< 马可福音 3 >

1 耶稣又进了会堂,在那里有一个人枯干了一只手。
Wani lokaci, da ya sāke shiga majami’a, sai ga wani mutum mai shanyayyen hannu.
2 众人窥探耶稣,在安息日医治不医治,意思是要控告耶稣。
Waɗansu daga cikin mutane suna neman dalilin zargin Yesu, sai suka zuba masa ido, su ga ko zai warkar da shi a ranar Asabbaci.
3 耶稣对那枯干一只手的人说:“起来,站在当中。”
Yesu ya ce wa mutumin mai shanyayyen hannun, “Tashi ka tsaya a gaban kowa.”
4 又问众人说:“在安息日行善行恶,救命害命,哪样是可以的呢?”他们都不作声。
Sai Yesu ya tambaye su ya ce, “Me ya kamata a yi bisa ga doka, a ranar Asabbaci, a aikata alheri, ko a aikata mugunta, a ceci rai, ko a yi kisa?” Amma suka yi shiru.
5 耶稣怒目周围看他们,忧愁他们的心刚硬,就对那人说:“伸出手来!”他把手一伸,手就复了原。
Sai ya kalle su da fushi, don taurin zuciyarsu ya ɓata masa rai sosai. Sai ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye.
6 法利赛人出去,同希律一党的人商议怎样可以除灭耶稣。
Sai Farisiyawa suka fita, suka fara ƙulla shawara da mutanen Hiridus yadda za su kashe Yesu.
7 耶稣和门徒退到海边去,有许多人从加利利跟随他。
Yesu da almajiransa suka janye zuwa tafkin, taro mai yawa kuwa daga Galili ya bi shi.
8 还有许多人听见他所做的大事,就从犹太、耶路撒冷、以土买、约旦河外,并泰尔、西顿的四方来到他那里。
Mutane da yawa daga Yahudiya, da Urushalima, da Edom, da kuma yankunan da suke ƙetaren Urdun, da kewayen Taya, da Sidon suka zo wurinsa, don sun ji dukan abubuwan da yake yi.
9 他因为人多,就吩咐门徒叫一只小船伺候着,免得众人拥挤他。
Saboda taron, sai ya ce wa almajiransa su shirya masa ƙaramin jirgin ruwa, don kada mutane su matse shi.
10 他治好了许多人,所以凡有灾病的,都挤进来要摸他。
Gama ya warkar da mutane da yawa, masu cututtuka suka yi ta ƙoƙarin zuwa gaba, don su taɓa shi.
11 污鬼无论何时看见他,就俯伏在他面前,喊着说:“你是 神的儿子。”
Duk sa’ad da mugayen ruhohi suka gan shi, sai fāɗi a gabansa, su ɗaga murya, su ce, “Kai Ɗan Allah ne.”
12 耶稣再三地嘱咐他们,不要把他显露出来。
Amma yakan tsawata musu, kada su shaida ko wane ne shi.
13 耶稣上了山,随自己的意思叫人来;他们便来到他那里。
Yesu ya hau gefen wani dutse, ya kira waɗanda yake so, suka kuma zo wurinsa.
14 他就设立十二个人,要他们常和自己同在,也要差他们去传道,
Ya naɗa sha biyu, ya kira su manzanni don su kasance tare da shi, domin kuma yă aike su yin wa’azi,
15 并给他们权柄赶鬼。
don kuma su sami ikon fitar da aljanu.
16 这十二个人有西门(耶稣又给他起名叫彼得),
Ga sha biyun da ya naɗa. Siman (wanda ya ba shi suna Bitrus);
17 还有西庇太的儿子雅各和雅各的兄弟约翰(又给这两个人起名叫半尼其,就是雷子的意思),
Yaƙub ɗan Zebedi da kuma ɗan’uwansa Yohanna (ga waɗannan kuwa ya sa musu suna Buwarnajis, wato, “’ya’yan tsawa”);
18 又有安得烈、腓力、巴多罗买、马太、多马、亚勒腓的儿子雅各,和达太,并奋锐党的西门,
Andarawus, Filibus, Bartolomeyu, Mattiyu, Toma, Yaƙub ɗan Alfayus, Taddayus, Siman wanda ake kira Zilot,
19 还有卖耶稣的加略人犹大。
da kuma Yahuda Iskariyot, wanda ya bashe Yesu.
20 耶稣进了一个屋子,众人又聚集,甚至他连饭也顾不得吃。
Sai Yesu ya shiga wani gida, taro kuma ya sāke haɗuwa, har shi da almajiransa ma ba su sami damar cin abinci ba.
21 耶稣的亲属听见,就出来要拉住他,因为他们说他癫狂了。
Da’yan’uwansa suka sami wannan labari, sai suka tafi don su dawo da shi, suna cewa, “Ai, ya haukace.”
22 从耶路撒冷下来的文士说:“他是被别西卜附着”;又说:“他是靠着鬼王赶鬼。”
Malaman dokokin da suka zo daga Urushalima suka ce, “Ai, yana da Be’elzebub! Da ikon sarkin aljanu yake fitar da aljanu.”
23 耶稣叫他们来,用比喻对他们说:“撒但怎能赶出撒但呢?
Sai Yesu ya kira su, ya yi musu magana da misalai ya ce, “Yaya Shaiɗan zai fitar da Shaiɗan?
24 若一国自相纷争,那国就站立不住;
In mulki yana gāba da kansa, wannan mulki ba zai tsaya ba.
25 若一家自相纷争,那家就站立不住。
In gida yana gāba da kansa, wannan gida ba zai tsaya ba.
26 若撒但自相攻打纷争,他就站立不住,必要灭亡。
In kuwa Shaiɗan yana gāba da kansa, ya kuma rabu biyu, ba zai tsaya ba, ƙarshensa ya zo ke nan.
27 没有人能进壮士家里,抢夺他的家具;必先捆住那壮士,才可以抢夺他的家。
Tabbatacce, ba mai shiga gidan mai ƙarfi yă kwashe dukiyarsa, sai bayan ya daure mai ƙarfin, sa’an nan zai iya yin fashin gidansa.
28 我实在告诉你们,世人一切的罪和一切亵渎的话都可得赦免;
Gaskiya nake gaya muku, za a gafarta duk zunubai da kuma saɓon mutane suka yi.
29 凡亵渎圣灵的,却永不得赦免,乃要担当永远的罪。” (aiōn g165, aiōnios g166)
Amma duk wanda ya saɓi Ruhu Mai Tsarki, ba za a taɓa gafara masa ba. Ya aikata madawwamin zunubi ke nan.” (aiōn g165, aiōnios g166)
30 这话是因为他们说:“他是被污鬼附着的。”
Ya faɗi haka domin suna cewa, “Yana da mugun ruhu.”
31 当下,耶稣的母亲和弟兄来,站在外边,打发人去叫他。
Sai mahaifiyar Yesu tare da’yan’uwansa suka iso. Suna tsaye a waje, sai suka aiki wani ciki yă kira shi.
32 有许多人在耶稣周围坐着,他们就告诉他说:“看哪,你母亲和你弟兄在外边找你。”
Taron yana zaune kewaye da shi, sai suka ce masa, “Mahaifiyarka da’yan’uwanka suna waje, suna nemanka.”
33 耶稣回答说:“谁是我的母亲?谁是我的弟兄?”
Ya yi tambaya ya ce, “Su wane ne mahaifiyata, da’yan’uwana?”
34 就四面观看那周围坐着的人,说:“看哪,我的母亲,我的弟兄。
Sai ya dubi waɗanda suke zaune kewaye da shi ya ce, “Ga mahaifiyata da’yan’uwana!
35 凡遵行 神旨意的人就是我的弟兄姊妹和母亲了。”
Duk wanda yake aikata nufin Allah, shi ne ɗan’uwana, da’yar’uwata, da kuma mahaifiyata.”

< 马可福音 3 >