< 民数记 13 >

1 耶和华晓谕摩西说:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 “你打发人去窥探我所赐给以色列人的迦南地,他们每支派中要打发一个人,都要作首领的。”
“Ka aiki waɗansu mutane zuwa ƙasar Kan’ana, wadda nake ba Isra’ilawa. Daga kowace kabila, ka aiki ɗaya daga cikin shugabanninta.”
3 摩西就照耶和华的吩咐从巴兰的旷野打发他们去;他们都是以色列人的族长。
Saboda haka bisa ga umarnin Ubangiji, Musa ya aike su daga Hamadan Faran. Dukansu kuwa shugabanni ne na Isra’ilawa.
4 他们的名字:属吕便支派的有撒刻的儿子沙母亚。
Shugabannin kuwa su ne, Shammuwa ɗan Zakkur, daga kabilar Ruben;
5 属西缅支派的有何利的儿子沙法。
Shafat ɗan Hori, daga kabilar Simeyon;
6 属犹大支派的有耶孚尼的儿子迦勒。
Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
7 属以萨迦支派的有约色的儿子以迦。
Igal ɗan Yusuf, daga kabilar Issakar;
8 属以法莲支派的有嫩的儿子何希阿。
Hosheya ɗan Nun, daga kabilar Efraim;
9 属便雅悯支派的有拉孚的儿子帕提。
daga kabilar Benyamin, Falti ɗan Rafu;
10 属西布伦支派的有梭底的儿子迦叠。
Gaddiyel ɗan Sodi, daga kabilar Zebulun;
11 约瑟的子孙,属玛拿西支派的有稣西的儿子迦底。
Gaddi ɗan Susi, daga kabilar Manasse (wata kabilar Yusuf);
12 属但支派的有基玛利的儿子亚米利。
Ammiyel ɗan Gemalli, daga kabilar Dan;
13 属亚设支派的有米迦勒的儿子西帖。
Setur ɗan Mika’ilu, daga kabilar Asher;
14 属拿弗他利支派的有缚西的儿子拿比。
Nabi ɗan Bofsi, daga kabilar Naftali;
15 属迦得支派的有玛基的儿子臼利。
Geyuwel ɗan Maki, daga kabilar Gad.
16 这就是摩西所打发、窥探那地之人的名字。摩西就称嫩的儿子何希阿为约书亚。
Waɗannan su ne sunayen mutanen da Musa ya aika su binciki ƙasar. (Sai Musa ya ba Hosheya ɗan Nun, suna Yoshuwa.)
17 摩西打发他们去窥探迦南地,说:“你们从南地上山地去,
Sa’ad da Musa ya aike su domin su binciki Kan’ana ya ce, “Ku haura, ku ratsa ta Negeb har zuwa ƙasar tudu.
18 看那地如何,其中所住的民是强是弱,是多是少,
Ku ga yadda ƙasar take, ku ga ko mutanen da suke zama a can ƙarfafa ne, ko raunannu, ko su kima ne, ko kuma suna da yawa.
19 所住之地是好是歹,所住之处是营盘是坚城。
Wace irin ƙasa ce suke zama a ciki, Mai kyau ce, ko mummuna? Waɗanne irin birane ne suke zama a ciki? Suna da katanga, ko babu?
20 又看那地土是肥美是瘠薄,其中有树木没有。你们要放开胆量,把那地的果子带些来。”(那时正是葡萄初熟的时候。)
Yaya ƙasar take? Tana da wadata, ko babu? Akwai itatuwa, ko babu? Ku yi iya ƙoƙarinku ku ɗebo daga cikin albarkar ƙasar ku kawo.” (Lokacin farkon nunan inabi ne.)
21 他们上去窥探那地,从寻的旷野到利合,直到哈马口。
Saboda haka suka haura, suka binciki ƙasar daga Hamadan Zin har zuwa Rehob, wajen Lebo Hamat.
22 他们从南地上去,到了希伯 ;在那里有亚衲族人亚希幔、示筛、挞买。(原来希伯 城被建造比埃及的锁安城早七年。)
Suka kuma haura ta Negeb, suka iso Hebron, inda Ahiman, da Sheshai, da Talmai, zuriyar Anak, suke zama. (An gina Hebron da shekara bakwai kafin a gina Zowan a Masar.)
23 他们到了以实各谷,从那里砍了葡萄树的一枝,上头有一挂葡萄,两个人用杠抬着,又带了些石榴和无花果来。(
Da suka iso Kwarin Eshkol, sai suka yanko reshe guda na nonon inabi tare da’ya’yansa cunkus. Mutum biyu suka ɗauka shi rataye a sanda a kafaɗarsu, suka haɗa tare da rumman da kuma ɓaure.
24 因为以色列人从那里砍来的那挂葡萄,所以那地方叫做以实各谷。)
Sai aka kira wurin Kwarin Eshkol saboda nonon inabin da suka yi cunkus, wanda Isra’ilawa suka yanko a wurin.
25 过了四十天,他们窥探那地才回来,
A ƙarshen kwana arba’in sai suka komo daga bincikensu.
26 到了巴兰旷野的加低斯,见摩西、亚伦,并以色列的全会众,回报摩西、亚伦,并全会众,又把那地的果子给他们看;
Suka dawo wurin Musa, da Haruna, da dukan jama’ar Isra’ilawa, a Kadesh, a Hamadan Faran. A can suka ba da rahoton ga dukan taron da yake wurin, suka kuma nuna musu amfanin ƙasar.
27 又告诉摩西说:“我们到了你所打发我们去的那地,果然是流奶与蜜之地;这就是那地的果子。
Suka ce wa Musa, “Mun je ƙasar da ka aike mu, ƙasar tana zub da madara da zuma! Ga kuma amfaninta.
28 然而住那地的民强壮,城邑也坚固宽大,并且我们在那里看见了亚衲族的人。
Amma fa mazaunan can ɗin ƙarfafa ne, an kuma kewaye biranen da manya-manyan katanga. Mun kuma ga zuriyar Anak a can.
29 亚玛力人住在南地;赫人、耶布斯人、亚摩利人住在山地;迦南人住在海边并约旦河旁。”
Amalekawa suna zama a Negeb; Hittiyawa, Yebusiyawa da kuma Amoriyawa, suna zama ne a ƙasar tudu. Kan’aniyawa kuma suna zama kusa da teku da kuma a bakin Urdun.”
30 迦勒在摩西面前安抚百姓,说:“我们立刻上去得那地吧!我们足能得胜。”
Sai Kaleb ya sa mutane suka yi shiru a gaban Musa, sai ya ce, “Ya kamata mu tafi mu mallaki ƙasar, gama lalle za mu iya cinta.”
31 但那些和他同去的人说:“我们不能上去攻击那民,因为他们比我们强壮。”
Amma sauran mutanen da suka je tare da shi, suka ce, “Ba za mu iya kara da mutanen nan ba; sun fi mu ƙarfi.”
32 探子中有人论到所窥探之地,向以色列人报恶信,说:“我们所窥探、经过之地是吞吃居民之地,我们在那里所看见的人民都身量高大。
Sai suka yaɗa labari marar kyau ga Isra’ilawa game da ƙasar da suka binciko. Suka ce, “Ƙasar da muka ratsa cikinta domin mu leƙi asirinta, tana cinye waɗanda suke zama a cikinta. Dukan mutanen da muka gani a wurin, ƙatti ne.
33 我们在那里看见亚衲族人,就是伟人;他们是伟人的后裔。据我们看,自己就如蚱蜢一样;据他们看,我们也是如此。”
Mun ga Nefilimawa a can (zuriyar Anak sun fito ne daga Nefilim). Sai muka ga kanmu kamar fāra ne kawai, haka kuwa muke a gare su.”

< 民数记 13 >