< 路加福音 1 >
1 提阿非罗大人哪,有好些人提笔作书,述说在我们中间所成就的事,是照传道的人从起初亲眼看见又传给我们的。
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 这些事我既从起头都详细考察了,就定意要按着次序写给你,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 当犹太王希律的时候,亚比雅班里有一个祭司,名叫撒迦利亚;他妻子是亚伦的后人,名叫伊利莎白。
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 他们二人在 神面前都是义人,遵行主的一切诫命礼仪,没有可指摘的,
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 只是没有孩子;因为伊利莎白不生育,两个人又年纪老迈了。
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 天使对他说:“撒迦利亚,不要害怕,因为你的祈祷已经被听见了。你的妻子伊利莎白要给你生一个儿子,你要给他起名叫约翰。
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 他在主面前将要为大,淡酒浓酒都不喝,从母腹里就被圣灵充满了。
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 他要使许多以色列人回转,归于主—他们的 神。
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 他必有以利亚的心志能力,行在主的前面,叫为父的心转向儿女,叫悖逆的人转从义人的智慧,又为主预备合用的百姓。”
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 撒迦利亚对天使说:“我凭着什么可知道这事呢?我已经老了,我的妻子也年纪老迈了。”
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 天使回答说:“我是站在 神面前的加百列,奉差而来对你说话,将这好信息报给你。
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 到了时候,这话必然应验;只因你不信,你必哑巴,不能说话,直到这事成就的日子。”
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 及至他出来,不能和他们说话,他们就知道他在殿里见了异象;因为他直向他们打手式,竟成了哑巴。
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 这些日子以后,他的妻子伊利莎白怀了孕,就隐藏了五个月,
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 说:“主在眷顾我的日子,这样看待我,要把我在人间的羞耻除掉。”
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 到了第六个月,天使加百列奉 神的差遣往加利利的一座城去(这城名叫拿撒勒),
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 到一个童女那里,是已经许配大卫家的一个人,名叫约瑟。童女的名字叫马利亚;
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 天使进去,对她说:“蒙大恩的女子,我问你安,主和你同在了!”
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 马利亚因这话就很惊慌,又反复思想这样问安是什么意思。
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 天使对她说:“马利亚,不要怕!你在 神面前已经蒙恩了。
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 他要为大,称为至高者的儿子;主 神要把他祖大卫的位给他。
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 他要作雅各家的王,直到永远;他的国也没有穷尽。” (aiōn )
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn )
34 马利亚对天使说:“我没有出嫁,怎么有这事呢?”
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 天使回答说:“圣灵要临到你身上,至高者的能力要荫庇你,因此所要生的圣者必称为 神的儿子。
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 况且你的亲戚伊利莎白,在年老的时候也怀了男胎,就是那素来称为不生育的,现在有孕六个月了。
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 马利亚说:“我是主的使女,情愿照你的话成就在我身上。”天使就离开她去了。
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 那时候,马利亚起身,急忙往山地里去,来到犹大的一座城;
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 伊利莎白一听马利亚问安,所怀的胎就在腹里跳动。伊利莎白且被圣灵充满,
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 高声喊着说:“你在妇女中是有福的!你所怀的胎也是有福的!
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 因为你问安的声音一入我耳,我腹里的胎就欢喜跳动。
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 这相信的女子是有福的!因为主对她所说的话都要应验。”
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 因为他顾念他使女的卑微; 从今以后, 万代要称我有福。
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 他用膀臂施展大能; 那狂傲的人正心里妄想就被他赶散了。
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 为要记念亚伯拉罕和他的后裔, 施怜悯直到永远, 正如从前对我们列祖所说的话。 (aiōn )
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn )
56 马利亚和伊利莎白同住,约有三个月,就回家去了。
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 邻里亲族听见主向她大施怜悯,就和她一同欢乐。
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 到了第八日,他们来要给孩子行割礼,并要照他父亲的名字叫他撒迦利亚。
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 他们就向他父亲打手式,问他要叫这孩子什么名字。
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 他要了一块写字的板,就写上,说:“他的名字是约翰。”他们便都希奇。
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 撒迦利亚的口立时开了,舌头也舒展了,就说出话来,称颂 神。
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 周围居住的人都惧怕;这一切的事就传遍了犹太的山地。
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 凡听见的人都将这事放在心里,说:“这个孩子将来怎么样呢?因为有主与他同在。”
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 主—以色列的 神是应当称颂的! 因他眷顾他的百姓,为他们施行救赎,
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 正如主借着从创世以来圣先知的口所说的话, (aiōn )
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn )
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 就可以终身在他面前, 坦然无惧地用圣洁、公义事奉他。
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 孩子啊!你要称为至高者的先知; 因为你要行在主的前面, 预备他的道路,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 因我们 神怜悯的心肠, 叫清晨的日光从高天临到我们,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 要照亮坐在黑暗中死荫里的人, 把我们的脚引到平安的路上。
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 那孩子渐渐长大,心灵强健,住在旷野,直到他显明在以色列人面前的日子。
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.