< 诗篇 69 >

1 大卫的诗,交与伶长。调用百合花。 神啊,求你救我! 因为众水要淹没我。
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
2 我陷在深淤泥中,没有立脚之地; 我到了深水中,大水漫过我身。
Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
3 我因呼求困乏,喉咙发干; 我因等候 神,眼睛失明。
Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
4 无故恨我的,比我头发还多; 无理与我为仇、要把我剪除的,甚为强盛。 我没有抢夺的,要叫我偿还。
Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
5 神啊,我的愚昧,你原知道; 我的罪愆不能隐瞒。
Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
6 万军的主—耶和华啊, 求你叫那等候你的,不要因我蒙羞! 以色列的 神啊, 求你叫那寻求你的,不要因我受辱!
Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
7 因我为你的缘故受了辱骂, 满面羞愧。
Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
8 我的弟兄看我为外路人; 我的同胞看我为外邦人。
Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
9 因我为你的殿心里焦急,如同火烧, 并且辱骂你人的辱骂都落在我身上。
gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
10 我哭泣,以禁食刻苦我心; 这倒算为我的羞辱。
Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
11 我拿麻布当衣裳, 就成了他们的笑谈。
sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
12 坐在城门口的谈论我; 酒徒也以我为歌曲。
Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
13 但我在悦纳的时候向你—耶和华祈祷。 神啊,求你按你丰盛的慈爱, 凭你拯救的诚实应允我!
Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
14 求你搭救我出离淤泥, 不叫我陷在其中; 求你使我脱离那些恨我的人, 使我出离深水。
Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
15 求你不容大水漫过我, 不容深渊吞灭我, 不容坑坎在我以上合口。
Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
16 耶和华啊,求你应允我! 因为你的慈爱本为美好; 求你按你丰盛的慈悲回转眷顾我!
Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
17 不要掩面不顾你的仆人; 我是在急难之中,求你速速地应允我!
Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
18 求你亲近我,救赎我! 求你因我的仇敌把我赎回!
Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
19 你知道我受的辱骂、欺凌、羞辱; 我的敌人都在你面前。
Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
20 辱骂伤破了我的心, 我又满了忧愁。 我指望有人体恤,却没有一个; 我指望有人安慰,却找不着一个。
Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
21 他们拿苦胆给我当食物; 我渴了,他们拿醋给我喝。
Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
22 愿他们的筵席在他们面前变为网罗, 在他们平安的时候变为机槛。
Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
23 愿他们的眼睛昏蒙,不得看见; 愿你使他们的腰常常战抖。
Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
24 求你将你的恼恨倒在他们身上, 叫你的烈怒追上他们。
Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
25 愿他们的住处变为荒场; 愿他们的帐棚无人居住。
Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
26 因为,你所击打的,他们就逼迫; 你所击伤的,他们戏说他的愁苦。
Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
27 愿你在他们的罪上加罪, 不容他们在你面前称义。
Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
28 愿他们从生命册上被涂抹, 不得记录在义人之中。
Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
29 但我是困苦忧伤的; 神啊,愿你的救恩将我安置在高处。
Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
30 我要以诗歌赞美 神的名, 以感谢称他为大!
Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
31 这便叫耶和华喜悦,胜似献牛, 或是献有角有蹄的公牛。
Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
32 谦卑的人看见了就喜乐; 寻求 神的人,愿你们的心苏醒。
Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
33 因为耶和华听了穷乏人, 不藐视被囚的人。
Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
34 愿天和地、 洋海和其中一切的动物都赞美他!
Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
35 因为 神要拯救锡安,建造犹大的城邑; 他的民要在那里居住,得以为业。
gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
36 他仆人的后裔要承受为业; 爱他名的人也要住在其中。
’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.

< 诗篇 69 >