< 耶利米哀歌 5 >
1 耶和华啊,求你记念我们所遭遇的事, 观看我们所受的凌辱。
Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
2 我们的产业归与外邦人; 我们的房屋归与外路人。
An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
5 追赶我们的,到了我们的颈项上; 我们疲乏不得歇息。
Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
7 我们列祖犯罪,而今不在了; 我们担当他们的罪孽。
Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
11 敌人在锡安玷污妇人, 在犹大的城邑玷污处女。
An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
16 冠冕从我们的头上落下; 我们犯罪了,我们有祸了!
Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
21 耶和华啊,求你使我们向你回转, 我们便得回转。 求你复新我们的日子,像古时一样。
Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.