< 耶利米书 15 >

1 耶和华对我说:“虽有摩西和撒母耳站在我面前代求,我的心也不顾惜这百姓。你将他们从我眼前赶出,叫他们去吧!
Sai Ubangiji ya ce mini, “Ko da Musa da Sama’ila za su tsaya a gabana, zuciyata ba za tă komo ga mutanen nan ba. Ka kore su daga gabana! Su tafi!
2 他们问你说:‘我们往哪里去呢?’你便告诉他们,耶和华如此说: 定为死亡的,必致死亡; 定为刀杀的,必交刀杀; 定为饥荒的,必遭饥荒; 定为掳掠的,必被掳掠。”
In kuma suka tambaye ka, ‘Ina za mu tafi?’ Sai ka faɗa musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Waɗanda aka ƙaddara ga mutuwa, ga mutuwa za su; waɗanda aka ƙaddara ga takobi, ga takobi za su; waɗanda aka ƙaddara ga yunwa, ga yunwa za su; waɗanda aka ƙaddara ga zaman bauta, ga zaman bauta za su.’
3 耶和华说:“我命定四样害他们,就是刀剑杀戮、狗类撕裂、空中的飞鸟,和地上的野兽吞吃毁灭;
“Zan aika musu da iri masu hallakarwa guda huɗu,” in ji Ubangiji, “takobi zai kashe, karnuka za su kwashe, tsuntsaye da namun jeji kuma su cinye su kuma hallaka.
4 又必使他们在天下万国中抛来抛去,都因犹大王希西家的儿子玛拿西在耶路撒冷所行的事。”
Zan sa su zama abin ƙyama ga dukan mulkokin duniya saboda abin da Manasse ɗan Hezekiya sarkin Yahuda ya aikata a Urushalima.
5 耶路撒冷啊,谁可怜你呢? 谁为你悲伤呢? 谁转身问你的安呢?
“Wa zai ji tausayinki, ya Urushalima? Wa zai yi makoki dominki? Wa zai dakata ya tambayi lafiyarki?
6 耶和华说:你弃绝了我, 转身退后; 因此我伸手攻击你,毁坏你。 我后悔甚不耐烦。
Kin ƙi ni,” in ji Ubangiji. “Ki ci gaba da ja da baya. Ta haka zan ɗibiya hannuwana a kanki in hallaka ki; ba zan ƙara nuna miki jinƙai ba.
7 我在境内各城门口, 用簸箕簸了我的百姓, 使他们丧掉儿女。 我毁灭他们, 他们仍不转离所行的道。
Zan sheƙe ki da abin sheƙewa a ƙofofin birnin ƙasar. Zan kawo baƙin ciki da hallaka a kan mutanena, gama ba su canja hanyoyinsu ba.
8 他们的寡妇在我面前比海沙更多; 我使灭命的午间来, 攻击少年人的母亲, 使痛苦惊吓忽然临到她身上。
Zan ƙara yawan gwaurayensu su fi yashin teku yawa. Da tsakar rana zan kawo mai hallakarwa a kan iyaye mata na samarinsu; farat ɗaya zan kawo musu wahala da razana.
9 生过七子的妇人力衰气绝; 尚在白昼,日头忽落; 她抱愧蒙羞。 其余的人, 我必在他们敌人跟前,交与刀剑。 这是耶和华说的。
Mahaifiya’ya’ya bakwai za tă suma ta ja numfashinta na ƙarshe. Ranarta zai fāɗi tun lokacin bai yi ba; za tă sha kunya a kuma wulaƙanta ta. Zan sa a kashe raguwa da takobi a gaban abokan gābansu,” in ji Ubangiji.
10 我的母亲哪,我有祸了!因你生我作为遍地相争相竞的人。我素来没有借贷与人,人也没有借贷与我,人人却都咒骂我。
Kaitona, mahaifiyata, da kika haife ni, mutumin da dukan ƙasa take faɗa take kuma gardama da shi! Ban ba da bashi ko in ci bashi ba, duk da haka kowa yana zagina.
11 耶和华说:“我必要坚固你,使你得好处。灾祸苦难临到的时候,我必要使仇敌央求你。(
Ubangiji ya ce, “Tabbatacce zan cece ka don alheri; tabbatacce zan sa abokan gābanka su yi roƙo gare ka a lokacin masifa da kuma lokacin wahala.
12 人岂能将铜与铁,就是北方的铁折断呢?)
“Mutum zai iya karye ƙarfe ƙarfe daga arewa, ko tagulla?
13 “我必因你在四境之内所犯的一切罪,把你的货物财宝当掠物,白白地交给仇敌。
“Dukiyarku da arzikinku zan ba da su ganima, babu tara, saboda duka zunubanku ko’ina a ƙasar.
14 我也必使仇敌带这掠物到你所不认识的地去,因我怒中起的火要将你们焚烧。”
Zan bautar da ku ga abokan gābanku a ƙasar da ba ku sani ba, gama fushina zai yi ƙuna kamar wuta da za tă yi ƙuna a kanku.”
15 耶和华啊,你是知道的; 求你记念我,眷顾我, 向逼迫我的人为我报仇; 不要向他们忍怒取我的命, 要知道我为你的缘故受了凌辱。
Ka gane, ya Ubangiji; ka tuna da ni ka kuma lura da ni. Ka yi mini ramuwa a kan masu tsananta mini. Cikin jimirinka, kada ka ɗauke ni; ka tuna yadda na sha zagi saboda kai.
16 耶和华—万军之 神啊, 我得着你的言语就当食物吃了; 你的言语是我心中的欢喜快乐, 因我是称为你名下的人。
Sa’ad da maganganunka suka zo, na cinye su; suka zama abin farin ciki zuciyata kuma ta yi murna, gama ana kirana da sunanka, Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki.
17 我没有坐在宴乐人的会中, 也没有欢乐; 我因你的感动独自静坐, 因你使我满心愤恨。
Ban taɓa zauna a cikin’yan tawaye ba, ban taɓa yi murna da su ba; na zauna ni kaɗai domin hannunka yana a kaina ka kuma sa na cika da haushi.
18 我的痛苦为何长久不止呢? 我的伤痕为何无法医治、不能痊愈呢? 难道你待我有诡诈,像流干的河道吗?
Me ya sa wahalata ba ta ƙarewa mikina kuma ba ya warkuwa? Za ka zama mini kamar rafi mai yaudara ne, kamar maɓulɓulan da ta kafe ne?
19 耶和华如此说:你若归回, 我就将你再带来, 使你站在我面前; 你若将宝贵的和下贱的分别出来, 你就可以当作我的口。 他们必归向你, 你却不可归向他们。
Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “In ka tuba, zan maido da kai don ka bauta mini; in ka ambaci maganganu masu kyau, ba marasa kyau ba, za ka zama kakakina. Bari wannan mutane su juyo gare ka, amma kada ka juye gare su.
20 我必使你向这百姓成为坚固的铜墙; 他们必攻击你,却不能胜你; 因我与你同在,要拯救你,搭救你。 这是耶和华说的。
Zan mai da kai katanga ga wannan mutane, katanga mai ƙarfi na tagulla; za su yi yaƙi da kai amma ba za su yi nasara a kanka ba, gama ina tare da kai don in kuɓutar in kuma cece ka,” in ji Ubangiji.
21 我必搭救你脱离恶人的手, 救赎你脱离强暴人的手。
“Zan cece ka daga hannuwan mugaye in ɓamɓare ka daga hannun marasa tausayi.”

< 耶利米书 15 >