< Luka 5 >

1 Dok se jednom oko njega gurao narod da čuje riječ Božju, stajaše on pokraj Genezaretskog jezera.
Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
2 Spazi dvije lađe gdje stoje uz obalu; ribari bili izašli iz njih i ispirali mreže.
sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
3 Uđe u jednu od tih lađa; bila je Šimunova pa zamoli Šimuna da malo otisne od kraja. Sjedne te iz lađe poučavaše mnoštvo.
Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
4 Kada dovrši pouku, reče Šimunu: “Izvezi na pučinu i bacite mreže za lov.”
Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
5 Odgovori Šimun: “Učitelju, svu smo se noć trudili i ništa ne ulovismo, ali na tvoju riječ bacit ću mreže.”
Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
6 Učiniše tako te uhvatiše veoma mnogo riba; mreže im se gotovo razdirale.
Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
7 Mahnuše drugovima na drugoj lađi da im dođu pomoći. Oni dođoše i napuniše obje lađe, umalo im ne potonuše.
Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
8 Vidjevši to, Šimun Petar pade do nogu Isusovih govoreći: “Idi od mene! Grešan sam čovjek, Gospodine!”
Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
9 Zbog lovine riba što ih uloviše bijaše se zapanjio on i svi koji bijahu s njime,
Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
10 a tako i Jakov i Ivan, Zebedejevi sinovi, drugovi Šimunovi. Isus reče Šimunu: “Ne boj se! Odsada ćeš loviti ljude!”
Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
11 Oni izvukoše lađe na kopno, ostaviše sve i pođoše za njim.
Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
12 I dok bijaše u jednom gradu, gle čovjeka puna gube! Ugledavši Isusa, padne ničice i zamoli ga: “Gospodine, ako hoćeš, možeš me očistiti.”
Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
13 Isus pruži ruku i dotakne ga se govoreći: “Hoću, očisti se!” I odmah nesta gube s njega.
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
14 I zapovjedi mu: “Nikome ni riječi, nego otiđi, pokaži se svećeniku i prinesi za svoje očišćenje kako propisa Mojsije, njima za svjedočanstvo.”
Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
15 Glas se o njemu sve više širio i silan svijet grnuo k njemu da ga sluša i da ozdravi od svojih bolesti.
Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
16 A on se sklanjao na samotna mjesta da moli.
Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
17 I jednog je dana on naučavao. A sjeđahu ondje farizeji i učitelji Zakona koji bijahu došli iz svih galilejskih i judejskih sela i Jeruzalema. A sila ga je Gospodnja nukala da liječi.
Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
18 I gle, ljudi doniješe na nosiljci čovjeka koji bijaše uzet. Tražili su da ga unesu i stave preda nj.
Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 Budući da zbog mnoštva nisu našli kuda bi ga unijeli, popnu se na krov te ga između crepova s nosiljkom spuste u sredinu pred Isusa.
Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
20 Vidjevši njihovu vjeru reče on: “Čovječe, otpušteni su ti grijesi!”
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
21 Pismoznanci i farizeji počeše mudrovati: “Tko je ovaj što huli? Tko može grijehe otpuštati doli Bog jedini?”
Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
22 Proniknuvši njihovo mudrovanje, upita ih Isus: “Što mudrujete u sebi?
Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
23 Što je lakše? Reći: 'Otpušteni su ti grijesi' ili reći: 'Ustani i hodi?'
Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
24 Ali da znate: Vlastan je Sin Čovječji na zemlji otpuštati grijehe!” I reče uzetomu: “Tebi zapovijedam: ustani, uzmi nosiljku i idi kući!”
Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
25 I on odmah usta pred njima, uze na čemu ležaše i ode kući slaveći Boga.
Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
26 A sve obuze zanos te su slavili Boga i puni straha govorili: “Danas vidjesmo nešto neviđeno!”
Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
27 Nakon toga iziđe i ugleda carinika imenom Levija gdje sjedi u carinarnici. I reče mu: “Pođi za mnom!”
Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
28 On sve ostavi, usta i pođe za njim.
Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
29 I Levi mu u svojoj kući priredi veliku gozbu. A s njime bijaše za stolom veliko mnoštvo carinika i drugih.
Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
30 Farizeji i pismoznanci njihovi negodovahu i govorahu njegovim učenicima: “Zašto s carinicima i grešnicima jedete i pijete?”
Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
31 Isus im odgovori: “Ne treba zdravima liječnika, nego bolesnima.
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
32 Nisam došao zvati pravedne, nego grešnike na obraćenje.”
Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 A oni mu rekoše: “Učenici Ivanovi, a tako i farizejski, počesto poste i obavljaju molitve, tvoji pak jedu i piju.”
Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
34 Reče im Isus: “Ne možete svatove prisiliti da poste dok je zaručnik s njima.
Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
35 Doći će već dani: kad im se ugrabi zaručnik, tada će postiti, u one dane!”
Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
36 A kazivao im je i prispodobu: “Nitko neće otparati krpe s novog odijela da je stavi na staro odijelo. Inače će i novo rasparati, a starom neće pristajati krpa s novoga.”
Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
37 “I nitko ne ulijeva novo vino u stare mješine. Inače će novo vino proderati mješine pa će se i ono proliti i mješine će propasti.
Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
38 Nego, novo vino neka se ulijeva u nove mješine!”
A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
39 “I nitko pijuć staro, ne zaželi novoga. Ta veli se: 'Valja staro!'”
Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”

< Luka 5 >