< Luka 1 >

1 Kad već mnogi poduzeše sastaviti izvješće o događajima koji se ispuniše među nama -
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 kako nam to predadoše oni koji od početka bijahu očevici i sluge Riječi -
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 pošto sam sve, od početka, pomno ispitao, naumih i ja tebi, vrli Teofile, sve po redu napisati
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 da se tako osvjedočiš o pouzdanosti svega u čemu si poučen.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 U dane Heroda, kralja judejskoga, bijaše neki svećenik imenom Zaharija iz razreda Abijina. Žena mu bijaše od kćeri Aronovih, a ime joj Elizabeta.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Oboje bijahu pravedni pred Bogom: živjeli su besprijekorno po svim zapovijedima i odredbama Gospodnjim.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 No nisu imali djeteta jer Elizabeta bijaše nerotkinja, a oboje već poodmakle dobi.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Dok je Zaharija jednom po redu svoga razreda obavljao svećeničku službu pred Bogom,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 ždrijebom ga zapade po bogoslužnom običaju da uđe u Svetište Gospodnje i prinese kad.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 Za vrijeme kađenice sve je ono mnoštvo naroda vani molilo.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 A njemu se ukaza anđeo Gospodnji. Stajao je s desne strane kadionoga žrtvenika.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 Ugledavši ga, Zaharija se prepade i strah ga spopade.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 No anđeo mu reče: “Ne boj se, Zaharija! Uslišana ti je molitva: žena će ti Elizabeta roditi sina. Nadjenut ćeš mu ime Ivan.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 Bit će ti radost i veselje i rođenje će njegovo mnoge obradovati.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 Bit će doista velik pred Gospodinom. Ni vina ni drugoga opojnog pića neće piti. Duha Svetoga bit će pun već od majčine utrobe.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 Mnoge će sinove Izraelove obratiti Gospodinu, Bogu njihovu.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 Ići će pred njim u duhu i sili Ilijinoj da obrati srce otaca k sinovima i nepokorne k razumnosti pravednih te spremi Gospodinu narod pripravan.”
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 Nato Zaharija reče anđelu: “Po čemu ću ja to razaznati. Ta star sam i žena mi poodmakle dobi.”
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 Anđeo mu odgovori: “Ja sam Gabriel koji stojim pred Bogom. Poslan sam da govorim s tobom i da ti donesem ovu radosnu poruku.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 I evo, budući da nisi povjerovao mojim riječima, koje će se ispuniti u svoje vrijeme, zanijemjet ćeš i nećeš moći govoriti do dana dok se to ne zbude.”
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 Narod je iščekivao Zahariju i čudio se što se toliko zadržao u Svetištu.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 Kad je napokon izašao, nije im mogao ništa reći pa zaključiše da je u Svetištu imao viđenje. Nastojao im se doduše izraziti znakovima, ali osta nijem.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 Kad se navršiše dani njegove službe, otiđe kući.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 Nakon tih dana zatrudnje Elizabeta, njegova žena. Krila se pet mjeseci govoreći:
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 “Evo, to mi je učinio Gospodin u dane kad mu se svidje skinuti s mene sramotu među ljudima.”
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 U šestome mjesecu posla Bog anđela Gabriela u galilejski grad imenom Nazaret
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 k djevici zaručenoj s mužem koji se zvao Josip iz doma Davidova; a djevica se zvala Marija.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 Anđeo uđe k njoj i reče: “Zdravo, milosti puna! Gospodin s tobom!”
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 Na tu se riječ ona smete i stade razmišljati kakav bi to bio pozdrav.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 No anđeo joj reče: “Ne boj se, Marijo! Ta našla si milost u Boga.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 Evo, začet ćeš i roditi sina i nadjenut ćeš mu ime Isus.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 On će biti velik i zvat će se Sin Svevišnjega. Njemu će Gospodin Bog dati prijestolje Davida, oca njegova,
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 i kraljevat će nad domom Jakovljevim uvijeke i njegovu kraljevstvu neće biti kraja.” (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Nato će Marija anđelu: “Kako će to biti kad ja muža ne poznajem?”
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 Anđeo joj odgovori: “Duh Sveti sići će na te i sila će te Svevišnjega osjeniti. Zato će to čedo i biti sveto, Sin Božji.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 A evo tvoje rođakinje Elizabete: i ona u starosti svojoj zače sina. I njoj, nerotkinjom prozvanoj, ovo je već šesti mjesec.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 Ta Bogu ništa nije nemoguće!”
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Nato Marija reče: “Evo službenice Gospodnje, neka mi bude po tvojoj riječi!” I anđeo otiđe od nje.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Tih dana usta Marija i pohiti u Gorje, u grad Judin.
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 Uđe u Zaharijinu kuću i pozdravi Elizabetu.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 Čim Elizabeta začu Marijin pozdrav, zaigra joj čedo u utrobi. I napuni se Elizabeta Duha Svetoga
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 i povika iz svega glasa: “Blagoslovljena ti među ženama i blagoslovljen plod utrobe tvoje!
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 Ta otkuda meni da mi dođe majka Gospodina mojega?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 Gledaj samo! Tek što mi do ušiju doprije glas pozdrava tvojega, zaigra mi od radosti čedo u utrobi.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 Blažena ti što povjerova da će se ispuniti što ti je rečeno od Gospodina!”
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Tada Marija reče: “Veliča duša moja Gospodina,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 klikće duh moj u Bogu, mome Spasitelju,
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 što pogleda na neznatnost službenice svoje: odsad će me, evo, svi naraštaji zvati blaženom.
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 Jer velika mi djela učini Svesilni, sveto je ime njegovo!
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 Od koljena do koljena dobrota je njegova nad onima što se njega boje.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 Iskaza snagu mišice svoje, rasprši oholice umišljene.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 Silne zbaci s prijestolja, a uzvisi neznatne.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 Gladne napuni dobrima, a bogate otpusti prazne.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 Prihvati Izraela, slugu svoga, kako obeća ocima našim:
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 spomenuti se dobrote svoje prema Abrahamu i potomstvu njegovu dovijeka.” (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 Marija osta s Elizabetom oko tri mjeseca, a onda se vrati kući.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Elizabeti se međutim navršilo vrijeme da rodi. I porodi sina.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 Kad su njezini susjedi i rođaci čuli da joj Gospodin obilno iskaza dobrotu, radovahu se s njome.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 Osmoga se dana okupe da obrežu dječaka. Htjedoše ga prozvati imenom njegova oca - Zaharija,
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 no mati se njegova usprotivi: “Nipošto, nego zvat će se Ivan!”
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 Rekoše joj na to: “Ta nikoga nema od tvoje rodbine koji bi se tako zvao.”
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 Tada znakovima upitaju oca kojim ga imenom želi prozvati.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 On zaiska pločicu i napisa “Ivan mu je ime!” Svi se začude,
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 a njemu se umah otvoriše usta i jezik te progovori blagoslivljajući Boga.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 Strah obuze sve njihove susjede, a po svem su se Gorju judejskom razglašavali svi ti događaji.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 I koji su god čuli, razmišljahu o tome pitajući se: “Što li će biti od ovoga djeteta?” Uistinu, ruka Gospodnja bijaše s njime.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 A Zaharija, otac njegov, napuni se Duha Svetoga i stade prorokovati:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 “Blagoslovljen Gospodin Bog Izraelov, što pohodi i otkupi narod svoj!
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 Podiže nam snagu spasenja u domu Davida, sluge svojega,
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 kao što obeća na usta svetih proroka svojih odvijeka: (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 spasiti nas od neprijatelja naših i od ruke sviju koji nas mrze;
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 iskazati dobrotu ocima našim i sjetiti se svetog Saveza svojega,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 zakletve kojom se zakle Abrahamu, ocu našemu: da će nam dati
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 te mu, izbavljeni iz ruku neprijatelja, služimo bez straha
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 u svetosti i pravednosti pred njim u sve dane svoje.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 A ti, dijete, prorok ćeš se Svevišnjega zvati jer ćeš ići pred Gospodinom da mu pripraviš putove,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 da pružiš spoznaju spasenja narodu njegovu po otpuštenju grijeha njihovih,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 darom premilosrdnog srca Boga našega po kojem će nas pohoditi Mlado sunce s visine
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 da obasja one što sjede u tmini i sjeni smrtnoj, da upravi noge naše na put mira.”
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 Dječak je međutim rastao i duhom jačao. Boravio je u pustinji sve do dana svoga javnog nastupa pred Izraelom.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luka 1 >