< 2 Královská 13 >

1 Léta třimecítmého Joasa syna Ochoziáše, krále Judského, kraloval Joachaz syn Jéhu nad Izraelem v Samaří sedmnácte let.
A shekara ta ashirin da uku ta Yowash ɗan Ahaziya, sarkin Yahuda, Yehoyahaz ɗan Yehu, ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuwa yi mulki shekaru goma sha bakwai.
2 A činil to, což jest zlého před očima Hospodinovýma; nebo následoval hříchů Jeroboáma syna Nebatova, kterýž přivedl k hřešení Izraele, a neuchýlil se od nich.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji ta wurin bin zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai kuwa guje musu ba.
3 I rozhněvala se prchlivost Hospodinova na Izraele, a vydal je v ruku Hazaele krále Syrského, a v ruku Benadada syna Hazaelova po všecky ty dny.
Saboda haka fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Isra’ila, kuma da daɗewa ya sa su a ƙarƙashin ikon Hazayel sarkin Aram da Ben-Hadad ɗansa.
4 Ale když se modlil Joachaz Hospodinu, vyslyšel jej Hospodin. Viděl zajisté trápení Izraelské, že je ssužoval král Syrský.
Sai Yehoyahaz ya nemi tagomashin Ubangiji, Ubangiji kuwa ya saurare shi, domin ya gan irin matsin da sarkin Aram yake yi wa Isra’ila.
5 Protož dal Hospodin Izraelovi vysvoboditele, a vyšli z ruky Syrských, i bydlili synové Izraelští v příbytcích svých jako kdy prvé.
Sai Ubangiji ya tā da mai ceto wa Isra’ila, suka kuma kuɓuta daga ikon Aram. Ta haka Isra’ilawa suka yi zama a gidajensu yadda suka yi a dā.
6 Však proto neodstoupili od hříchů domu Jeroboámova, kterýž přivedl k hřešení Izraele, nýbrž v nich chodili, ano i háj ještě zůstával v Samaří,
Sai dai ba su bar yin zunuban gidan Yerobowam ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata; suka ci gaba da yinsu. Haka ma, ginshiƙin Ashera ta kasance a tsaye a cikin Samariya.
7 Ačkoli nezanechal Joachazovi lidu, kromě padesáti jízdných a desíti vozů a desíti tisíců pěších; nebo je pohubil král Syrský, a setřel je jako prach při mlácení.
Ba abin da ya rage na rundunar Yehoyahaz sai mahayan dawakai hamsin, kekunan yaƙi goma da kuma sojoji ƙasa dubu goma. Gama sarkin Aram ya hallaka sauran, ya kuma yi kaca-kaca da su kamar ƙura a masussuka.
8 O jiných pak činech Joachazových, a cožkoli činil, i o síle jeho zapsáno jest v knize o králích Izraelských.
Game da sauran ayyukan mulkin Yehoyahaz, dukan abubuwan da ya yi da kuma nasarorinsa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
9 I usnul Joachaz s otci svými, a pochovali ho v Samaří. Kraloval pak Joas syn jeho místo něho.
Yehoyahaz ya huta da kakanninsa, aka binne shi a Samariya, Yehowash ɗansa kuma ya gāje shi.
10 Léta třidcátého sedmého Joasa krále Judského kraloval Joas syn Joachazův nad Izraelem v Samaří šestnácte let.
A shekaru talatin da bakwai ta Yowash sarkin Yahuda, Yehowash ɗan Yehoyahaz ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki shekaru goma sha shida.
11 A činil to, což jest zlého před očima Hospodinovýma, neuchýliv se od žádných hříchů Jeroboáma syna Nebatova, kterýž přivedl k hřešení Izraele, ale chodil v nich.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, bai juya ga barin zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, ya ci gaba da yinsu.
12 O jiných pak činech Joasových, i cožkoli činil, i o síle jeho, kterouž bojoval proti Amaziášovi králi Judskému, zapsáno jest v knize o králích Izraelských.
Game da sauran ayyukan mulkin Yowash, da dukan abubuwan da ya yi, da kuma nasarorinsa, haɗe da yaƙin da ya yi da Amaziya sarkin Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
13 I usnul Joas s otci svými, a sedl Jeroboám na stolici jeho. I pochován jest Joas v Samaří s králi Izraelskými.
Yowash ya huta da kakanninsa, Yerobowam kuwa ya gāje shi. Aka binne Yehowash a Samariya tare da sarakunan Isra’ila.
14 Elizeus pak roznemohl se nemocí těžkou, v kteréž i umřel. A přišel byl k němu Joas král Izraelský, a pláče nad ním, řekl: Otče můj, otče můj, vozové Izraelští a jízdo jeho!
To, Elisha ya kamu da ciwon da ya kashe shi. Yowash sarkin Isra’ila ya gangara don yă gan shi, ya kuma yi kuka dominsa. Ya yi kuka yana cewa, “Babana! Babana, keken yaƙin Isra’ila da mahayan dawakanta!”
15 Ale Elizeus řekl jemu: Vezmi lučiště a střely. I vzav, přinesl k němu lučiště a střely.
Elisha ya ce wa Yehowash, “Ka samo baka da kibiyoyi,” ya kuwa yi haka.
16 Řekl dále králi Izraelskému: Vezmi v ruku svou lučiště. I vzal je v ruku svou. Vložil také Elizeus ruce své na ruce královy.
Sai ya ce wa Yehowash sarkin Isra’ila, “Ka ɗauki baka a hannunka.” Da ya ɗauka, sai Elisha ya sa hannunsa a hannuwan sarki.
17 A řekl: Otevři to okno k východu. A když otevřel, řekl Elizeus: Střeliž. I střelil. Tedy řekl: Střela spasení Hospodinova a střela vysvobození proti Syrským; nebo porazíš Syrské v Afeku, až i do konce vyhladíš je.
Ya ce masa, “Ka buɗe taga wajen gabas,” sai ya buɗe. Sai Elisha ya ce, “Ka harba!” Sai ya harba. Elisha ya ce, “Kibiyar nasara ta Ubangiji, kibiyar nasara a kan Aram! Za ka hallaka Arameyawa sarai a Afek.”
18 Opět řekl: Vezmi střely. I vzal. Tedy řekl králi Izraelskému: Střílej k zemi. I střelil po třikrát, potom tak nechal.
Sa’an nan ya ce, “Ka ɗauki kibiyoyi,” sai sarkin ya ɗauko. Sai Elisha ya ce, “Ka caki ƙasa.” Sai ya caka sau uku sa’an nan ya daina.
19 Pročež rozhněvav se na něj muž Boží, řekl: Měls pětkrát neb šestkrát střeliti, ješto bys byl porazil Syrské, ažbys je i do konce byl vyhladil; nyní pak jen po třikrát porazíš Syrské.
Sai mutumin Allah ya yi fushi da shi ya ce, “Da a ce ka caki ƙasar sau biyar ko shida; da za ka yi nasara a kan Aram ka kuma hallaka ta sarai. Amma yanzu za ka yi nasara a kanta sau uku ne kawai.”
20 Potom umřel Elizeus, a pochovali ho. Lotříkové pak Moábští vtrhli do země nastávajícího roku.
Elisha ya mutu, aka kuma binne shi. To, mahara Mowabawa sun saba kawo hari a ƙasar Isra’ila a kowace bazara.
21 I stalo se, když pochovávali jednoho, že uzřevše ty lotříky, uvrhli muže toho do hrobu Elizeova. Kterýžto muž, jakž tam padl, a dotekl se kostí Elizeových, ožil a vstal na nohy své.
Wata rana yayinda waɗansu Isra’ilawa suke binne wani mutum, farat ɗaya sai ga mahara; saboda haka suka jefar da gawar mutumin a kabarin Elisha. Da gawar ta taɓa ƙasusuwan Elisha, sai mutumin ya farka, ya tashi ya tsaya da ƙafafunsa.
22 Hazael pak král Syrský, ssužoval Izraele po všecky dny Joachaza.
Hazayel sarkin Aram ya musguna wa Isra’ila a duk tsawon mulkin Yehoyahaz.
23 A milostiv jsa jim Hospodin, slitoval se nad nimi, a popatřil na ně, pro smlouvu svou s Abrahamem, s Izákem a s Jákobem, a nechtěl jich zahladiti, aniž zavrhl jich od tváři své až do tohoto času.
Amma Ubangiji ya nuna musu alheri, ya ji tausayinsu, ya kuma damu da su saboda alkawarinsa da Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Har yă zuwa yau bai yarda yă hallaka su ko yă shafe su daga gabansa ba.
24 I umřel Hazael král Syrský, a kraloval Benadad syn jeho místo něho.
Hazayel sarkin Aram ya mutu, sai Ben-Hadad ɗansa ya gāje shi.
25 Protož Joas syn Joachazův pobral zase města z ruky Benadada syna Hazaelova, kteráž byl vzal z ruky Joachaza otce jeho válečně; nebo po třikrát porazil ho Joas, a navrátil města Izraelská.
Sa’an nan Yowash ya sāke ƙwato garuruwan da Ben-Hadad ya ci da yaƙi a hannun mahaifinsa Yehoyahaz. Sau uku Yehowash ya yi nasara a kansa, ta haka kuwa ya ƙwace garuruwan Isra’ilawa.

< 2 Královská 13 >