< 路加福音 1 >

1 提阿非羅大人哪,有好些人提筆作書,述說在我們中間所成就的事,是照傳道的人從起初親眼看見又傳給我們的。
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 這些事我既從起頭都詳細考察了,就定意要按着次序寫給你,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 使你知道所學之道都是確實的。
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 當猶太王希律的時候,亞比雅班裏有一個祭司,名叫撒迦利亞;他妻子是亞倫的後人,名叫伊利莎白。
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 他們二人在上帝面前都是義人,遵行主的一切誡命禮儀,沒有可指摘的,
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 只是沒有孩子;因為伊利莎白不生育,兩個人又年紀老邁了。
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 撒迦利亞按班次在上帝面前供祭司的職分,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 照祭司的規矩掣籤,得進主殿燒香。
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 燒香的時候,眾百姓在外面禱告。
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 有主的使者站在香壇的右邊,向他顯現。
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 撒迦利亞看見,就驚慌害怕。
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 天使對他說:「撒迦利亞,不要害怕,因為你的祈禱已經被聽見了。你的妻子伊利莎白要給你生一個兒子,你要給他起名叫約翰。
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 你必歡喜快樂;有許多人因他出世,也必喜樂。
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 他在主面前將要為大,淡酒濃酒都不喝,從母腹裏就被聖靈充滿了。
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 他要使許多以色列人回轉,歸於主-他們的上帝。
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 他必有以利亞的心志能力,行在主的前面,叫為父的心轉向兒女,叫悖逆的人轉從義人的智慧,又為主預備合用的百姓。」
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 撒迦利亞對天使說:「我憑着甚麼可知道這事呢?我已經老了,我的妻子也年紀老邁了。」
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 天使回答說:「我是站在上帝面前的加百列,奉差而來對你說話,將這好信息報給你。
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 到了時候,這話必然應驗;只因你不信,你必啞巴,不能說話,直到這事成就的日子。」
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 百姓等候撒迦利亞,詫異他許久在殿裏。
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 及至他出來,不能和他們說話,他們就知道他在殿裏見了異象;因為他直向他們打手式,竟成了啞巴。
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 他供職的日子已滿,就回家去了。
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 這些日子以後,他的妻子伊利莎白懷了孕,就隱藏了五個月,
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 說:「主在眷顧我的日子,這樣看待我,要把我在人間的羞恥除掉。」
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 到了第六個月,天使加百列奉上帝的差遣往加利利的一座城去(這城名叫拿撒勒),
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 到一個童女那裏,是已經許配大衛家的一個人,名叫約瑟。童女的名字叫馬利亞;
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 天使進去,對她說:「蒙大恩的女子,我問你安,主和你同在了!」
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 馬利亞因這話就很驚慌,又反覆思想這樣問安是甚麼意思。
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 天使對她說:「馬利亞,不要怕!你在上帝面前已經蒙恩了。
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 你要懷孕生子,可以給他起名叫耶穌。
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 他要為大,稱為至高者的兒子;主上帝要把他祖大衛的位給他。
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 他要作雅各家的王,直到永遠;他的國也沒有窮盡。」 (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 馬利亞對天使說:「我沒有出嫁,怎麼有這事呢?」
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 天使回答說:「聖靈要臨到你身上,至高者的能力要蔭庇你,因此所要生的聖者必稱為上帝的兒子 。
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 況且你的親戚伊利莎白,在年老的時候也懷了男胎,就是那素來稱為不生育的,現在有孕六個月了。
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 因為,出於上帝的話,沒有一句不帶能力的。」
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 馬利亞說:「我是主的使女,情願照你的話成就在我身上。」天使就離開她去了。
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 那時候,馬利亞起身,急忙往山地裏去,來到猶大的一座城;
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 進了撒迦利亞的家,問伊利莎白安。
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 伊利莎白一聽馬利亞問安,所懷的胎就在腹裏跳動。伊利莎白且被聖靈充滿,
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 高聲喊着說:「你在婦女中是有福的!你所懷的胎也是有福的!
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 我主的母到我這裏來,這是從哪裏得的呢?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 因為你問安的聲音一入我耳,我腹裏的胎就歡喜跳動。
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 這相信的女子是有福的!因為主對她所說的話都要應驗。」
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 馬利亞說: 我心尊主為大;
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 我靈以上帝我的救主為樂;
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 因為他顧念他使女的卑微; 從今以後, 萬代要稱我有福。
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 那有權能的,為我成就了大事; 他的名為聖。
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 他憐憫敬畏他的人, 直到世世代代。
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 他用膀臂施展大能; 那狂傲的人正心裏妄想就被他趕散了。
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 他叫有權柄的失位, 叫卑賤的升高;
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 叫飢餓的得飽美食, 叫富足的空手回去。
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 他扶助了他的僕人以色列,
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 為要記念亞伯拉罕和他的後裔, 施憐憫直到永遠, 正如從前對我們列祖所說的話。 (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 馬利亞和伊利莎白同住,約有三個月,就回家去了。
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 伊利莎白的產期到了,就生了一個兒子。
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 鄰里親族聽見主向她大施憐憫,就和她一同歡樂。
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 到了第八日,他們來要給孩子行割禮,並要照他父親的名字叫他撒迦利亞。
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 他母親說:「不可!要叫他約翰。」
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 他們說:「你親族中沒有叫這名字的。」
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 他們就向他父親打手式,問他要叫這孩子甚麼名字。
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 他要了一塊寫字的板,就寫上,說:「他的名字是約翰。」他們便都希奇。
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 撒迦利亞的口立時開了,舌頭也舒展了,就說出話來,稱頌上帝。
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 周圍居住的人都懼怕;這一切的事就傳遍了猶太的山地。
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 凡聽見的人都將這事放在心裏,說:「這個孩子將來怎麼樣呢?因為有主與他同在。」
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 他父親撒迦利亞被聖靈充滿了,就預言說:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 主-以色列的上帝是應當稱頌的! 因他眷顧他的百姓,為他們施行救贖,
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 在他僕人大衛家中, 為我們興起了拯救的角,
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 正如主藉着從創世以來聖先知的口所說的話, (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 拯救我們脫離仇敵 和一切恨我們之人的手,
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 向我們列祖施憐憫, 記念他的聖約-
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 就是他對我們祖宗亞伯拉罕所起的誓-
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 叫我們既從仇敵手中被救出來,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 就可以終身在他面前, 坦然無懼地用聖潔、公義事奉他。
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 孩子啊!你要稱為至高者的先知; 因為你要行在主的前面, 預備他的道路,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 叫他的百姓因罪得赦, 就知道救恩。
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 因我們上帝憐憫的心腸, 叫清晨的日光從高天臨到我們,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 要照亮坐在黑暗中死蔭裏的人, 把我們的腳引到平安的路上。
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 那孩子漸漸長大,心靈強健,住在曠野,直到他顯明在以色列人面前的日子。
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< 路加福音 1 >