< Psalmi 50 >

1 Psalam. Asafov. Bog nad bogovima, Jahve, govori i zove zemlju od izlaza sunčeva do zalaza.
Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
2 Sa Siona predivnog Bog zablista:
Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
3 Bog naš dolazi i ne šuti. Pred njim ide oganj što proždire, oko njega silna bjesni oluja.
Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
4 On zove nebesa odozgo i zemlju da sudi narodu svojemu:
Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
5 “Saberite mi sve pobožnike koji žrtvom Savez sa mnom sklopiše!”
“Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
6 Nebesa objavljuju pravednost njegovu: on je Bog sudac!
Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
7 “Slušaj, narode moj, ja ću govoriti, o Izraele, svjedočit ću protiv tebe: ja, Bog - Bog tvoj!
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
8 Ne korim te zbog žrtava tvojih - paljenice su tvoje svagda preda mnom.
Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
9 Neću od doma tvog' uzet junca, ni jaraca iz tvojih torova:
Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
10 tÓa moje su sve životinje šumske, tisuće zvjeradi u gorama mojim.
gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
11 Znam sve ptice nebeske, moje je sve što se miče u poljima.
Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
12 Kad bih ogladnio, ne bih ti rekao, jer moja je zemlja i sve što je ispunja.
Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
13 Zar da ja jedem meso bikova ili da pijem krv jaraca?
Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
14 Prinesi Bogu žrtvu zahvalnu, ispuni Višnjemu zavjete svoje!
“Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
15 I zazovi me u dan tjeskobe: oslobodit ću te, a ti ćeš me slaviti.”
ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
16 A grešniku Bog progovara: “Što tumačiš naredbe moje, što mećeš u usta Savez moj?
Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
17 Ti, komu stega ne prija, te riječi moje iza leđa bacaš?
Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
18 Kad tata vidiš, s njime se bratimiš i družiš se s preljubnicima.
Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
19 Svoja si usta predao pakosti, a jezik ti plete prijevare.
Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
20 U društvu na brata govoriš i kaljaš sina matere svoje.
Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
21 Sve si to činio, a ja da šutim? Zar misliš da sam ja tebi sličan? Pokarat ću te i stavit ću ti sve to pred oči.”
Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
22 Shvatite ovo svi vi koji Boga zaboraviste, da vas ne pograbim i nitko vas spasiti neće.
“Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
23 Pravo me štuje onaj koji prinosi žrtvu zahvalnu: i onomu koji hodi stazama pravim - njemu ću pokazati spasenje svoje.
Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”

< Psalmi 50 >