< 2 Ljetopisa 21 >

1 Jošafat počinu kraj svojih otaca i bi sahranjen uz njih u Davidovu gradu. Na njegovo se mjesto zakraljio sin mu Joram.
Yehoshafat ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sai Yehoram ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
2 Joram je imao šestoricu braće, Jošafatovih sinova: Azarju, Jehiela, Zahariju, Azarju, Mihaela i Šefatju. Svi su oni bili sinovi izraelskog kralja Jošafata.
’Yan’uwan Yehoram,’ya’yan Yehoshafat maza su ne, Azariya, Yehiyel, Zakariya, Azariyahu, Mika’ilu da Shefatiya. Dukan waɗannan su ne’ya’yan Yehoshafat sarkin Isra’ila maza.
3 Otac im je dao mnoge darove u srebru, zlatu i dragocjenostima, s utvrđenim gradovima u Judi; kraljevstvo je dao Joramu jer je bio prvenac.
Mahaifinsu ya ba su kyautai masu yawa na azurfa da zinariya da kayayyaki masu daraja, tare da birane masu katanga a Yahuda, amma ya ba da mulki ga Yehoram domin shi ne ɗan farinsa.
4 Stupivši na očevo prijestolje i utvrdiv se, Joram pobi svu braću mačem, pa i neke izraelske knezove.
Sa’ad da Yehoram ya kafa kansa sosai a bisa mulkin mahaifinsa, sai ya kashe dukan’yan’uwansa da takobi tare da waɗansu sarakunan Isra’ila.
5 Joramu su bile trideset i dvije godine kad se zakraljio, a kraljevao je osam godina u Jeruzalemu.
Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas.
6 Živio je poput izraelskih kraljeva, kao i dom Ahabov, jer mu je kći Ahabova bila žena; radio je što je zlo u Jahvinim očima.
Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, kamar yadda gidan Ahab ta yi, gama ya auri’yar Ahab. Ya aikata mugayen ayyuka a idon Ubangiji.
7 Ipak Jahve ne htjede razoriti kuće Davidu zbog Saveza što ga sklopi s njim i zato što mu obeća da će dati svjetiljku njemu i njegovim sinovima zauvijek.
Duk da haka, domin alkawarin da Ubangiji ya yi wa Dawuda, Ubangiji bai so yă hallaka gidan Dawuda ba. Ubangiji ya riga ya yi alkawari zai ci gaba da riƙe fitila domin Dawuda da zuriyarsa har abada.
8 U njegovo se vrijeme Edomci odmetnuše ispod judejske vlasti i postaviše sebi kralja.
A zamanin Yehoram, Edom ya tayar wa Yahuda ya kuma naɗa sarkinsa.
9 Zato Joram pođe sa svojim vojskovođama i sa svim bojnim kolima. Diže se noću i pobi Edomce koji bijahu opkolili njega i zapovjednike bojnih kola.
Saboda haka Yehoram ya tafi can tare da shugabannin sojojinsa da kuma dukan keken yaƙinsa. Mutanen Edom suka kewaye shi da shugabannin keken yaƙinsa, amma ya tashi ya fatattaki su da dare.
10 Ipak su se Edomci oslobodili ispod judejske vlasti sve do danas. U isto se doba odmetnu i Libna da ne bude pod njegovom vlašću, jer je on ostavio Jahvu, Boga svojih otaca.
Har yă zuwa yau Edom na tawaye a kan Yahuda. Libna ya yi tawaye a lokaci guda, domin Yehoram ya yashe Ubangiji Allah na kakanninsa.
11 Još je i uzvišice napravio po judejskim gorama, naveo na blud Jeruzalemce i zaveo Judejce.
Ya gina masujadan kan tudu a tuddan Yahuda, ya kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, ya sa Yahuda suka kauce.
12 Tada mu od proroka Ilije stiže pismo: “Ovako veli Jahve, Bog tvoga oca Davida: 'Kako nisi išao putovima oca Jošafata, ni putovima judejskoga kralja Ase,
Yehoram ya sami wasiƙa daga Iliya annabi, wadda ta ce, “Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda ya ce, ‘Ba ka yi tafiya a hanyoyin mahaifinka Yehoshafat ko Asa sarkin Yahuda ba.
13 nego si išao putovima izraelskih kraljeva i naveo na blud Judejce i Jeruzalemce, kao što je učinio dom Ahabov, a uz to si poubijao vlastitu braću, svoju obitelj, koji bjehu bolji od tebe:
Amma ka yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, ka sa Yahuda ya kauce, ka kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, kamar yadda gidan Ahab ta yi. Ka kuma kashe’yan’uwanka, membobi gidan mahaifinka, mutanen da suka fi ka kirki.
14 evo, Jahve će svaliti veliku nesreću na tvoj narod, na tvoje sinove, tvoje žene, na sve tvoje imanje.
Saboda haka a yanzu Ubangiji yana shirin ya bugi mutanenka,’ya’yanka maza, matanka da kuma kome da yake naka, da bugu mai ƙarfi.
15 Oboljet ćeš od mnogih bolesti: od bolesti u crijevima, tako da će ti crijeva izaći od bolesti koja će trajati dane i dane.'”
Kai kuma za ka kamu da ciwon hanji wanda zai yi ta cinka kowace rana sai har hanjinka sun fito.’”
16 Jahve podiže na Jorama srdžbu Filistejaca i Arapa koji žive kraj Etiopljana.
Ubangiji ya sa Filistiyawa da Larabawa waɗanda suke zama kusa da Kushawa su yi gāba da Yehoram
17 Oni napadoše Judeju i osvojiše je, porobiše sve blago što se našlo u kraljevu dvoru, pa i njegove sinove i njegove žene, tako da nije ostao nitko, osim najmlađega sina, Joahaza.
Suka yaƙi Yahuda, suka kai masa hari, suka kwashe dukan abubuwa masu kyau da suka samu a fadan sarki, tare da’ya’yansa maza da kuma matansa. Ba wanda aka bari, sai dai Ahaziya autansa.
18 Poslije svega toga udari ga Jahve neizlječivom crijevnom bolešću.
Bayan dukan wannan, sai Ubangiji ya sa wa Yehoram cuta marar warkarwa ta ciki.
19 Ona je trajala dane i dane, a kad su se navršile dvije godine, izašla su mu crijeva s bolešću te je umro u strašnim mukama. Narod mu nije priredio mirisna paljenja, kao što je palio njegovim ocima.
Cikin lokaci, a ƙarshen shekara ta biyu, sai hanjin cikinsa suka fito saboda cutar, ya kuma mutu cikin tsananin zafi. Mutanensa suka hura wuta don girmama shi, kamar yadda suka yi wa kakanninsa.
20 Bile su mu trideset i dvije godine kad se zakraljio, a osam je godina kraljevao u Jeruzalemu. Preminuo je, a nitko nije požalio za njim; i sahraniše ga u Davidovu gradu, ali ne u kraljevskoj grobnici.
Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas. Ya mutu, ba ma wanda ya kula, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda, amma ba a makabartan sarakuna ba.

< 2 Ljetopisa 21 >