< 以赛亚书 58 >

1 你要大声喊叫,不可止息; 扬起声来,好像吹角。 向我百姓说明他们的过犯; 向雅各家说明他们的罪恶。
“Ku yi ihu da ƙarfi, ba ƙaƙƙautawa. Ku tā da muryarku kamar busar ƙaho. Ku furta wa mutanena tawayensu da kuma ga gidan Yaƙub zunubansu.
2 他们天天寻求我, 乐意明白我的道, 好像行义的国民, 不离弃他们 神的典章, 向我求问公义的判语, 喜悦亲近 神。
Gama kowace rana suna nemana; suna marmarin sanin hanyoyina, sai ka ce al’ummar da take yin abin da yake daidai ba ta kuma yashe umarnan Allahnta ba. Sun nemi shawarwaran da suke daidai daga gare ni suna kuma marmari Allah ya zo kusa da su.
3 他们说:我们禁食,你为何不看见呢? 我们刻苦己心,你为何不理会呢? 看哪,你们禁食的日子仍求利益, 勒逼人为你们做苦工。
Suna cewa, ‘Don me muka yi azumi, ba ka kuma gani ba? Me ya sa muka ƙasƙantar da kanmu, ba ka kuma lura da wannan ba?’ “Duk da haka a ranar azuminku, kuna yi yadda kuka ga dama kuna kuma zaluntar dukan ma’aikata.
4 你们禁食,却互相争竞, 以凶恶的拳头打人。 你们今日禁食, 不得使你们的声音听闻于上。
Azuminku yakan ƙare a faɗa da kuma hargitsi, kuna ta naushin juna da mugayen naushe-naushe. Ba za ku iya azumi kamar yadda kuke yi a yau ku zaci za a ji muryarku can sama.
5 这样禁食岂是我所拣选、 使人刻苦己心的日子吗? 岂是叫人垂头像苇子, 用麻布和炉灰铺在他以下吗? 你这可称为禁食、为耶和华所悦纳的日子吗?
Irin azumin da na zaɓa ke nan, rana guda kawai don mutum ya ƙasƙantar da kansa? Sunkuyar da kanku kamar iwa kawai kuna kuma kwance a tsummoki da toka? Abin da kuke kira azumi ke nan rana yardajje ga Ubangiji?
6 我所拣选的禁食不是要松开凶恶的绳, 解下轭上的索, 使被欺压的得自由, 折断一切的轭吗?
“Irin azumin da na zaɓa shi ne, a kunce sarƙoƙin rashin adalci a kuma kunce igiyoyin karkiya, a’yantar da waɗanda ake zalunta a kuma kakkarye kowace karkiya?
7 不是要把你的饼分给饥饿的人, 将飘流的穷人接到你家中, 见赤身的给他衣服遮体, 顾恤自己的骨肉而不掩藏吗?
Ba shi ne ku rarraba abincinku da mayunwata ku kuma tanada wa matalauta masu yawo mahalli, sa’ad da kuka ga wanda yake tsirara, ku yi masa sutura, kada kuma ku ba wa namanku da jininku baya?
8 这样,你的光就必发现如早晨的光; 你所得的医治要速速发明。 你的公义必在你前面行; 耶和华的荣光必作你的后盾。
Sa’an nan haskenku zai keto kamar ketowar alfijir, warkarwarku kuma zai bayyana nan da nan; sa’an nan adalcinku zai tafi a gabanku, ɗaukakar Ubangiji kuma zai tsare ku daga baya.
9 那时你求告,耶和华必应允; 你呼求,他必说:我在这里。 你若从你中间除掉重轭 和指摘人的指头,并发恶言的事,
Sa’an nan za ku yi kira, Ubangiji kuma zai amsa; za ku yi kuka don neman taimako, zai kuwa ce ga ni nan. “In kuka kawar da karkiyar zalunci, kuka daina nuna wa juna yatsa da kuma faɗar mugayen maganganu,
10 你心若向饥饿的人发怜悯, 使困苦的人得满足, 你的光就必在黑暗中发现; 你的幽暗必变如正午。
in kuma kuka ɗauki lokaci kuka ƙosar da mayunwata kuka kuma biya bukatun waɗanda suke shan tsanani, sa’an nan ne haskenku zai haskaka cikin duhu darenku kuma zai zama kamar tsakar rana.
11 耶和华也必时常引导你, 在干旱之地使你心满意足, 骨头强壮。 你必像浇灌的园子, 又像水流不绝的泉源。
Ubangiji zai bishe ku kullum; zai biya muku bukatunku a ƙasa mai zafin rana ya kuma ƙarfafa ƙasusuwanku. Za ku zama kamar lambun da aka yi masa banruwa, kamar rafin da ruwansa ba ya ƙafewa.
12 那些出于你的人必修造久已荒废之处; 你要建立拆毁累代的根基。 你必称为补破口的, 和重修路径与人居住的。
Mutanenku za su sāke gina kufai na da su kuma daga tsofaffin harsashai; za a ce da ku Masu Gyaran Katangar da ta Rushe, Masu Farfaɗo da Tituna da kuma Wuraren zama.
13 你若在安息日掉转你的脚步, 在我圣日不以操作为喜乐, 称安息日为可喜乐的, 称耶和华的圣日为可尊重的; 而且尊敬这日, 不办自己的私事, 不随自己的私意, 不说自己的私话,
“In kun kiyaye ƙafafunku daga take Asabbaci da kuma daga aikata abin da kuka gan dama a ranata mai tsarki, in kuka kira Asabbaci ranar murna rana mai tsarki ta Ubangiji kuma mai bangirma, in kuka girmama ta ta wurin ƙin yin abin da kuka gan dama da kuma yin al’amuranku ko yin mugayen maganganu,
14 你就以耶和华为乐。 耶和华要使你乘驾地的高处, 又以你祖雅各的产业养育你。 这是耶和华亲口说的。
sa’an nan za ku yi farin ciki a cikin Ubangiji, zan kuma sa ku a kan maɗaukaka ƙasashe ku kuma yi biki a gādon mahaifinku Yaƙub.” Ni Ubangiji ne na faɗa.

< 以赛亚书 58 >