< 诗篇 66 >

1 一篇诗歌,交与伶长。 全地都当向 神欢呼!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
2 歌颂他名的荣耀! 用赞美的言语将他的荣耀发明!
Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
3 当对 神说:你的作为何等可畏! 因你的大能,仇敌要投降你。
Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
4 全地要敬拜你,歌颂你, 要歌颂你的名。 (细拉)
Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
5 你们来看 神所行的, 他向世人所做之事是可畏的。
Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
6 他将海变成干地,众民步行过河; 我们在那里因他欢喜。
Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
7 他用权能治理万民,直到永远。 他的眼睛鉴察列邦; 悖逆的人不可自高。 (细拉)
Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
8 万民哪,你们当称颂我们的 神, 使人得听赞美他的声音。
Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
9 他使我们的性命存活, 也不叫我们的脚摇动。
ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
10 神啊,你曾试验我们, 熬炼我们,如熬炼银子一样。
Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
11 你使我们进入网罗, 把重担放在我们的身上。
Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
12 你使人坐车轧我们的头; 我们经过水火, 你却使我们到丰富之地。
Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
13 我要用燔祭进你的殿, 向你还我的愿,
Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
14 就是在急难时我嘴唇所发的、 口中所许的。
alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
15 我要把肥牛作燔祭, 将公羊的香祭献给你, 又把公牛和山羊献上。 (细拉)
Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
16 凡敬畏 神的人,你们都来听! 我要述说他为我所行的事。
Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
17 我曾用口求告他; 我的舌头也称他为高。
Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
18 我若心里注重罪孽, 主必不听。
Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
19 但 神实在听见了; 他侧耳听了我祷告的声音。
amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
20 神是应当称颂的! 他并没有推却我的祷告, 也没有叫他的慈爱离开我。
Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!

< 诗篇 66 >