nimi; nebo jsem tobě zjevil při svou.
Amma, ya Ubangiji Maɗaukaki, kai da kake yin shari’a da adalci kake gwada zuciya da kuma tunani, ka sa in ga sakayyar da za ka yi musu, gama a gare ka na danƙa maganata.
21 Protož takto praví Hospodin o Anatotských, kteříž hledají bezživotí tvého, říkajíce: Neprorokuj ve jménu Hospodinovu, abys neumřel v ruce naší:
“Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa game da mutanen Anatot, waɗanda suke neman ranka suna kuma cewa, ‘Kada ka yi annabci da sunan Ubangiji in ba haka za ka mutu a hannunmu’
22 Protož takto praví Hospodin zástupů: Aj, já navštívím je. Mládenci zbiti budou mečem, synové jejich i dcery jejich zemrou hladem,
saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, ‘Zan hukunta su. Samarinsu za su mutu ta wurin takobi,’ya’yansu maza da mata kuwa ta wurin yunwa.
23 A nebudou míti potomků, když uvedu zlé na Anatotské, času toho, v němž je navštívím.
Babu raguwar da za a bar musu, domin zan kawo masifa a kan mutanen Anatot a shekarar hukuncinsu.’”

< Jeremiáš 11 >